Sashe 41
Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuska ba walwala ta ce, "Hatsabibiya akwai tarin matsaloli domin Huzaifa ya saka ni a gaba, bayan Huzaifa akwai wani bafulatanin maigadinsu da alama zai kawo mana matsala. Amma wanda ya fi kawo mana matsala Huzaifa ne, don haka na ce ba zan yi ƙasa a gwiwa ba sai mun san abin yi don yanzu haka..."
Tun Intisar bata rufe baki ba Hatsabibiya Bungulu ta katseta da cewar, "Duk na ga abin da ya faru har É—aukan Raihan da ya yi zuwa tsibirinsa." Intisar ta jinjina kai cikin huci tana cewa, "Da alama ya tsoratar da ita kuma a kowanne lokaci tana gabda bijirewa umarninmu."
"Sai mu kashe Huzaifa idan zai kawo mana matsala." Hatsabibiya ta faɗa kanta tsaye ba tare da ji shakku ko shayi ba." A firgice Intisar ta ɗago cikin tashin hankali ta zubawa Hatsabibiya ido, bakinta na rawa ta furta. "Kin manta wanene Huzaifa a wurina? Mijina ne fa." Hatsabibiya ta wara hannuwa cikin halin ko'inkula ta ce, "Ci gabanki ya fi zamantakewarki da shi don haka bana ganin zai amfane ki da komai." Intisar ta turɓune fuska ta ci gaba da cewa, "Ba zan lamince a kashe mijina kuma uban ƴaƴana ba, amma tabbas dole a nemi wata hanyar da za a samu mafita."
🤠NA SAN DA YAWA ZA KU YI MAMAKIN JIN INTISAR MATAR HUZAIFA CE, KO KUN TUNO MUGAZA😂 ITA CE INTISAR. AMMA MAI YA SA HUZAIFA BAI GANE TA BA HAR SUKE TAKUN-SAƘA, SHIN WACCE RIBA MUGAZA ZA TA CI DA TA JEFA RAIHAN A ƘUNGIYAR ASIRI? IDAN SU MOMMY SUKA KOMA SHARAƊA SUN TSIRA KO DA SAURAN TAFIYA?
Share pls🌚
[11/5, 3:26 PM] Mai Agogo: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*
© *AMEERA ADAM*
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
FREE PAGE 8
Ilahirin jikin mommy rawa ya ɗauka Aunty lubna ta zaro ido hankali a tashe don ko a mafarki bata taɓa cin karo da wannan mummunan abin da Raihan ta aikata ba. Mommy tana son tunkarar Raihan amma tana gudun hukuncin da za ta zartar a kanta, murya na rawa ta dubi Raihan ta ce, "Raihan lafiya me kike yi haka? Ƙadangare ne fa a hannunki." Raihan da har lokacin idonta jawur suke ta sake kai kallonta kan ƙadangaren hannunta, ta sake saka wurin jelarsa a baki ta cisgeta da ƙarfin tsiya ta kalli saitin da su Mommy suke ta tofar a wurin. Wani irin huci ta fara yi idanunta na sake firfitowa ta ce, "Ɗana yake shirin cinye min don haka dole na hallaka shi." Mommy ta tunkari wurin tana son Raihan ta wurgar da ƙadagaren hannunta amma tsoron abin da kaje ya zo ya hanata. Don a lokacin da take da shekara goma ntana da makamancin ciwon ta ya tashi ta taɓa cirewa wani almajiri ɗan yatsa, a lokacin shi ma zuwa ya yi zai ƙwaci agwagwar malaminsu da ta fito kiwo Raihan da Mommy sun fito daga mota, a lokacin da suka kai ziyara Albasu. Tuno da haka ya sa mommy take son tunkararta amma tana jin tsoro. Daga nesa da ita Mommy ta leƙa fuskarta tana faɗin, "Raihan ki yarda abin hannunki." Cikin wani irin ƙaraji ta nufo wurinsu gadan-gadan da ihu tini ba shiri su Mommy suka fice a guje kowa yana gudun ceton ransa.
Hankali a tashe mommy ta nufi sashen Daddy tana ƙwala masa kira. A bakin ƙofa ta ci karo da shi tana ganinsa ta fara nuna masa hanya tana faɗin, "Alhaji Raihan ce..." Maganarta ta maƙale saboda yadda take sauke ajiyar zuciya. A zabure Daddy ya kama kafaɗarta yana jijjigawa yana faɗin, "Me ya samu Raihan ɗin ki faɗa min tana ina?" Hanya ta riƙa nuna masa tana faɗin, "Tana can ta tsintsinka ƙadangare da haƙoranta." Da gudu ya nufi hanyar ɗakin Raihan hankali a tashe. Nan take ragowar mutanen da ke cikin gidan suka yi tsilli-tsilli, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci tana cikin matsanancin tashin hankali.
