← Book details Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 27

Sashe 15

Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

a karamin murmushi ta yi ta na gyada mishi kai kafin ta juya ta fara takawa
duk taku daya in ta yi sai wadanan santala santalan cinyoyin na ta sun fito
da sauri AMIR ya kauda kan shi dan fa ya ga abun 🤣

har ta kai bakin kofar Dressing room ta jiyo Muryar shi ya na fadin " tsaya "
cak ta tsaya da tafiyar ta ta juyo ta kale shi ta ce " lafiya yaya Zayd "
girgiza mata kai ya yi allamun ba komai kafin ya ce mata ta dawo
ba musu ta dawo gaban shi ta tsaya ta na murmushi

shiru ya yi bai ce mata komai ba ya zuba mata wadanan idanun na shi
sai da ya dan dauki lokaci a haka kafin ya daga kafa a hankali ya juya ya nufi kofar dakin
a tunanin ta fita zai yi , kawai sai ganin ta yi ya meda kofar ya rufe , sannan ya juyo ya karaso bakin gadon ya zauna
ita dai Inaya da ido kawai ta ke bin shi , ta na murmushi , ba ta san abun da ya ke shirin aikatawa ba

a hankali ya mika mata hannun shi ya na kallon cikin idanun ta
ba musu ta daura hannun ta saman na shi ta na ci gaba da murmushin ta kafin ta tako ta tsaya dab gaban shi
a hankali ya janyo ta ya zaunar da ita saman cinyar shi murya kassa kassa ya ce mata " Saura kwana nawa a fara azumi "

a hankali ta daga kan ta sama , ta hura kumatun
ta na a haka kawai sai ji ta yi ya daura mata yatsar shi saman kumatun ta ya dan danna
ba ta san lokacin da wata yar karamar dariya ta kubce mata ba

" tambayar ki na yi ban ce ki hura min kumatu ba " ya fada mata ya janye hannun shi
" Yo ai yaya Zayd tunani na ke yi " ta fada cikin shagwaba
" shikenan kin samo ? "
" eh saura sati guda ina ji "

gyada mata kai ya yi a hankali , ya kai hannun shi ya riko nata ya ce " yeah , saura sati guda , ni da Malik za mu yi tafiya zuwa Makka , a cen mu ke yin azumi ko wace shekara "

da sauri ta katse shi da cewa " Yaya Zayd yanzu tafiya za ka yi ka bar ni ? " ta fada idanun ta su na kawo ruwa nan take ta fara ruwan hawaye

A hankali ya kai hannu ya kontar da kan ta saman shoulder din shi cikin sigar rarrashi ya ce mata " don't worry , bayan watan azumi zan dawo kuma ba yanzu ba zan tafi ki kontar da hankalin ki "

zagayo da hannayan ta ta yi a wuyan shi ta na sakin dan karamin kuka

a hankali ya lumshe idanun shi ya na jin zuciyar shi ba dadi har ga Allah ba ya son jin kukan ta
ga shi ba wani rarrashi ya iya ba bare ya ce ya rarrashe ta , haka kawai ya tsaya ya yi shiru ya na sauraron yadda ta ke kukan ta kassa kassa

slowly ya sauko da hannun shi da ga saman kan ta bai sauke shi ko ina ba sai saman cinyar ta , dama tun zaman da ta yi ta fito

Wani irin shock ne ya ji lokacin da hannun shi ya sauka saman fatar jikin ta , luwai luwai da ita ga taushi kamar ta baby , nan take ya ji wani zir tun da ga tafin kafar shi har tsakiyar kan shi , duk wata siga ta jikin shi sai da ta mike , duk wasu kofofin feelings din shi sai da su ka bude lokaci guda

a hankali ya fara shafa cinyar ta ido a lumshe , ya kontar da kan shi saman shoulder din ta
ya na a haka kawai ya ji ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya har sai da ya ware idanun shi ba shiri
ya na bude idanun shi ya ji fara yo kassa da hannun ta guda ta daura shi saman kirjin shi

a hankali ya bude baki ya ce mata " me ki ke so na sayo miki idan na je "
murya cen kassan makoshi ta ce mishi " duk abun da ya burge ka ina so "
" shikenan yanzu tashi ki je ki sauya rigar ki " ya fada ya na dago kan shi da ga saman shoulder din ta

a hankali ita ma ta dago ta kale shi
sai da gaban ta ya fadi lokacin da ta ga yadda idanun shi su ka koma jazir
" yaya Zayd me ya samu idanun ka , su ka yi ja haka ? " ta fada ta na daura hannu ta saman kumatun shi

dan lumshe idanun shi ya yi kafin ya sake bude su a hankali saman ta , murya cen kassan makoshi ya ce mata " Ba komai tashi ki tafi "

