Sashe 30
Bakar Daula Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Tabbas Raihan ita ce Muraza, tun shigowarta kogon dutsen nan alaminta da babban matsafi ya sanar da mu suka bayyana. Ƙofar nasarorinmu ta buɗe ƙarfin iko, tsafi da sihiri da ƙarfin ƙungiyar asirinmu za ta sake dawowa da ƙarfin ikonta, domin haske ya bayyana inuwarta ɗauke take tartsakin wuta mai halakar da magautanmu, za mu riƙe hannu bibbiyu domin saminta tamkar samun lu'ulu ne a ƙarƙashin teku, idan muka yi sake ta kubce mana tabbas mun tafka babbar asara." Intisar ta faɗaɗa murmushinta sai da ta yi taku biyu sannan ta waiwayo ta ce, "Haƙiƙa zan jinkirta buƙatata har tsawon wani lokaci bayan mun cimma matsayarmu, amma tabbas ko ba yanzu ba akwai ranar da Ya za ta ɗakin ƙanwa, lokaci na tafe zan aiwatar da abin da yake ci mini tuwo a ƙwarya. Ni ma lokaci ya dawo mini da zan karɓo sihirtacciyar sandar mahaifiyata Bokanya Shirzan, a lokacin ne duk wani cikar ikona zai dawo." Tana rufe baki suka fara ƙyaƙyata wata irin dariya mara daɗin sauraron mai ɗauke da amsa kuwwar kukan jakuna, suna tsaka da kuka sai ga wani matashin saurayi ya diro cikin ɗakin hannunsa ɗauke wani jariri sabuwar haihuwa. Jaririn sai mutsu-mutsu yake ko jikinsa ba a gyara ba balle a yanke cibiyarsa, a kan tafin hannun wani gunkin tsoho da ke tsaye ya wara hannuwansa. Yana ɗora jaririn a kai nan take wannan Hatsabibiya da ke ɗauke da siffar tsuntsu ta taso ta dira a kan cikin jaririn. Wata ƙara ya ƙwalla saboda wata irin azaba da ke ratsa sassan jikinsa, da ƙafafuwansa tsuntsun ya huda ƙirjin jaririn ya kafa kai yana tsotsar jinin jaririn. Kafin wani lokaci tuni idanun jaririn sun ƙafe jikinsa ya saki numfashinsa ya ɗauke, tana ganin haka ta tashi daga kanta sai Intisar ta ƙarasa ta banƙare ƙirjinsa ta ciro zuciyarsa ta wurga bakinta ta cinye.
Ɗaukan gawar jaririn ta yi ta miƙawa sauran mutanen wurin, da sauri suka caɓe shi suka buɗe wani ƙaramin ɗaki mai ja da baƙin labule suka wurga ciki.
Raihan na zuwa gida a hankali ta fara zaga bangon da ke cikin ɗakunansu, ga mamakinta tana bi ta cikin ɗakinta ta hangi mai siffarta kwance a kan makwancinta a gefe ɗaya ga Mama Uwani tana zaune tana gadinta. Amma ga mamakinta sai gani ta yi ta gifta ta gabanta ba tare da ta lura da ita ba. Hasalima ratsawa take yi ta ko'ina ba tare da gini ko ƙofa sun yi mata shamaki ba, a hankali ta ci gaba da tafiya kamar mai tafiya a sararin samaniya har ta dira a ɗakin Mahaifiyarta sai da ta ƙare mata kallo sannan ta wuce ɗakin da Mama Hasiya take kwance tana bacci. Kamar yadda Hatsabibiya ta umarceta haka ta tsaya a saitin kanta, ƙashin hannunta ta kai saitin fuskar Mama Hasiya lokaci ɗaya ta buɗe idonta firgigit ta sauke su a kan Raihan, sai dai a cikin idanunta gani ta yi Raihan ta siffanta da wata mummunar hallita, cikin rashin tausayi Raihan ta ƙarasa gabanta ta damƙo maƙogaronta, nan take Mama Hasiya ta fara kakari idanunta suka firfito waje.
Da murya mai wahalarwa Mama Hasiya ta fara karanta kalmar shahada, tana yi tana ambaton sunan Maigidanta da duk sunan wanda ya zo bakinta.