Daddy kai tsaye ɗakin da Raihan take ciki ya tunkara yana shiga ya same ta a cen gefe ta faɗi da alama bata numfashi. Kallon ɗakin ya fara yi saboda yadda jinin ƙadangaren ya ɓata saman carpet ɗin ɗakin, daga gefen hannunta ya hangi gangar jikin ƙadangaren hannunta ya jiƙe sharkaf da jini. A hankali ya ƙarasa wurin ya mirgino da ita yana ambatar sunanta muryarsa a raunace, shiru ne ya ratso a ɗakin babu abin da yake tashi sai karar AC da saukar numfashin Daddy. Tsugunnawa ya yi a gabanta ya tallafo da kanta zuwa kan cinyarsa, murya na rawa ya furta: "Me yake samunki ne Raiha? Me ya sa waɗannan abubuwan suke faruwa da ke?" Kuka ne ya ci ƙarfinsa ya kafa kansa a jikinta yana wani irin kuka mai tsuma zuciya. Daga bakin ƙofa Mommy ce ta shiga jiki a sanyaye, ita kanta lamarin Raihan ya fara bata tsoro. Kusan shekara goma sha biyar kenan suna fama da abu ɗaya, babban tashin hankalin da ciwon kullin gaba yake yi baya raguwa. A sanyaye ta zauna a gefen Daddy ta ce, "Daddyn Raihan." Ɗagowa ya yi ya dube ta idonsa na ci gaba da zubda ƙwallah, ita ma hawaye ne ya fara zuba a fuskarta ta sa hannu ta share sannan ta ci gaba da cewa, "Ka daina kuka don yanzu babu buƙatarsa a gurbin halin da muke ciki..." Tun bata rufe baki ba Daddy ya katseta da cewar, "Ido yana zubda hawaye ne ba don gangar jiki da ruhi suna buƙata ba, sai don samun sauƙi ga raɗaɗin ƙunan zuciya. A da na ɗauka rashin haihuwa babban masifa ne a gare ni sai ga shi a yau na wayi gari Allah ya bani gudan jinina ga kuma masifar da tafi min rashin haihuwar..." Da sauri Mommy ta rufe masa baki tana girgiza kai ta ce, "Bai kamata ka riƙa furta irin kalmomin nan ba, domin duk abin da ya samu bawa yana daga Ubangiji shi ya fi mu sanin dalilinsa na yin haka." Mommy ta numfasa sannan ta ci gaba da cewa, "Ya zama wajibi ciwon yarinyar nan a koma yin da Islamic don wannan yana da alaƙa da shafar aljanu..." A razane ya katse ta yana faɗin, "Kina hauka ne? Na gargaɗe ki da ki daina danganta jinina da jinsin aljanu." Wanna karon mommy ita ma hassala ta yi ta ci gaba da cewa, "Kar ka sake furta kalma ta ƙasƙanci a kaina, don duk taƙamar da kake yi ba kai kaɗai ka haifeta. Raihan ƴata ce idan kai ba za ka nema mata maganin Islamic ba dole ni zan nema mata." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin, Daddy ko a jikinsa tana fita ya ɗauki waya ya kira likitan da ke duba Raihan, zayyana masa komai ya yi sannan suka yi sallama ya ci gaba da zubawa Raihan ido yana tunane-tunane a zuciyarsa.