dan karamin murmushi ta yi kafin ta janye hannun ta , ta tashi da ga saman cinyar shi ta nufi dressing room , har za ta shiga ta juya ta nufi toilet ta shiga ta rufe kofar

da kallo ya rakata har sai da ta rufe kofar toilet din sannan ya tashi a hankali ya nufi kofar fita dakin ya ficewar shi
ya na fitowa parlourn ya nufi kofar fita part din
har ya kai bakin kofa ya jiyo Muryar MALIKAT INAS ta na fadin " AMIR me ya same ka ? ka sauya lokaci guda "
ba tare da ya juyo ba ya ce mata ba komai , da ga haka ya daga kafa ya fice part din
da kallo ta raka shi har sai da ya fice sannan ta saki wani cool murmushi

* ROUKSAR

zaune su ke ita da Tesnim cikin parlourn part din MALIKAT AL'UMU , ga uban Fruits a gaban su , ko wace na rike da wayar ta sai faman chating su ke yi

sun dan jima a haka kafin Rouksar ta ajiye wayar ta ta kali Tesnim ta ce " Amira , wai wacece yarinyar nan da na ga ta konta a jikin Amir , kuma bai ce mata komai ba "
ba tare da ta ajiye wayar ta ba tesnim ta ce mata " Ni ma dai ban san ta ba , amma tare da Amir ta ke , a wajen su ya zauna tsawon shekarun nan , shi ya sa ki ka ta na lake mishi , really she is so cute , she looks so innocent "

dan tabe baki Rouksar ta yi kafin ta ce " Kamar ya , yanzu haka za ki sa mata ido ta na lakewa Amir , ki taka mata burki mana .... "

cikin nitsuwa Tesnim ta katse ta da cewa " Why zan yi haka ? Tun da Amir ba shi da matsala da hakan , ba na da hakin shiga lamarin shi , na san ba karamin aikin shi ba ne yanzu da na fada mata wani abu ya yi min mugun fada " ta na kai karshen maganar ta , ta saki wata yar karamar dariya

" Tesnim , kin fin kowa sanin wanene Amir , Ba girman shi ba ne a ce wannan yar karamar yarinyar ta makale mishi , he is the successor of MALIK HICHAM BIN JAABAR shugaban kassar Saudiya baki Daya "

ajiye wayar ta Tesnim ta yi , ta dan matso da face din ta ta ce ma Rouksar " kin ga ko , ga kofa cen bude , ban tare ki ba , tashi ki je ki fada mishi hakan , amma kin ga ni , wlh ko kashe ni a ke yi ba zan taba shiga abun da ya shafi Amir " ta na gama fadar haka ta dauki wayar ta ci gaba da aikin ta na chat

wani mugun kallo Rouksar ta wurga ma Tesnim , maganar ta ta yi matukar kuna mata rai
a hankali Rouksar ta mike ta na fadin " zan je toilet ina zuwa "
da to kawai Tesnim ta amsa mata ba tare da ta dago kai ba
sai da Rouksar ta harare ta sama da kassa kafin ta daga kafa
ta nufi corridor din bedrooms , ta nufi bedroom ta farko , ta shiga ta meda kofar , sannan ta nufi toilet ta shiga ta meda kofar ta sa key

ta na shiga ta saki wata yar karamar kara ta na fadin " sai na yi maganin ki yar rainin hankali "
ta na gama fadar haka ta bace bat a wajen babu ita babu mai kama da ita
😨😨😨 KU TSAYA NA KORA RUWA ABUN YA FARA FIN KARFI NA
[16/09 à 18:17] M.N.M:

❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤

(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥

💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀

👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑

【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】

Marubuciyar littafin
【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】

【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】

____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________

PAGE 9 ❤🔥

da sauri ya sa Hannayan shi ya janye na ta , ya tashi da sauri ya fice dakin
a rude ta ke kiran sunan shi , amma ina ko sauraron ta ba ya yi , ya fice dakin da sauri ya fito corridor din ya shigo parlour

har Diya ya yi tafiyar shi , MALIKAT INAS da RIANNA sun dawo su na nan zaune parlourn tare da Nesrine

su na ganin yadda ya fito corridor din ya na saurin nan su ka san ba lafiya ba
ko ta kan su bai bi ba ya sa kafa ya fice parlourn ya fita part din baki daya

ya na fita MALIKAT INAS ta kali RIANNA ta ce mata " Tashi ki dubo kar a je Zuciya ta debe shi , ya buge ta bai sani ba "

da sauri RIANNA ta tashi ta nufi corridor ta shiga bedroom din Inaya babu ko sallama

ta na shiga ta ga Inaya konce saman gadon ta , ta na latsa wayar ta ga sweet a bakin ta
Chapter 15 · 0% Book details