Ana cikin haka wasu tafka-tafkan kunamu suka fara ratsowa ta jikin bango girman kowacce ɗaya ya fi girman kan jariri, da gudu suka fara rarrafowa suka haye gadon sun kai kusan goma suka maƙale a jikin Mama Hatsiya kowacce ta kafa bakinta suka fara zuƙar jini.
Cikin tsananin azaba Mama Hasiya ta fara wani irin ƙaraji da gurnani, tun tana cikin hayyacinta har ta fara fita daga haka idanunta suka kafe rai ya yi halinsa. Raihan na ganin haka ta saki wuyan gawar Mama Hasiya ta faɗa kan gado yaraf ta ja mayafi ta rufeta sannan ta miƙawa kunamin nan hannu lokaci ɗaya suka maƙaleta, ta ɗago da su saitin fuskarta. Haƙoranta ne suka fara girma ga wata fiƙa irin ta karnuka da ta fito mata, bakinta ya fara zubda wani baƙin jini mai yauƙi. Ƙwayar idanunta zazzago suna wani irin juyi, a hankali ta fara takawa ta fice daga ɗakin ta koma ta sashen ɗakin Mahaifiyarta, ta jima a bakin window sai da ta yi ƙwafa sannan ta ratsa ta jikin bango ta fice daga gidan.
Bayan sun wurga Jaririn cikin wannan ɗakin wata irin tsawa aka yi mai haɗe da walƙiya, a hankali hatsabibiya ta shiga ɗakin tuni wata mummunar hallita mai ɗauke da kawuna har guda goma a jikinta, a kowanne baki akwai aikin da yake aiwatarwa. A ɗaya daga cikin kan mummunar hallitar ta cafke jaririn tana laƙumewa, wani kan kuma ya fara amayo da kuɗaɗe kala-kala har da na ƙasashen waje, ya yin da wani kan ya fara tatsar da wani ruwa mai yauƙi yana zuba watsu ƙananan ƙwari suna zuwa suna tsotsa.
Suna nan tsaya Raihan ta diro cikin gidan, hannuwanta biyu saƙale da kunamu tana tafe cikin takun ƙasaita dauke mummunar hallita. Tana zuwa Hatsabibiya ta fito fuskarta ɗauke da murmushi, shigar Raihan wurin ya sa jikin wannan dattijon ya fara ɓamɓarowa daskararran jikinsa ya fara rozayewa a hankali har ya rozaye gabaɗaya. Wata irin girgiza ya yi nan take ya fara kallon mutanen wurin ɗaya bayan ɗaya, Hatsabibiya ta tako a hankali fuskarta ɗauke da annuri ta ce, "Barka da dawowa cikin rayuwarka ta ainihini Ya masoyina." Hannuwanta ya riƙo yana bin ta da kallo lokaci ɗaya ya rungume ta yana shafa bayanta sannan ya ce, "Ina godiya da sadaukarwarki, amma ya aka yi kika samu tsarkakken jini alhalin an ce sai ta silar Muraza shin kun samota ne?" Hannunsa ta ja bakin wata tsohuwar rijiya da ke cikin ɗakin tana faɗin, "Mu je turaka zan baka labari." Tana rufe baki suka faɗa cikin rijiyar shigewarsu keda wuya wurin ya shafe tamkar ba a taɓa hallitar wani abu a wurin ba.
Wani tutturnan mutum da suke kira da Mataimaki shi ya ƙarasa wurin Raihan ya karɓi kunamin hannunta, ya zuba su a cikin wani ƙoƙon kai sannan ya dubi Raihan ya ce, "An gaishe ki Jaruma, Shugaba mai cikakken iko sai ke gagabadau. Za ki iya tafiya sai ranar taro na gaba amma a ranar muna buƙatar tukwicin sabuwar gawar mace mai ƙarancin shekaru kar su yi ƙasa da talati kar kuma ta haura shekara arba'in." Raihan ban da jinjina kai babu abin da take yi, tana gama sauraronsa ta dubi Intisar alamar su tafi. Intisar ta nuna mata wata ƙoriyar ƙwarya mai cike da wani ruwa mai ɗauke da launin jini kamar anwanke nama, sannan ta ce: "Ki kuskure bakinki da ruwan tsarki domin samun albarka." Ba musu Raihan ta ƙarasa ta ɗauki ƙwaryar ta kafa kanta, tana kafa kai ta ji kanta ya sake yin nauyi dumm! A hankali ta iya kai ƙwaryar bakinta ta kuskure wata irin kasala ta mamaye jikinta, ga wani irin addababban bacci da ya lulluɓe idanunta. Tana ajiye ƙwaryar ta tafi luuuu za ta faɗi da sauri Intisar ta taro ta jikinta, sannan ta saɓa ta a kafaɗa ta fice daga cikin kogon dutsen kai tsaye ta wuce gidan su Raihan.
