← Book details Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 46

Sashe 44

Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hargitse Raihan ta waiga don ganin wanda yake shirin dakatar da ita ga cika umarnin Abar bauta, tana waigawa ta hangi Alhaji Ƙarami abokin mahaifinta. A hankali ya fara takowa gabanta cikin izza yana faɗin, "Matata ce irin dana dasa don ya ci gaba da yaɗo domin samun farinciki da rayuwa mai morewa." Raihan cike da ƙarfin gwiwa ta juya wurinsa tana cewa, "Wa'adin yabanyarka ya zo ƙarshe don a yanzu ba sai gobe ba zan sallamawa abar bauta jininta, ko mahaifana basu isa su dakatar da ni ga aiwatar da wannan kudurin ba." A zabure Alhaji Ƙarami ya fisgo Raihan da niyyar illata ruhinta, da sauri ta kauce ya kaiwa ƙasa duka. Duk abin da yake faruwa babu wanda ya lura daga masu naƙudar dake cikin halin naƙuda har zuwa Nurses ɗin da suke taimaka musu. Raiha ta kalle shi a fusace ta nuna shi da yatsa tana faɗin, "Ka fita a ido tun ban hallaka ruhinka kai da matarka ba, ka barni na yi abin da ya kawo ni tun ban fusata na yi ɓarnar da za ta girgiza ruhinka ba." Ko ba a faɗa ba Alhaji Ƙarami ya san wacece Raihan a cikin Daular ƙungiyar asiri, dukda ba ƙungiyarsu ɗaya ba ya samu labarinta da jimawa a wurin Babban Dodo, tun da jimawa ya so ya ringajayi ruhinta zuwa ta su ƙungiyar amma Huzaifa ya yi kaka gida ya hana shi aiwatar da abin da ya yi niyya. Amma dukda ya san wannan ƙarfin iko nata ba zai hana shi tsayawa tsayin daka don ganin ya ƙwato rayuwar Matarsa ba don ita ce komai na shi a rayuwa. Ya kalleta cikin dakiya da ƙarfin zuciya ya ce, "Na salwantar da rayuwar Mahaifana don cimma burina, na sadaukar da ƙwayoyin haihuwar jikin matata don samun farincikina, duk wani ɗigon numfashi da matata take yi ƙarin arzikina ne, matsawar babu ita duk wahalar da na yi ta tsawon shekaru ta kau don haka dole na dakatar da ke." Raihan na cikin sauraronsa ta ji kuka jariri a gefenta tana dubawa ta ga ta biyun ce ta haihu sai Matar abokin mahaifinta da suke taƙaddama akanta ita kaɗai ta rage, Raihan ta bushe da wata mahaukaciyar dariya haɗe da dukan ƙasa wurin, nan take wasu manyan kunamu suka fara fitowa suna tunkarar wurin da Alhaji ƙarami yake, da sauri suka fara rarrafawa har suka mammaƙale a jikinsa suka fara kai masa sara ta ko'ina. Da sauri ta koma kan matarsa da take cikin wani hali tana nishi da alama ita ma kan jariri ya fara hararamar fitowa, juyawa ta yi wurin da Kunamun nan suke fitowa ta sa hannu ta ɗauko guda ɗaya ta leƙa ƙarƙashin matar ta tura mata kunamar ta cikin gabanta. Lokaci ɗaya matar ta ƙwalla wata irin gigitacciyar ƙara, Raihan ta saki wani shu'umin murmushi ta waiga wurin da Alhaji Ƙarami da yake ta ƙoƙarin ganin ya ƙwaci kansa ta hanyar amfani da tsafi da sihiri, amma tuni kunamun suka kaishi ƙasa. Takawa ta yi har gabansa ta tsugunna a saitin furkarsa ta furta, "Da ka barni na yi abin da yake gabana da ka ceci rayuwarka, ba na son shisshigi a lamurana don haka bana jira ga duk wanda zai kawo min matsala." Tana gama maganar ta miƙe zuwa gaban Matar Alhaji ƙarami da Nurses suka rufu a kanta don ganin sun kawo mata ɗauki, tana nan tsaye Likita ya ƙaraso kanta don har ya fara tunanin a yi mata CS Raihan ta fara bin su ɗaya bayan ɗaya da kallo sannan ta ɗauki ruhin Matar Alhaji Ƙarami ta wuce da ita zuwa kogon tsafinsu.

