← Book details Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 27

Sashe 3

Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dan karamin murmushi MALIK ya yi kafin ya kali yarinyar da ke zaune geffen shi ya ce " TESNIM yaushe za ki tafi Daular Ottoman , mun yi waya da kakan na ki ya ce ya shirya miki wata tsaraba ta musaman "

Kunbure fuska TESNIM ta yi ta turo dan bakin nan nata gaba ta ce " Abbi ba AMIR ne ba na ce mishi yaushe za mu tafi ya ce wai shi ba zai je ba "

Slowly AMIR ya dago kai ya kali TESNIM murya kassa kassa ya ce " dole sai da ni za ki je , ba ki san hanya ba ne "

" NAWFEL laifin me ta yi maka da ga ta ce ka raka ta " MALIK ya fada ya na kallon AMIR

Dan karamin tsaki ya yi kafin ya mike tsaye ya juyo ya fara takawa cike da nitsuwa ya bar wajen
" NAWFEL ina za ka je ba ka Kamala abincin ka ba " RIANNA ta fada

Ko amsa mata bai yi ba ya ci gaba da tafiyar shi
Sai da ya bar wajen sannan ta juyo ta kali MALIK ta ce " Abbi don Allah ku janye maganar nan ta AMIR ya hau mulki wlh ba ya so "

Daga mata hannu MALIK ya yi ya katse ta kafin ya ce mata " RIANNA ke da NAWFEL na ga bakin ku daya , idan bai hau mulki baya na ba wa zai hawa , ku nai sheda shi kadai ne yarima da na mallaka , ya tafi ya hura miki kunne ko , ya zuba miki shagwabar da ya saba ko "

Marairaice fuska RIANNA ta yi ta na fadin " please Daddy , ku ba shi damar ya zabi abun da ya ke son yi , kar ku condemend din shi saman abun da bai da ra a yi , wlh Abbi tun da ya nuna ba ya son Mulkin nan wlh ko ya hau ba zai tsaya ya kula da saudiya kamar yadda ku ke yi "

" RIANNA tashi fice min da ga gani sai ki bi bayan shi dama ke ce ke darme mishi gindi ya na abun da ya ga dama , to sai ki je ki rarrashe shi , ki kuma fada mishi gobe ya shirya bi na Fada "

" Abbi ......... "
Da sauri Malik ya daga mata hannu ba tare da ya ce komai ba
Tashi ta yi ta na dan kananan magaganun ta bi bayan AMIR ita ma ta bar wajen
Su dai Malikat kallon shi kawai su ke dan sun san halin Malik idan ya yanke shawara to babu wanda ya isa ya sa shi ya sauya shawarar nan dama haka nan ya ke da magana guda a ka san shi , duk irin halin da zai tsinci kan shi , shawarar kan shi kawai ya ke dauka , bai taba neman shawarar wani ba , Idan kuma abu ya shige mishi duhu shawarar Matan shi kawai ya ke nema

Bayan RIANNA ta baro dining room din su kai tsaye wani kyawatencen parlour ta nufa nan ta isko AMIR zaune saman chair din Malik ta gold zalla ya daura kafa daya bisa daya ya kurawa Tv ido

Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi da sauri ta nufe shi ta na fadin " kai AMIR kujerar Malik za ka hau haka , maza sauka tun bai gan ka ba , ka fi kowa sanin bayan shi babu wanda ya isa ya hau wannan kujerar "

Slowly AMIR ya juyo da kan shi ya kali RIANNA ya na dan lumshe idanun shi kamar mai jin barci , cike da izza ya ce mata " da ga yau ta zama tawa " ya kai karshen ya na meda kallon shi kan Tv

Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi baki sake , tun da ta ke da AMIR ba ta taba ganin ya yi mata kwarjini kamar na yau ba
Ta na shirin magana ta jiyo Muryar Malik a bayan ta ya na fadin " yanzu sai ka tashi me ita ya zo "

Dum ta ji gaban ta ya buga da sauri ta juya ta na kallon shi ta na dan zazzaro idanu
Shi dai AMIR ko motsi bai yi ba asali ma ko kallon inda Malik ya ke bai yi ba ya ci gaba da kallon Tv ................... ( ku tsaya na dubo abun da ke cikin Tv din nan gaskia )
Ba komai ba ne face masarautar ya ke kallo ta cikin kananan camera da a ka boye ta ko ina cikin masarautar , shi dai kawai ya na kallon abun da ke faruwa a cikin masarautar ne amma hankalin shi na nesa