Lokacin da Macijiyar ta É“ace daga É—akin Kabiru, daga gefen hagunsa ya fara jin wani irin gurnani irin na riÆ™aƙƙun kumurcin maciji, a hargitse ya sake miÆ™ewa yana kalle-kalle bakinsa na furta Amanarrasulu don a tunaninsa macijin ne zai sake bayyanar masa. Ya jima yana jin wannan gurnanin daga baya ya ji shiru komai ya É—auke daga dodon kunnensa, daga jikin hannun rigarsa wata fata ya ga ta kwakkwaÉ“o irin saÉ“ar fatar maciji wacce yake yi. Da sauri ya É—ago ta cikin tashin hankali don lamari ya fi Æ™arfin tunaninsa, ido ya zurawa gwiwar hannunsa ta wurin da fatar ta faÉ—o ya ga wurin ya sake yin sheÆ™i tamkar bayan maciji. Kwalla ce ya ji ta zubo masa saboda duk wanda ya lura da halin da yake ciki ba zai taÉ“a zama a kusa da shi ba, kallo É—aya za ka yi wa jikinsa ya firgita ka don bambamcinsa da maciji kai, hannu da Æ™afafuwa. A hankali ya Æ™arasa wurin buhun kayansa, nan take ya fara zazzagewa yana birkito kayan da zai saka don ya rufe jikinsa. Sanin kansa ne ko masu aikin gidan suka fahimci halin da yake ciki zamansa a cikin gidan ya Æ™are balle kuma a ce Alhaji ya lura da yadda surar jikinsa ta koma. Sai da ya tura Æ™ofarsa ya rufeta ruf don kar wani ya turo, sannan ya tuÉ“e rigar jikinsa da yake mai gajeren hannu ce. A jikin mudubin ya tsaya yana Æ™arewa jikinsa kallo fatar jikinsa ta koma sak irin ta maciji, wani hawayen ne ya sake gangaro masa ya sa hannu ya share sannan ya É—auko wata tsohuwar rigar shadda mai dogon hannu, ya É—auko wani tsohon mayafinsa da wanda ya gada a wurin mahaifiyarsa ya naÉ—e wuyansa da shi. A jikin bango ya jingina a fili ya fara magana cikin karyewar zuciya, "Allah sarki Baffajo ba don rashin lafiyarka ba, da babu abin da zai hanani barin wannan gidan, don da alama wannan ba wurin zama ba ne." Kabiru ya É—aga hannu sama ya ci gaba da cewa, "Allah ka bawa Baffajo lafiya, da yardar Allah sai na bar gidan nan don na nemawa kaina lafiya." Daga gefensa ya ji an bushe da dariya, yana juyawa ya hangi matashiyar budurwa tana tsaye tsirara babu kaya a jikinta. Hannuwa biyu ta wara masa tana faÉ—in, "Ina da hanyar da zan kawo maka mafita matuÆ™ar za ka bani dama." Kabiru ya kauda kansa gefe yana faÉ—in, "Wa'iyazubillah." Æangaren da ya juya fuskarsa ta sake komawa tana faÉ—in, "Indai akan matsalar abin da ya faru da jikinka ne zan warkar maka da shi matsawar za ka bani haÉ—in kai." Kabiru ya É—ago da kansa yana shirin yi mata magana, karaf idonsu suka haÉ—u wuri É—aya nan take ya ji tsigar jikinsa na tashi. Da Æ™yar ya iya saita kansa sannan ya furta, "Ki taimaka min ki raba ni da wannan fatar macijin, ki gaya min me kike buÆ™ata daga wurina yanzu na aiwatar miki?"
Tun Intisar bata rufe baki ba Hatsabibiya Bungulu ta katseta da cewar, "Duk na ga abin da ya faru har É—aukan Raihan da ya yi zuwa tsibirinsa." Intisar ta jinjina kai cikin huci tana cewa, "Da alama ya tsoratar da ita kuma a kowanne lokaci tana gabda bijirewa umarninmu."
"Sai mu kashe Huzaifa idan zai kawo mana matsala." Hatsabibiya ta faɗa kanta tsaye ba tare da ji shakku ko shayi ba." A firgice Intisar ta ɗago cikin tashin hankali ta zubawa Hatsabibiya ido, bakinta na rawa ta furta. "Kin manta wanene Huzaifa a wurina? Mijina ne fa." Hatsabibiya ta wara hannuwa cikin halin ko'inkula ta ce, "Ci gabanki ya fi zamantakewarki da shi don haka bana ganin zai amfane ki da komai." Intisar ta turɓune fuska ta ci gaba da cewa, "Ba zan lamince a kashe mijina kuma uban ƴaƴana ba, amma tabbas dole a nemi wata hanyar da za a samu mafita."
🤠NA SAN DA YAWA ZA KU YI MAMAKIN JIN INTISAR MATAR HUZAIFA CE, KO KUN TUNO MUGAZA😂 ITA CE INTISAR. AMMA MAI YA SA HUZAIFA BAI GANE TA BA HAR SUKE TAKUN-SAƘA, SHIN WACCE RIBA MUGAZA ZA TA CI DA TA JEFA RAIHAN A ƘUNGIYAR ASIRI? IDAN SU MOMMY SUKA KOMA SHARAƊA SUN TSIRA KO DA SAURAN TAFIYA?