A gaban abar bauta ta ɗire ta a lokacin tuni ta fara fita daga hayyacinta saboda irin saran da kunamar take yi mata, Abar bauta ce ta miƙa hannunta ɗaya daga cikin hannuwa sama da Ashirin cikin ƙasan matar, da ƙarfi ta fisgo kunamar da aka saka mata. Wata uwar ƙarar ta sake ƙwallawa kamar ranta zai fita, Abar bauta ta sake tura hannunta a karo na biyu ta fisgo jaririn cikinta da tuni ƙungiyar asirin Mijinta suka zuƙe masa jini. Abar bauta wurgi ta yi da jariri zuwa ɗaya daga cikin kawunan jikinta nan take suka yayyage shi da haƙwaranta suka fatattaka namansa. Abar bauta ta dubi Raihan da ke tsaya ta fara magana da muryarta mara daɗi, "Aiki ya rage naki yau mun baki wuƙa da nama." Raihan na zuwa ta kafa kanta a ƙirjin matar za ta zuƙu jini da sauri abar bauta ta dakatar da ita da cewar, "Ba iya jininta kaɗai muke buƙata ba, muna buƙatar ki ɗebo mana kayan cikinta kafin mu sha jini, a cirowa Autan kai zuciyarta ya cinye." Raihan na gama sauraronta ta tsugunna tana kallon hannunta nan take wasu irin manyan farata suka fara tsiro mata a hannu masu kaifi da tsini kamar mashi, waɗansu manyan fiƙoƙi masu kama da fiƙoƙin zaki suka fara tsiro wa a cikin bakinta. Hannuwanta ta tura cikin gaban matar faratanta na ratsa cikin jikinta har ta samu nasarar kwaso kayan cikinta, wata irin gigitacciyar ƙara take kwararawa iya ƙarfinta tun tana cikin hayyacinta har ta fita daga hayyacinta. Kamar yadda harshen kare yake lallagi hara Raihan ta zaro harshenta ta fara lasar jinin jikin kayan cikin. Tana gama siɗewa ta wurgawa Abar bauta ta karɓe ta haɗiyesu. Hannuwanta ta ƙara sawa a daidai ƙirjinta a lokacin tuni rai ya fita daga jikin matar, da zaƙwa-zaƙwan faratanta da farke kirjin matar ta zaro zuciyarta ta miƙawa Autan kan da ke jikin Abar bauta, ta saka kanta a saitin wurin da ta ciro zuciyar ta fara zuƙar jinin jikinta.

Raihan sai da ta sha jini ta yi ƙat sannan ta ɗago, tana sauke ajiyar zuciya. Hatsabibiya na zuwa ta ja gawar matar zuwa ɗakin arziƙi ta wurgata ciki. Wata irin guɗa ce ta tashi a wurin mai haɗe da walƙiya nan take ƙofar ɗakin ta shafe kamar ba'a taɓa ƙera ƙofa a wurin ba. Abar bauta ta dubi Raihan cikin farinciki ta ce, "Kin haure mataki na farko a cikin ƙungiya yanzu za ki wuce zuwa mataki na gaba, muna buƙatar jinin Mahaifiyarki. Za mu sassauta miki don ba za mu bari ki hallakar da ita da kanki ba, ungo wannan." Abar bauta ta miƙawa Raihan wani kaifaffan ƙashin bil'adama, sai dai kafinsa tamakar kaifaffiyar wuƙa haka yake. Ba musu Raihan ta ƙarasa ta amsa da hannu bibbiyu tana jiran umarninta.