Intisar bata tsaya a ko'ina ba sai a tsakiyar ɗakin Raihan, tana kallon Mama Uwani ta saki wani malalacin murmushi. Kwantar da Raihan ta yi sannan ta fara zagaye ɗakin ba tare da idanun Mama Uwani sun gane mata Intisar ba, lokaci ɗaya ta saki wata mahaukaciyar dariya. Tun tana dariya a tsaye har ta durƙushe a wurin sannan ta ratse ta ƙarƙashin ƙasa ta fice daga ɗakin.
WASHEGARI
Ɗaukan gawar jaririn ta yi ta miƙawa sauran mutanen wurin, da sauri suka caɓe shi suka buɗe wani ƙaramin ɗaki mai ja da baƙin labule suka wurga ciki.
Raihan na zuwa gida a hankali ta fara zaga bangon da ke cikin ɗakunansu, ga mamakinta tana bi ta cikin ɗakinta ta hangi mai siffarta kwance a kan makwancinta a gefe ɗaya ga Mama Uwani tana zaune tana gadinta. Amma ga mamakinta sai gani ta yi ta gifta ta gabanta ba tare da ta lura da ita ba. Hasalima ratsawa take yi ta ko'ina ba tare da gini ko ƙofa sun yi mata shamaki ba, a hankali ta ci gaba da tafiya kamar mai tafiya a sararin samaniya har ta dira a ɗakin Mahaifiyarta sai da ta ƙare mata kallo sannan ta wuce ɗakin da Mama Hasiya take kwance tana bacci. Kamar yadda Hatsabibiya ta umarceta haka ta tsaya a saitin kanta, ƙashin hannunta ta kai saitin fuskar Mama Hasiya lokaci ɗaya ta buɗe idonta firgigit ta sauke su a kan Raihan, sai dai a cikin idanunta gani ta yi Raihan ta siffanta da wata mummunar hallita, cikin rashin tausayi Raihan ta ƙarasa gabanta ta damƙo maƙogaronta, nan take Mama Hasiya ta fara kakari idanunta suka firfito waje.
Da murya mai wahalarwa Mama Hasiya ta fara karanta kalmar shahada, tana yi tana ambaton sunan Maigidanta da duk sunan wanda ya zo bakinta.
Ana cikin haka wasu tafka-tafkan kunamu suka fara ratsowa ta jikin bango girman kowacce ɗaya ya fi girman kan jariri, da gudu suka fara rarrafowa suka haye gadon sun kai kusan goma suka maƙale a jikin Mama Hatsiya kowacce ta kafa bakinta suka fara zuƙar jini.
Cikin tsananin azaba Mama Hasiya ta fara wani irin ƙaraji da gurnani, tun tana cikin hayyacinta har ta fara fita daga haka idanunta suka kafe rai ya yi halinsa. Raihan na ganin haka ta saki wuyan gawar Mama Hasiya ta faɗa kan gado yaraf ta ja mayafi ta rufeta sannan ta miƙawa kunamin nan hannu lokaci ɗaya suka maƙaleta, ta ɗago da su saitin fuskarta. Haƙoranta ne suka fara girma ga wata fiƙa irin ta karnuka da ta fito mata, bakinta ya fara zubda wani baƙin jini mai yauƙi. Ƙwayar idanunta zazzago suna wani irin juyi, a hankali ta fara takawa ta fice daga ɗakin ta koma ta sashen ɗakin Mahaifiyarta, ta jima a bakin window sai da ta yi ƙwafa sannan ta ratsa ta jikin bango ta fice daga gidan.