Share pls🌚
[11/5, 3:26 PM] Mai Agogo: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*
© *AMEERA ADAM*
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
FREE PAGE 8
Ilahirin jikin mommy rawa ya ɗauka Aunty lubna ta zaro ido hankali a tashe don ko a mafarki bata taɓa cin karo da wannan mummunan abin da Raihan ta aikata ba. Mommy tana son tunkarar Raihan amma tana gudun hukuncin da za ta zartar a kanta, murya na rawa ta dubi Raihan ta ce, "Raihan lafiya me kike yi haka? Ƙadangare ne fa a hannunki." Raihan da har lokacin idonta jawur suke ta sake kai kallonta kan ƙadangaren hannunta, ta sake saka wurin jelarsa a baki ta cisgeta da ƙarfin tsiya ta kalli saitin da su Mommy suke ta tofar a wurin. Wani irin huci ta fara yi idanunta na sake firfitowa ta ce, "Ɗana yake shirin cinye min don haka dole na hallaka shi." Mommy ta tunkari wurin tana son Raihan ta wurgar da ƙadagaren hannunta amma tsoron abin da kaje ya zo ya hanata. Don a lokacin da take da shekara goma ntana da makamancin ciwon ta ya tashi ta taɓa cirewa wani almajiri ɗan yatsa, a lokacin shi ma zuwa ya yi zai ƙwaci agwagwar malaminsu da ta fito kiwo Raihan da Mommy sun fito daga mota, a lokacin da suka kai ziyara Albasu. Tuno da haka ya sa mommy take son tunkararta amma tana jin tsoro. Daga nesa da ita Mommy ta leƙa fuskarta tana faɗin, "Raihan ki yarda abin hannunki." Cikin wani irin ƙaraji ta nufo wurinsu gadan-gadan da ihu tini ba shiri su Mommy suka fice a guje kowa yana gudun ceton ransa.
Hankali a tashe mommy ta nufi sashen Daddy tana ƙwala masa kira. A bakin ƙofa ta ci karo da shi tana ganinsa ta fara nuna masa hanya tana faɗin, "Alhaji Raihan ce..." Maganarta ta maƙale saboda yadda take sauke ajiyar zuciya. A zabure Daddy ya kama kafaɗarta yana jijjigawa yana faɗin, "Me ya samu Raihan ɗin ki faɗa min tana ina?" Hanya ta riƙa nuna masa tana faɗin, "Tana can ta tsintsinka ƙadangare da haƙoranta." Da gudu ya nufi hanyar ɗakin Raihan hankali a tashe. Nan take ragowar mutanen da ke cikin gidan suka yi tsilli-tsilli, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci tana cikin matsanancin tashin hankali.
Daddy kai tsaye ɗakin da Raihan take ciki ya tunkara yana shiga ya same ta a cen gefe ta faɗi da alama bata numfashi. Kallon ɗakin ya fara yi saboda yadda jinin ƙadangaren ya ɓata saman carpet ɗin ɗakin, daga gefen hannunta ya hangi gangar jikin ƙadangaren hannunta ya jiƙe sharkaf da jini. A hankali ya ƙarasa wurin ya mirgino da ita yana ambatar sunanta muryarsa a raunace, shiru ne ya ratso a ɗakin babu abin da yake tashi sai karar AC da saukar numfashin Daddy. Tsugunnawa ya yi a gabanta ya tallafo da kanta zuwa kan cinyarsa, murya na rawa ya furta: "Me yake samunki ne Raiha? Me ya sa waɗannan abubuwan suke faruwa da ke?" Kuka ne ya ci ƙarfinsa ya kafa kansa a jikinta yana wani irin kuka mai tsuma zuciya. Daga bakin ƙofa Mommy ce ta shiga jiki a sanyaye, ita kanta lamarin Raihan ya fara bata tsoro. Kusan shekara goma sha biyar kenan suna fama da abu ɗaya, babban tashin hankalin da ciwon kullin gaba yake yi baya raguwa. A sanyaye ta zauna a gefen Daddy ta ce, "Daddyn Raihan." Ɗagowa ya yi ya dube ta idonsa na ci gaba da zubda ƙwallah, ita ma hawaye ne ya fara zuba a fuskarta ta sa hannu ta share sannan ta ci gaba da cewa, "Ka daina kuka don yanzu babu buƙatarsa a gurbin halin da muke ciki..." Tun bata rufe baki ba Daddy ya katseta da cewar, "Ido yana zubda hawaye ne ba don gangar jiki da ruhi suna buƙata ba, sai don samun sauƙi ga raɗaɗin ƙunan zuciya. A da na ɗauka rashin haihuwa babban masifa ne a gare ni sai ga shi a yau na wayi gari Allah ya bani gudan jinina ga kuma masifar da tafi min rashin haihuwar..." Da sauri Mommy ta rufe masa baki tana girgiza kai ta ce, "Bai kamata ka riƙa furta irin kalmomin nan ba, domin duk abin da ya samu bawa yana daga Ubangiji shi ya fi mu sanin dalilinsa na yin haka." Mommy ta numfasa sannan ta ci gaba da cewa, "Ya zama wajibi ciwon yarinyar nan a koma yin da Islamic don wannan yana da alaƙa da shafar aljanu..." A razane ya katse ta yana faɗin, "Kina hauka ne? Na gargaɗe ki da ki daina danganta jinina da jinsin aljanu." Wanna karon mommy ita ma hassala ta yi ta ci gaba da cewa, "Kar ka sake furta kalma ta ƙasƙanci a kaina, don duk taƙamar da kake yi ba kai kaɗai ka haifeta. Raihan ƴata ce idan kai ba za ka nema mata maganin Islamic ba dole ni zan nema mata." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin, Daddy ko a jikinsa tana fita ya ɗauki waya ya kira likitan da ke duba Raihan, zayyana masa komai ya yi sannan suka yi sallama ya ci gaba da zubawa Raihan ido yana tunane-tunane a zuciyarsa.
