← Book details Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 46

Sashe 29

Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shigar su ɗaki keda wuya, Mama Hasiya ƙanwar Daddy ta yi sallama cikin falon. Fara'a ɗauke a fuskarta ta shiga cikin falon. Mommy da murmushi ta tarbi Mama Hasiya tana faɗin, "Mai gidan da ba awo ba cefane, ba waya ba labari." Mama Hasiya ta zame mayafin jikinta tana faɗin, "Mutum da gidansa wacce waya zai yi." Mommy ta saki murmushi tana faɗin, "Barka da zuwa wai da yamman nan kike tafe." Mama Hasiya ta ajiye jakar hannunta tana faɗin, "Wallahi dole ce ta kawo ni, kin san Hubbi ya yi tafiya ƙafar Dubai to sun yi waya da DR John wai yau zai shigo gari so kin san matsalar hospital ɗin Dr John idan kana son ganinsa sai dare." Mommy ta sauya fuska cikin yanayin damuwa ta ce, "Allah ya sa a dace wai wancen karon ba ya ce ƙasa da six months komai zai iya faruwa ba? Ya ce za ki iya samu ciki a kowanne lokaci." Mama Hasiya ta jinjina kai ta ce, "To kin ga dai shiru, lamarin rashin haihuwar nan ba ƙaramin damuna yake yi ba. Tun hubbi bai fara damuwa ba yanzu na fuskanci abin ya fara damunsa, shekara sama da goma sha biyar ba haihuwa an ya ina da rabon ganin ƙwaina a duniya kuwa?" Mama Hasiya ta yi maganar idanunta na cikowa da ƙwallah. Cikin sigar lallashi Mommy ta dubi Mama Hasiya tana faɗin, "Komai kika ga ya faru da bawa da sanin Allah, ba a nan take ba. Komai fa lokaci ne mutane da dama akwai waɗanda suka fiki daɗewa kuma Allah ya kawo musu mafita, mu ci gaba da addu'a komai ya yi farko zai yi ƙarshe." Mama Uwani ta ƙaraso cikin falon fuskarta ɗauke da fara'a tana faɗin, "Hajiya barka da zuwa." Bayan sun gaisa ta fara kawo mata kayan ciye-ciye da shaye-shaye bata jima da barin wurin ba su Inno suka fito falo, nan take suka ci gaba da hira.

Mama Hasiya ƙanwar Daddy ce uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, tana auren wani hamshaƙin ɗan kasuwa a unguwar Hotoro. Sun shafe shekara goma sha biyar da auren saurayi da budurwa, sai dai Allah bai basu haihuwa ba duk wannan tsahon shekarun, sun yi yawon ƙasashe amma duk ba a dace ba har sai da suka fara ganin wani likita Dr John, ta taɓa samun ciki ta yi ɓari har sau biyu daga haka ko ɓatan wata bata sake yi ba, don haka ta nace wa Dr John lokaci-lokaci take zuwa ganin likita.

DR JOHN SPECIAL HOSPITAL shi ne sunan asibitin da Mama Hasiya take zuwa ganin likita, asibitin a bayan gidan su Mommyn Raihan yake. Duk ranar da Mama Hasiya za ta zo ganin likita a gidan Daddy take kwana saboda asibitin sai goman dare Dr John yake fara ganin patient, wannan dalilin ya sa idan ta ga likita take dawowa gidan É—an'uwanta ya kwana, yawaici tare suke zuwa da Mommy saboda mai gidanta yana tafiye-tafiye, kuma yawo babu inda ba su je ba don neman haihuwa.

Cikin Dare.

Wata irin guguwa mai ɗauke da amsa kuwwa marar daɗin sauraro ta fara karaɗe lungu da saƙon da ke cikin dodon kunnuwanta, a hankali iskar ta fara kaɗa labulayen ɗakinta. A hankali ta fara ratso bangawayen da gidan tana raɓewa ta jikin ƙananan shukokin da ke harabar gidan, ta jikin bangon ɗakinta ta ratso jikinta ɗauke da jajayen kaya masu ratsin baƙi haɗe da ɗishi-ɗishin busasshen jini a jikinta. Tana shiga ɗakin Raihan ta tsaya cak a bangon gudu, ta fara huro mata iska nan take Raihan ta miƙe zaune hannuwanta toshe a kunnuwanta ta dubi Intisar. Cikin wata irin girgiza ta ƙaraso wurin Raihan ta kama hannuwanta tana shirin yin magana Raihan ta ce, "Intisar me kika zo yi yanzu gidanmu?" Intisar bata bi ta kanta ba ta hura mata iska a fuska nan take ta fara layi tana shirin faɗuwa, da sauri Intisar ta tarota tana dafe kafaɗarta ta ce, "Za ki bi ni?" Babu musu Raihan ta gyaɗa mata kai, Intisar bata bi ta kanta ba ta riƙe hannunta nan take suka ɓace daga ɗakin.

