Sashe 31
Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da Asuba bayan su Inno sun gabatar da sallah suna zaune kowacce a sallayarta suna jan carbi, Goggo ta dubi Inno ta ce: "Wai ni kuwa yarinyar ta tashi sallah kuwa don ko motsinta ban ji ba, saboda Allah neman haihuwa ya fi bautar Ubaniji. Jiya na ga saboda neman haihuwa raba dare suka yi a wurin wancen Kafiriin, gaskiya a tambayi Malamai an ya; ya hallata neman haihuwa wurin kafiri." Inno takaici ya fara rufeta, ta dubi Goggo ta ce, "Zinaru ki yi ta kanki idan kika kafirta min yarinya a yau ba sai gobe wallahi sai Audullahi ya mayar da ke Albasu. Kafira ce da har yanzu za ta zauna babu sallah babu salati?" Goggo cikin nuna rashin damuwa ta wara hannuwa tana faɗin, "Allah shi ne masanin daidai, ba zan amsa ba ki sa na yi wa ƴar mutane ƙazafi akan abin da ban ji ba ban gani ba, ni dai na san da Hasiya ta tashi za ta leƙo wurinmu. Bari ki ga na je na tashe ta ko na samu lada mai tsoka, bar zancen Albasu tun da ko jini baki taɓa zubarwa a cen balle a binne mabiyyarki." Goggo na ƙarasa maganar ta fice daga ɗakin, tana tafe tana mita har ta ƙarasa bakin ƙofa tana ƙoƙarin buɗe ƙofar sai ga Inno ta rufo mata baya ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Saboda Allah Zinaru in haifi abartawa a ciki amma ki nemi ki yi mana farraƙu da ita, Allah ya sani idan Hasiya ta ga ban tashe ba na ɓalɓalce don ɗauka za ta yi baƙin cikin shiga aljanna nake yi mata." Goggo bata bi ta kan Inno ba ta tura ƙofar tana rangaɗa sallama, kamar haɗin baki suka shiga ambatar sunan Hasiya amma shiru suka ji kamar an shuka dusa. Inno ce ta yaye zanin rufar jikinta nan take suka yi tozali da gawarta, kusan suman tsaye suka yi aka rasa mai furta koda kalma ɗaya ne. Nan take Inno ta yanke jiki ta faɗi, Goggo jiki na tsuma ta juye hanyar waje tana ƙwalawa Mommy kira. Can sashenta ta wuce saboda fargaba tini ta zubar da carbi don lokaci ɗaya ya tsinke ya tarwatse, da kusan rarrafe Goggo ta hau sama tun bata ƙarasa ba suka ci karo da Mommy shi kansa Daddy kiran Goggo ne ya sa shi fitowa daga ɗakinsa a lokacin yana zaune yana cike-ciken takardu.Hankali a tashe suka shiga jera mata tambayoyi ban da nuna musu ƙofa babu abin da take yi, sai da ƙyar suka samu ta iya furta, "Hasiya babu ta riga mu gidan gaskiya." Cikin rashin fahimta suka ce, "Wace Hasiya?" Saboda ko a kaɗan basu kawo Hasiya a ransu ba. Goggo cike da jin haushi ta ce, "Hasiya dai ƙanwarka Audullahi ko kana da wata Hasiyan ne." Kusan tare suka nufi hanyar sauka don zuwa su ganowa idanunsu.
Kamar masu rige-rige haka suka shiga ɗakin da Hasiya ke yashe a kan gado, Daddy ne ya fara zuwa kan Inno Mommy ta ƙarasa wurin gawar Hasiya ta fara tattaɓata tana ambatar sunanta amma shiru tafiya ta miƙa. Da hanzari Mommy ta wuce firji ta ɗebo ruwa ta fara yayyafawa Inno sannan ta yayyafawa Hasiya, nan take Inno ta fara motsawa saidai da alama bata cikin hayyacinta amma Hasiya ko alamar motsi bata yi. Daddy ne ya rungumo Inno ya fita a guje yana ƙalawa maigadi waya, kusan gware suka yi a hanya Daddy ya nufi wurin motoci yana faɗin, "Maza-maza buɗe min gate." Tun bai rufe baki ba Driver ya fara kiciniyar buɗe ƙofa nan take bawa motarsa wuta ya fice daga gidan, Mommy jiki a sanyaye ta bi bayan motar da kallo fuska ɗauke da hawaye. Ɗakin ta koma ta janyo hannun Goggo ta rufe ɗakin, kan kujera ta zauna ta rafka tagumi ban da hawaye babu abin da take yi, saboda ba ƙaramin shaƙuwa suka yi da Hasiya ba. Goggo ban da sintiri babu abin da take yi tana nan tsaye suka ga Mama Uwani ta fita, cikin rashin sani ta fara tambaya, Goggo da sai a lokacin kuka ya kubce mata cikin shassheka ta ce, "Bari Uwani yau mun wayi gari da tashin hankali Hasiya babu, yarinyar nan jiya-jiya muka gama hira da ita amma yau sai labari." A tsorace Mama Uwani ta nufi ɗakin don ganewa idonta, tana shiga ta samu gawar a kan gado cikin hanzari ta buɗe ta tana ƙarewa gawar kallo.