Har sai da Malik ya karaso gaban shi ya tsaya ya na yi mishi magana bai sani ba
Kawai sai ji ya yi an buge mishi kafar shi ta sama ta fadi kassa ,
Slowly ya lumshe idanun shi kafin ya bude su ya na kallon Malik ido cikin ido kafin ya ce " What ? " a takaice

Ba Malik kadai ba har RIANNA da ke tsaye a bayan shi sai da ta zaro idanu ta na kallon AMIR
" NAWFEL sauka da ga saman kujera ta " Malik ya fada cikin nuna isa

Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya meda kallon shi kan Tv din ba tare da ya ce komai ba
" Akhie ............ "
Kut maganar ta yanke sakamakon daga mata hannu da Malik ya yi
" Idan ka na son zama saman wannan kujerar , dole sai ka yarda ka amshi sunan ka na yarima mai jiran gado ka fara bi na Fada domin ganin yadda a ke kula da masarautar nan sannan za ka iya zama saman wannan kujerar "

Slowly AMIR ya mike tsaye ya fara takawa a hankali ya karaso gaban Malik ya tsaya ya na kallon shi cikin ido ya ce " kujera ce dai sai na hau ta , sannan ni ba zan je Fada ba , ba na bukatar shawarar kowa ba na kuma bukatar sannin yadda a ke kula da masarautar , duk ranar da a ka nada ni a matsayin Malik tsari na kadai zan bi dan haka ka daina min zancen wata fada ni babu inda zan je " ya na gama fadar haka ya juya ya koma saman kujerar nan ya zauna ya daura kafa daya saman daya ya ci gaba da kallon Tv din gaban shi

Shi dai Malik sumar tsaye su ka yi shi da RIANNA
Sai ya kare mishi kallo da kyau sannan ya ce ma RIANNA ta ba su waje
Ba musu ta juya ta bar parlour dama part din Malik ne su ke ciki sai ta bar part din baki daya dama su Malikat su riga ta tafiya TESNIM kuma ta tafi yawon birididin da ta saba , ba ta wannan part ba ta wacen duk in da ta kama ta tafiya ta ke yi

A hankali Malik ya nufi wata Sofa da ke daman kujerar da AMIR ke zaune a kai shi ma ya zauna ya na kallon AMIR

Kamar ko ya san kallon shi ya ke yi ya ce mishi " lafiya ka na kallo na haka "
Girgiza kan shi Malik ya yi ya na murmushi ya ce " Mulki ya na kama ka AMIR why kullum ka ke abu kamar mace , sai dan karan shagwaba , ko takobi sai da RIANNA ta matsa sannan ka fara koyo , da ba hakan ba yanzu ko makiyi ya zo maka ba za ka iya kare kan ka ba "

Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba
Dariya Malik ya yi kafin ya dauki wani pillow saman sofar ya tila wa AMIR
da sauri AMIR ya kauce pillow din bai same shi ba
Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi ya ce " Abbi , ni fa fada ne da makami ba ya burge ni , na fi son fada da hannu "

" hmmm , hakan ba shi ba ne mafita ba , ya kamata a ce duk wani makami a duniya ka iya fada da shi , ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , bare kai da ka ke cikin gidan sarauta "

Cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Idan kuma makiyin ya zo maka ta baya ? "
Shiru Malik ya yi ya rasa amsar da zai ba shi
Jin ya yi shiru ya sa AMIR juyo da kan shi ya kali Malik
Dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , amma na san wani abu , duk mai sanin ganin bayan ka , ba zai soke ka ta gaba , dole ta bayan idon ka zai soke ka , saboda ya san ka fi karfin shi ta gaba "

" wait ! Maganar me ka ke yi min haka " Malik ya fada dan shi bai san abun da AMIR ke fada ba

Meda kallon shi AMIR ya yi kan Tv sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " ba komai kawai ina nufin ka zama me tsare bayan ka a kodayaushe saboda ba ka san ta inda makiyin ka zai zo maka ba , Idan kan ce ka za kare gaban ka kadai , to ta bayan ka zai zowa , dan haka ka zama mai kare gaba da bayan ka , saboda ba ka san da wa ka ke tare da shi ba , Makiyin ka zai zo ma ka da sufar aboki , aboki kuma da sufar makiyi "

Dariya sosai Malik ya yi kafin ya ce " shi ya sa ban yarda da kowa cikin masarautar nan , ko a fada ba shawarar kowa ba ke doka ba "

" Duk da hakan , yanzu idan na tambaye ka cikin fadar nan wanda ke zaune da kai da zuciya daya za ka iya fido min su "
Chapter 3 · 0% Book details