Lokacin da Macijiyar ta É“ace daga É—akin Kabiru, daga gefen hagunsa ya fara jin wani irin gurnani irin na riÆ™aƙƙun kumurcin maciji, a hargitse ya sake miÆ™ewa yana kalle-kalle bakinsa na furta Amanarrasulu don a tunaninsa macijin ne zai sake bayyanar masa. Ya jima yana jin wannan gurnanin daga baya ya ji shiru komai ya É—auke daga dodon kunnensa, daga jikin hannun rigarsa wata fata ya ga ta kwakkwaÉ“o irin saÉ“ar fatar maciji wacce yake yi. Da sauri ya É—ago ta cikin tashin hankali don lamari ya fi Æ™arfin tunaninsa, ido ya zurawa gwiwar hannunsa ta wurin da fatar ta faÉ—o ya ga wurin ya sake yin sheÆ™i tamkar bayan maciji. Kwalla ce ya ji ta zubo masa saboda duk wanda ya lura da halin da yake ciki ba zai taÉ“a zama a kusa da shi ba, kallo É—aya za ka yi wa jikinsa ya firgita ka don bambamcinsa da maciji kai, hannu da Æ™afafuwa. A hankali ya Æ™arasa wurin buhun kayansa, nan take ya fara zazzagewa yana birkito kayan da zai saka don ya rufe jikinsa. Sanin kansa ne ko masu aikin gidan suka fahimci halin da yake ciki zamansa a cikin gidan ya Æ™are balle kuma a ce Alhaji ya lura da yadda surar jikinsa ta koma. Sai da ya tura Æ™ofarsa ya rufeta ruf don kar wani ya turo, sannan ya tuÉ“e rigar jikinsa da yake mai gajeren hannu ce. A jikin mudubin ya tsaya yana Æ™arewa jikinsa kallo fatar jikinsa ta koma sak irin ta maciji, wani hawayen ne ya sake gangaro masa ya sa hannu ya share sannan ya É—auko wata tsohuwar rigar shadda mai dogon hannu, ya É—auko wani tsohon mayafinsa da wanda ya gada a wurin mahaifiyarsa ya naÉ—e wuyansa da shi. A jikin bango ya jingina a fili ya fara magana cikin karyewar zuciya, "Allah sarki Baffajo ba don rashin lafiyarka ba, da babu abin da zai hanani barin wannan gidan, don da alama wannan ba wurin zama ba ne." Kabiru ya É—aga hannu sama ya ci gaba da cewa, "Allah ka bawa Baffajo lafiya, da yardar Allah sai na bar gidan nan don na nemawa kaina lafiya." Daga gefensa ya ji an bushe da dariya, yana juyawa ya hangi matashiyar budurwa tana tsaye tsirara babu kaya a jikinta. Hannuwa biyu ta wara masa tana faÉ—in, "Ina da hanyar da zan kawo maka mafita matuÆ™ar za ka bani dama." Kabiru ya kauda kansa gefe yana faÉ—in, "Wa'iyazubillah." Æangaren da ya juya fuskarsa ta sake komawa tana faÉ—in, "Indai akan matsalar abin da ya faru da jikinka ne zan warkar maka da shi matsawar za ka bani haÉ—in kai." Kabiru ya É—ago da kansa yana shirin yi mata magana, karaf idonsu suka haÉ—u wuri É—aya nan take ya ji tsigar jikinsa na tashi. Da Æ™yar ya iya saita kansa sannan ya furta, "Ki taimaka min ki raba ni da wannan fatar macijin, ki gaya min me kike buÆ™ata daga wurina yanzu na aiwatar miki?"