Ido ta zurawa gawar tana jinjina kai a hankali ya furta, "Tabbas akwai lauje ciki naɗi amma akwai ɓoyayyan al'amari a dangane da gawar nan." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin zuwa falo, ba a ɗauki lokaci ba sai ga Daddy ya dawo. Dawowarsa babu wuya mommy ta tashi Raihan ta sanar da ita halin da ake ciki, murtsuke ido ta yi tana yamutsa fuska ta ce, "Mommy waye ya mutu?" Mommy ta sake maimaita mata, "Mamanki Hasiya yanzu haka gawarta na ɗaki mutane sun fara taruwa." Lokaci ɗaya ta ji kanta ya yi mata nauyi dum! Har sai da ta runtse idonta ta buɗe ta dafa kanta da hannu biyu ta ce, "Mommy me ya sameta ta mutu?" Da sauri Mommy ta rufe mata baki tana faɗin, "Raihan wa yace miki sai an yi ciwo ake yin mutuwa?" Jikin Raihan ba ƙaramin mutuwa ya yi ba, a hanakali ta tashi tana haɗa hanya jikinta sanye da rigar bacci shara-shara babu abin da ta ɓoye na surarta. Ɗakin da Mama Hasiya take ta tunkara Mama Uwani na hangota da sauri ta nufi wurinta ta rungomata tsam a jikinta tana faɗin, "Uwar ɗakina sai haƙuri." Wani iri Raihan ta ji a jikinta yarr a lokaci ɗaya kanta ya yi mata yaaaam! Tsigar jikinta ce ta ci gaba da tashi, a hankali ta saki hannunta tana bin Raihan da wani mayatattacen kallo.
Kafin wani lokaci tuni gidan ya cika da mutane ban da koke-koke babu abin da ake yi, Raihan can gefe ta raɓe ta fashe da wani irin matsanancin kuka. Mai gidanta da aka gaya masa da farko ƙaryatawa ya yi sai da ya zo ya ganta, zama ya yi kamar mace ya yi ta kuka sai da ƙyar ya yi shiru. Kimanin ƙarfe goma aka gama wanke gawarta aka shiryata, ana gabda za a fita da ita sai ga Intisar ta turo ƙofa ta shiga gidan tana kallon mutanen gidan ɗaiɗai tana shigowa ana ɗaukan gawar, tana kalle-kalle Mama Uwani ta fisgi hannun Intisar ta ja ta ɗakin baya wanda baƙi suke sauka a ciki. Rai a matuƙar ɓace ta dubi Intisar ta ce, "Me ya kawo ki gidan nan?" Intisar dariya ta yi ta fara takawa a hankali sai da ta yi taku uku sannan ta juya ta kalli Mama Uwani ta ce, "Abin da ka ke yi cikin suffar tsofaffi shi ne ya kawo ni a wannan suffar."
[7/1, 6:00 PM] My Data sim number: *DUBU JIKAR MAI CARBI*
©AMEERA ADAM
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*
https://chat.whatsapp.com/KQd6gkViAXfKDTv7iWLJpV
FREE PAGE 1
Babban gida ne mai ɗauke da ɓangare daban-daban har kusan sashen mutum goma sha biyu. A taƙaice za mu iya cewa gidan gandu ne da ya haɗa Kakanni, 'ya'yaye da jikoki. Garin Ɗangwauro yana ɗaya daga cikin ƙanana ƙauyukan da ke cikin ƙwaryar Kano, Allah ya azurta su da noma, kiwo da kasuwansu. Gidan Malam Muhammadu mai dogon Carbi sanannan gida ne a kaf cikin garin Ɗangwauro. Tun daga titi idan ka tambaya za a kai ka har cikin gidan, sakamakon gida ne gidan yawa don wani lokaci mutane na yi masa laƙabi da gidan 'Ya'ya da yawa.