Bayan sun wurga Jaririn cikin wannan ɗakin wata irin tsawa aka yi mai haɗe da walƙiya, a hankali hatsabibiya ta shiga ɗakin tuni wata mummunar hallita mai ɗauke da kawuna har guda goma a jikinta, a kowanne baki akwai aikin da yake aiwatarwa. A ɗaya daga cikin kan mummunar hallitar ta cafke jaririn tana laƙumewa, wani kan kuma ya fara amayo da kuɗaɗe kala-kala har da na ƙasashen waje, ya yin da wani kan ya fara tatsar da wani ruwa mai yauƙi yana zuba watsu ƙananan ƙwari suna zuwa suna tsotsa.
Suna nan tsaya Raihan ta diro cikin gidan, hannuwanta biyu saƙale da kunamu tana tafe cikin takun ƙasaita dauke mummunar hallita. Tana zuwa Hatsabibiya ta fito fuskarta ɗauke da murmushi, shigar Raihan wurin ya sa jikin wannan dattijon ya fara ɓamɓarowa daskararran jikinsa ya fara rozayewa a hankali har ya rozaye gabaɗaya. Wata irin girgiza ya yi nan take ya fara kallon mutanen wurin ɗaya bayan ɗaya, Hatsabibiya ta tako a hankali fuskarta ɗauke da annuri ta ce, "Barka da dawowa cikin rayuwarka ta ainihini Ya masoyina." Hannuwanta ya riƙo yana bin ta da kallo lokaci ɗaya ya rungume ta yana shafa bayanta sannan ya ce, "Ina godiya da sadaukarwarki, amma ya aka yi kika samu tsarkakken jini alhalin an ce sai ta silar Muraza shin kun samota ne?" Hannunsa ta ja bakin wata tsohuwar rijiya da ke cikin ɗakin tana faɗin, "Mu je turaka zan baka labari." Tana rufe baki suka faɗa cikin rijiyar shigewarsu keda wuya wurin ya shafe tamkar ba a taɓa hallitar wani abu a wurin ba.
Wani tutturnan mutum da suke kira da Mataimaki shi ya ƙarasa wurin Raihan ya karɓi kunamin hannunta, ya zuba su a cikin wani ƙoƙon kai sannan ya dubi Raihan ya ce, "An gaishe ki Jaruma, Shugaba mai cikakken iko sai ke gagabadau. Za ki iya tafiya sai ranar taro na gaba amma a ranar muna buƙatar tukwicin sabuwar gawar mace mai ƙarancin shekaru kar su yi ƙasa da talati kar kuma ta haura shekara arba'in." Raihan ban da jinjina kai babu abin da take yi, tana gama sauraronsa ta dubi Intisar alamar su tafi. Intisar ta nuna mata wata ƙoriyar ƙwarya mai cike da wani ruwa mai ɗauke da launin jini kamar anwanke nama, sannan ta ce: "Ki kuskure bakinki da ruwan tsarki domin samun albarka." Ba musu Raihan ta ƙarasa ta ɗauki ƙwaryar ta kafa kanta, tana kafa kai ta ji kanta ya sake yin nauyi dumm! A hankali ta iya kai ƙwaryar bakinta ta kuskure wata irin kasala ta mamaye jikinta, ga wani irin addababban bacci da ya lulluɓe idanunta. Tana ajiye ƙwaryar ta tafi luuuu za ta faɗi da sauri Intisar ta taro ta jikinta, sannan ta saɓa ta a kafaɗa ta fice daga cikin kogon dutsen kai tsaye ta wuce gidan su Raihan.
Intisar bata tsaya a ko'ina ba sai a tsakiyar ɗakin Raihan, tana kallon Mama Uwani ta saki wani malalacin murmushi. Kwantar da Raihan ta yi sannan ta fara zagaye ɗakin ba tare da idanun Mama Uwani sun gane mata Intisar ba, lokaci ɗaya ta saki wata mahaukaciyar dariya. Tun tana dariya a tsaye har ta durƙushe a wurin sannan ta ratse ta ƙarƙashin ƙasa ta fice daga ɗakin.
WASHEGARI