Gudu suke zabgawa cikin sararin samaniya a can wani ƙasurgumin dajin wani makeken gida suka sauka, Raihan ban da ido babu abin da take bin ƙawarta Intisar da shi. A wani katafarn kogon dutse suka dira mai ɗauke da wasu irin mutane masu mummunar hallita, ɗauke suke da jajayan sitiru sai zanen jini a jikkunansu. Wata mummunar hallita ce a tsugunne mai ɗauke da kan barewa da manyan ƙahunhuna ga wani irin jini da yake ɗiga daga bakinta a cikin wani ƙaton faifai. Zuwansu ke da wuya wani tiƙeƙe da ya kasance babbansu ya dubi Intisar ya ce, "Hatsabibiya Bungulu na maraba da baƙuwa mai daraja." Intisar da dubi Raihan ta ce, "Ki yi gaisuwa ga Habibiya Bungulu ta saka miki albarka." Kamar bawa da uban gidansa haka Raihan ta dubi wannan hallitar ta duƙa kamar yadda ta ga suna yi ta miƙa gaisuwa. Da wani ƙaton sirinji wani ɗan tsamurmuri ya zuƙi jinin da wannan hallitar take ɗigarwa daga bakinta, a shammace ya samu damtsen hannun Raihan ya kafa mata har sai da ya juye jinin jikin sirinjin a jikinta, sannan ya zuƙo nata ya fesa a jikin hallitar. Lokaci ɗaya ta fara rawar ɗari kamar mai jin sanyi, tun tana daga tsaye har ta duƙushe a wurin tana karkarwa. Tana jima tana abu ɗaya sannan ta tsagaita da rawar ɗarin, a zabure ta miƙe tsaye cikin wani irin ƙarfi ta zurawa mummunar hallitar tana jiran umarninta.

Buɗe bakinsa ya yi nan take wasu baƙaƙen macizai suka fara fitowa daga bakinsa, suna faɗowa suke fasa kai suna zagaye Raihan. Cikin wani irin yanayi hallitar ta miƙe tsaye tana girgiza sannan ta fara magana da wani irin yare har sai da ta yi yare ya fi kala goma, sannan ta yi magana da harshen hausa.

"Tabbas mun yi babban kamun da muka jima muna jiran wannan rana. Domin ƙara tabbatar da abin da muke zargi goɗiya za ta kawo mana jini mafi muhimmanci wanda zan shayar da mai gidana domin samun lafiyarsa." Tun bai rufe baki ba Raihan ta russuna tana faɗin, "An gama Hatsabibiya Bungulu." Mummunar hallitar ta nunawa Raihan wata ƙatuwar ƙwarya mai cike da tafasasshen jini ta ce, "Babu buƙatar haka domin da alama ke shugaba ce, muna buƙatar jinin wannan matar yanzun nan..." Raihan ta amsa mata tun bata ƙarasa maganar ba da cewar, "Jininta ya halarta a gare ki, duk duniya babu jinin da za ki buƙata ya gagara a wurina." Tana rufe baki Hatsabibuya Bungulu ta miƙa mata wani busasshen ƙashi da alama ƙashin jikin bil'adam ne. Raihan na karɓa ta wuce cikin sararin samaniyar iskar sihiri bata tsaya ko'ina ba sai a katafaran cikin gidan Mahaifinta, sai da ta zaga ɗakunan gidan sannan ta dira a ƙofar ɗakin mahaifiyarta.

🤭🤭🤭 WASAN YANZU YA FARA, MAZA HANZARTA KI BIYA NA KI DON JIN WACECE AINIHIN ZAUJATU JINNUL-ASHIQ ƊIN, SHIN A CIKIN SU WACECE ƳAR GABAN GOSHIN ALJANIN SOYAYYAR? SHIN WACECE WANNAN INTISAR ƊIN KUMA WACECE HATSABIBIYA BUNGULU? 😁 AMSOSHIN NA GABA DON JIN ƘULALLEN ƊAURIN DA KE CIKIN LABARIN.

Share Fisabillah🌚
[11/5, 3:26 PM] Mai Agogo: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*

© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

FREE PAGE 4

Raihan na fita Intisar ta ƙarasa gaban Hatsabibiya Bungulu rai a matuƙar ɓace ta ce, "Hatsabibiya uwar hatsabibai, sai kai mai siffar dabba a bayan fage ki koma bil'adama. Babu hallitar da ta gagare ki rikiɗa duk girmanta duk ƙanƙantarta, yaya ina tunanin lokacin share mini hawayena ya zo amma na ga wankin hula yana shirin kaini dare. Na kawo Raihan domin a salwantar mini da rayuwarta amma da alama tana shirin samun fada a wurin nan, yake Hatsabibiya tun farko kin san ba haka muka yi da ke ba."

Hatsabibiya Bungulu ta yi girgiza lokaci ɗaya ta rikiɗa zuwa wata kyakkyawar budurwar, zaune take tsirara sai wasu sassan gaɓɓoɓin jikinta da ke rufe. Wani malalacin murmushi ta saki sannan ta dubi Intisar ta ce, "Da mun san kina da wannan yarinyar da tuni mun jima da umartarki ki kawo mana ita, sai dai kash! Silar saninta na daga gare domin biyan buƙatarki. Kin kawota domin mu kashe ta sai dai ba za ta mutu ba." Da hannuwa biyu Intisar ta sa ta toshe dodon kunnenta saboda yadda ta ji kalmar a kunnenta, a duniya idan da wacce ta tsana to Raihan ce. Lokaci ɗaya ta murtuke fuska tana shirin yin magana Hatsabibiya ta ci gaba da magana.

"Na tabbata baki san wacece Raihan ba, da kin san amfanin da za ta yi mana a cikin ƙungiya da bakinki bai furta kalmar kisa a tattare da ita ba. Shin ko kinsan Muraza?" Da sauri Intisar ta ɗago da kai tana kallon Hatsabibiya tana girgiza kai bakinta na rawa ta ce, "Ina zan santa ya ke Hatsabibiya mu da muke nemanta ido rufe." Matashiyar budurwar da ake kira da Hatsabibiya ta yi girgiza nan take ta rikiɗe zuwa surar wani ƙaton tsuntsu, sai da ya yi tsalle-tsallensa sannan ya koma kan kujerarsa ya zauna ya ci gaba da magana cikin siffar tsuntsu.
Chapter 29 · 0% Book details