Abar bauta ta miƙe tsaye tana faɗin, "Wannan da kike gani ƙashin bayan mahaifiyata ne, ki je da shi ki yanki ɗan ƙaramin yatsan mahaifiyarki ki kawo mana sauran aikin yana gare mu idan kika yi haka kin haure mata ki na biyu idan kika tafi mataki na ƙarshe tayuwu matsayinki ya zarce namu domin ke ɗin ta musamman ce, kina da bambamci da mu ƙungiya tana alfahari da ke." Raihan ta russuna cikin girmamawa sannan ta fice daga kogon dutsen.
A lokacin da ta koma gida, gidan ya yi tsit babu kowa da alama duk sun yi bacci. A can gefe ta hangi Mama Uwani da wata mai siffarta a cikin ɗakinta. Ko kaɗan bata damu ba don a baya ma ta ga irin haka, sai ta yi tsammanin duk yana daga cikin aikin abar bauta ne. Kai tsaye ɗakin Mahaifinta ta wuce don tasan a cen mahaifiyarta take kwana, Daddy ta hanga a kan kujera yana danne-danne a laptop ɗinsa a gefe ɗaya ga cool misic yana tashi don idan yana aikin dare ya fi jin daɗin aiki yana jin sanyayyar waƙa musamman ta turawa. Bata bi ta kansa ba ta ƙarasa gefen gadon da Mahaifiyarta take kwance.

😰RASHIN TAUSAYIN RAIHAN YA FARA YIN YAWA, INA TSORON TA ZAMA SHUGABA A WURIN. WAI INA LABARIN KABIRU KUMA WANENE MAI YAWAN BASHI SHAWARAR NAN? SHIN ABOKIN DADDY YANA MUTUWA KO ZAI ƊAUKI FANSA AKAN MUTUWAR MATARSA? WANNE DALILI NE YA SA HUZAIFA ZAI SA A KAI RAIHAN INDIA? IDAN YA KAITA INDIA TA FITA DAGA ƘUNGIYA NE KO YAYA?🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️ CHAKWAKIYAR ƘARA GABA TAKE YI😂 MAZA HANZARTA KI BIYA NAKI KAR A YI BABU KE DON WANNAN SHI NE SHAFI NA BIYUN ƘARSHE💃🏼

Share Fisabilillah🌚
*ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*

© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

LAST FREE PAGES 10

Ilahirin jikin Mommy ban da karkarwa babu abin da yake yi saboda tsananin tsoro, firgici da tashin hankali. A takure take a ƙuryar gado ta sunkuyar da kanta ƙasa saboda tozali da ta yi wata shirgigegiyar mummunar hallita, girman hallitar ta zarce goggon biri ga wasu irin ƙwala-ƙwalan idanu da suka zazzago kamar za su faɗo ƙasa. Bakinta ban da fiƙoƙi babu komai a ciki sai ƙaton hancinta mai ƙofofi takwas, tare da manyan ƙahunhuna guda biyu. Sautin takun Hallitar kan iya nakasta dodon kunne don haka Mommy ta sa hannuwa biyu ta toshe kunnenta da take jin sa kamar zai tarwatse, Hannuwan hallitar kama suke da ƙafafuwan doki don haka a duƙushe take tafiya rafkeken kanta shi ne a gaba. Jin shirun takunta ya sa Mommy ta ɗago da kanta a zatonta ko hallitar ta ɓace daga wurinta, sai dai tana ɗagowa suka haɗa ido da hallitar nan take ta hango Raihan maƙale a hannun hallitar tana kuka tana miƙawa Mahaifiyarta hannu, jikin mommy har rawa yake yi ta yunƙura don zuwa wurin hallitar tana faɗin, "Don Allah ki bani ƴata ita kaɗai na mallaka karki hallakata, Hallitar ce ta fara ja da baya tare da Raihan ta fara yunƙurin kai kan Raihan zuwa bakinta don ta laƙumeta, da sauri Mommy ta yunƙura cikin tashin hankali ta furta, "Raaaaihaaaaan."

(Allah sarki Uwa kenan😰 Duk tsanani Mahaifiya ba za ta so ganin abin da zai cutar da Ƴarta/Ɗanta ba.)
Chapter 44 · 0% Book details