Gidan Mai dogon Carbi cike yake da mutane sakamakom wayar gari da suka yi da rasuwar rashin wannan Dattijo mai yawan shekaru, ba iya gidan ba hatta garin Ɗangwauro ya girgiza da rashin wannan Dattijon mai dogon zamani. Yaya Babba da Inna Furai sune matan wannan Dattijo da ya rasu mutuwar ba ƙarmin taɓa su ta yi ba.
Bisa ga al'adar Malam bahaushe a ranar da aka yi mutuwa mutane sun fi nuna damuwarsu ta hanyar koke-koke, kukan ma yana taƙaita yawancin bayan ankai mammaci. Hakan ce ta faru a gidan Mai dogon carbi domin an fita da gawarsa a yi mata sallah yara da Manya sai kuka suke yi.
A gefe ɗaya Hali dubu na hango rakuɓe sai muzurai take lokaci-lokaci tana share hawaye, sai dai cikin zuciyarta haushin mutanen gidan take ji saboda ta lura babu wanda yake bi ta kanta don ya rarrasheta, duk kuwa da irin gursheƙen kukan da take yi. Kallonsu ta fara yi tana ayyana irin abin da za ta yi domin ta janyo hankulansu kanta. Tun da ai ita gani take kamar ta fi su jin mutuwar koda suna yawan faɗa da Mai dogon carbi amma kafin ya rasu, ai ita ma Kakanta ne.
Kamar masu rige-rige haka suka shiga ɗakin da Hasiya ke yashe a kan gado, Daddy ne ya fara zuwa kan Inno Mommy ta ƙarasa wurin gawar Hasiya ta fara tattaɓata tana ambatar sunanta amma shiru tafiya ta miƙa. Da hanzari Mommy ta wuce firji ta ɗebo ruwa ta fara yayyafawa Inno sannan ta yayyafawa Hasiya, nan take Inno ta fara motsawa saidai da alama bata cikin hayyacinta amma Hasiya ko alamar motsi bata yi. Daddy ne ya rungumo Inno ya fita a guje yana ƙalawa maigadi waya, kusan gware suka yi a hanya Daddy ya nufi wurin motoci yana faɗin, "Maza-maza buɗe min gate." Tun bai rufe baki ba Driver ya fara kiciniyar buɗe ƙofa nan take bawa motarsa wuta ya fice daga gidan, Mommy jiki a sanyaye ta bi bayan motar da kallo fuska ɗauke da hawaye. Ɗakin ta koma ta janyo hannun Goggo ta rufe ɗakin, kan kujera ta zauna ta rafka tagumi ban da hawaye babu abin da take yi, saboda ba ƙaramin shaƙuwa suka yi da Hasiya ba. Goggo ban da sintiri babu abin da take yi tana nan tsaye suka ga Mama Uwani ta fita, cikin rashin sani ta fara tambaya, Goggo da sai a lokacin kuka ya kubce mata cikin shassheka ta ce, "Bari Uwani yau mun wayi gari da tashin hankali Hasiya babu, yarinyar nan jiya-jiya muka gama hira da ita amma yau sai labari." A tsorace Mama Uwani ta nufi ɗakin don ganewa idonta, tana shiga ta samu gawar a kan gado cikin hanzari ta buɗe ta tana ƙarewa gawar kallo.
Ido ta zurawa gawar tana jinjina kai a hankali ya furta, "Tabbas akwai lauje ciki naɗi amma akwai ɓoyayyan al'amari a dangane da gawar nan." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin zuwa falo, ba a ɗauki lokaci ba sai ga Daddy ya dawo. Dawowarsa babu wuya mommy ta tashi Raihan ta sanar da ita halin da ake ciki, murtsuke ido ta yi tana yamutsa fuska ta ce, "Mommy waye ya mutu?" Mommy ta sake maimaita mata, "Mamanki Hasiya yanzu haka gawarta na ɗaki mutane sun fara taruwa." Lokaci ɗaya ta ji kanta ya yi mata nauyi dum! Har sai da ta runtse idonta ta buɗe ta dafa kanta da hannu biyu ta ce, "Mommy me ya sameta ta mutu?" Da sauri Mommy ta rufe mata baki tana faɗin, "Raihan wa yace miki sai an yi ciwo ake yin mutuwa?" Jikin Raihan ba ƙaramin mutuwa ya yi ba, a hanakali ta tashi tana haɗa hanya jikinta sanye da rigar bacci shara-shara babu abin da ta ɓoye na surarta. Ɗakin da Mama Hasiya take ta tunkara Mama Uwani na hangota da sauri ta nufi wurinta ta rungomata tsam a jikinta tana faɗin, "Uwar ɗakina sai haƙuri." Wani iri Raihan ta ji a jikinta yarr a lokaci ɗaya kanta ya yi mata yaaaam! Tsigar jikinta ce ta ci gaba da tashi, a hankali ta saki hannunta tana bin Raihan da wani mayatattacen kallo.
Kafin wani lokaci tuni gidan ya cika da mutane ban da koke-koke babu abin da ake yi, Raihan can gefe ta raɓe ta fashe da wani irin matsanancin kuka. Mai gidanta da aka gaya masa da farko ƙaryatawa ya yi sai da ya zo ya ganta, zama ya yi kamar mace ya yi ta kuka sai da ƙyar ya yi shiru. Kimanin ƙarfe goma aka gama wanke gawarta aka shiryata, ana gabda za a fita da ita sai ga Intisar ta turo ƙofa ta shiga gidan tana kallon mutanen gidan ɗaiɗai tana shigowa ana ɗaukan gawar, tana kalle-kalle Mama Uwani ta fisgi hannun Intisar ta ja ta ɗakin baya wanda baƙi suke sauka a ciki. Rai a matuƙar ɓace ta dubi Intisar ta ce, "Me ya kawo ki gidan nan?" Intisar dariya ta yi ta fara takawa a hankali sai da ta yi taku uku sannan ta juya ta kalli Mama Uwani ta ce, "Abin da ka ke yi cikin suffar tsofaffi shi ne ya kawo ni a wannan suffar."
[7/1, 6:00 PM] My Data sim number: *DUBU JIKAR MAI CARBI*
©AMEERA ADAM
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*
https://chat.whatsapp.com/KQd6gkViAXfKDTv7iWLJpV
FREE PAGE 1
Babban gida ne mai ɗauke da ɓangare daban-daban har kusan sashen mutum goma sha biyu. A taƙaice za mu iya cewa gidan gandu ne da ya haɗa Kakanni, 'ya'yaye da jikoki. Garin Ɗangwauro yana ɗaya daga cikin ƙanana ƙauyukan da ke cikin ƙwaryar Kano, Allah ya azurta su da noma, kiwo da kasuwansu. Gidan Malam Muhammadu mai dogon Carbi sanannan gida ne a kaf cikin garin Ɗangwauro. Tun daga titi idan ka tambaya za a kai ka har cikin gidan, sakamakon gida ne gidan yawa don wani lokaci mutane na yi masa laƙabi da gidan 'Ya'ya da yawa.
Gidan Mai dogon Carbi cike yake da mutane sakamakom wayar gari da suka yi da rasuwar rashin wannan Dattijo mai yawan shekaru, ba iya gidan ba hatta garin Ɗangwauro ya girgiza da rashin wannan Dattijon mai dogon zamani. Yaya Babba da Inna Furai sune matan wannan Dattijo da ya rasu mutuwar ba ƙarmin taɓa su ta yi ba.
Bisa ga al'adar Malam bahaushe a ranar da aka yi mutuwa mutane sun fi nuna damuwarsu ta hanyar koke-koke, kukan ma yana taƙaita yawancin bayan ankai mammaci. Hakan ce ta faru a gidan Mai dogon carbi domin an fita da gawarsa a yi mata sallah yara da Manya sai kuka suke yi.
A gefe ɗaya Hali dubu na hango rakuɓe sai muzurai take lokaci-lokaci tana share hawaye, sai dai cikin zuciyarta haushin mutanen gidan take ji saboda ta lura babu wanda yake bi ta kanta don ya rarrasheta, duk kuwa da irin gursheƙen kukan da take yi. Kallonsu ta fara yi tana ayyana irin abin da za ta yi domin ta janyo hankulansu kanta. Tun da ai ita gani take kamar ta fi su jin mutuwar koda suna yawan faɗa da Mai dogon carbi amma kafin ya rasu, ai ita ma Kakanta ne.