Sashe 45
Alaƙar Zuci Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wurin karfe tara sai ga manyan raguna a gyare aka kawo min guda biyu, mu babu abinda muka yi a gidan domin an bada aikin abincin sunan ne, namar ne aka dauko wani mahauci ya gyara aka dauki daya aka saka min a firji daya kuma aka shiga aikinsa.
Wurin sha daya da rabi mai kwalliya da Jasminah suka iso, ta zo ta min make-up bayan ta gama bata tafi ba domin aikin wannan ranar ya biya baki
aya, sai da na shirya cikin wata lace me laushi, na fito sai gashi tare da su Aunty Mom da Granny, wayyo Allah tun anan ta fara kiran yarinyar Annah, wani irin kauna take yiwa yarinyar mara iyaka, ni dai ban san me zancewa Ubangiji ba, hoto muka yi sosai, karfe biyu aka sake min kwalliya muka wuce family house
insu, haka ya ce min na shirya mu tafi, sai da na je muka fahimci ashe anan ake bikin sunan domin an cika wai baki har daga Ethiopia, ban da na Gombe.
Hajiya Zeenatu ta gaya min magana da sai da na kusan kuka amma nayi yake, domin cewa tayi.
"Duk wannan hidimar akan y'a mace, ni na zata da ake boye cikin saboda d'a namiji za a ahaife ashe duk mu ne." Ban ce mata kome ba, domin idan nayi magaja nawa sai yayi zafi.
Bayan tafiyarta sai ga ta tare da wasu mata kamar yan boko irin Lagos Alaja din nan, suka zo yarbanci ta juya musu suka yi ta yin wasu abubuwan da ya sa na ce mata.
"Hajiya hala baki da tarihin jahar da na fito ko?
Ni yar jahar Bauchi ce, ina kuma alfahari da cewa ni namar kai ce ga kitse ga tauri, idan kika sake na saka ki a corner." Wani devilishly smile na mata, ina kallon cikin kwayar idanunta.
"Kada ki saka na kai ki inda ba zaki ji dadi ba." Ina fadar haka ta bala'in shiga hankalinta, fita suka yi ita da kawayenta.
Haka Yarta Mimi suka shigo kamar wani abin arziki, ta dauki Yarinyar sai da ta gama kallon yarinyar ta ce min.
"Anya wannan jinin KUMO ce kuwa ban ga tayi kalar fatar Kumo Family ba."
"Ba mamaki an saba number ta yadda kika kasance daban a cikin kumo family, domin duk kumo muna da manyan idanun naki kuwa kamar ta kwad'i." Inji Jasminah tana kallon Mimi, sai tayi shiru, tana kallon yarta.
"Yes kalle ni da kyau duk wani jinin kumo yana da dogon hanci dogon gashi, kai everything yaran kumo suna da shi hatta Bo
o da aka haifa jiya kalli gashi har yatsun hannunta sun nuna zata yi gashi, amma ke kuma ko goruba ys sallama miki rashin gashi, shima hasken fata baki ga lura cewa mai kike ta labtawa akanki ba." Duk Jarabar son ayi fada Jasminah ta sani, sai da ta kunyata yarinyar nan ta fita kuka, atow ka fada ne tsakani me baki mara kunya, haka ta fita daga parlourn, ni dai na zuba idanun ai kuwa can sai ga Hajiya Zeenatu ta shigo tana huci, kallonta Jasminah tayi irin kallon nan ne mara da
i, zata yi magana na rike hannunta.
Girgiza mata kai nayi ina murmushi, haka uwar ta gama zage-zage ta sannan ta fita a parlourn, abin bai yi dad'i ba domin Hajiya Khaulatu ta je ta ci mata mutunci wanda ya janyo katon tashin hankali a cikin gidan kamar zasu yi doke doke, dakyar aka gama lafiya Kannen Babanshi sun zo sun bani hakuri ni a lissafina kamar zasu kara biyo min ta baya ne, har muka dawo gida maganar ake nanatawa sai da Yadiko ta musu fada suka yi shiru, ashe wannan zuwan yadiko zama zata yi Umma zata koma Bauchi wai mijinta yana ta sintiri, duk sai naji ba dad'i.
Haka na tura mishi sako, aikuwa washi gari sai gashi da akwati ya shigo da shi suka gaisa, da yake kayan da aka mana na sunar basu kawo ba, kome ayin parkage dinsa ne, haka ya kawo mata ya saka dubu dari biyu a kai, tare da da godiya, dukkaninsu da suka zo sunan sai da aka musu shatara na arziki, suna da kwana biyu suka bar Lagos, a ranar kuma aka kawo kayan Yadiko tayi ta saka albarka.
Yanzu nasan ina wanka wato Yadiko sosai take wanke ni, Umma ai ni nake yi da kaina, Yadiko kuwa haka ta saka shi nimo mata ganyen lim, tayi ta zane ni da shi da sunan tana min wanka, ai sai da naji kamar zan yi hauka domin wankan ya saka ni jin wani irin tsoro da damuwa, sati uku nayi wani irin kwari sai yanzu na fahimci wankar tana gyara min lafiyata, domin kuwa idan nayi barci sosai, yarinyar ma idan ta sha ruwan zafi tuni take barci sai dai kukan dare da rikici.
Shima Yadiko take nuna min yadda zan yi, shima ganin Yadiko bata bada fuska sai ya kame kanshi ya daina nimana, abinci idan muka gama da ita xan jera zan koma daki yana dawowa zan zo na gaishe shi.
Bayan nan zan koma daki shima haka ta ce min, sauran kuma yayi da kanshi.
Sakon kewar da yayi, wani abun da yadiko take kara burge ni da shi da ta fito kiri ta gaya mishi gaskiya tare da cewa idan aka gama wankar da kanshi zai fahimci dalilin haka.
Sai bai kara nuna takura da yake ciki ba, haka muka cika wata guda, ranar Jasminah suka zo mana wuni ita da wata yarinya baka kyakyawa da ita anan take gaya min budurwa Taj ce, yarinyar ita ta yi mana abinci, da dare suka tafi gida, ya rage saura kwanaki goma yadiko ta sauke mana wanka.
Haka yayi ta sayayya yana kawowa gidan, idan na tambaye shi dalilin haka sai ya ce ina ruwana ranar da na mishi magana ban gane me yake nufi ba, budar bakinsa ya ce min..
"aure zanyi ko akwai matsala ne?" Daga ranar ban kara mishi magana ba, ana saura kwanaki uku ta ce min.
"Kina takure ko?" A kunyace na ce mata.
"A'a Yadiko!" Murmushi tayi ta ce min.
"Ki kula da kanki da Yarki, idan kin gama wanka jini ya dawo, ki kula da kwanakin kyankyasan kwanki, domin zaki kuma ciki.
Ki kula da kanki da Yarki don kin ga tana da lafiya da kuzari don Allah kada ki dauko wani cikin saboda wannan rawan kan da kuke da shi zaku iya samun wani cikin nan kusa wallahi." Ni dai ban kara magana ba, kuma ban kara motsi ko wani abu ba, sai dai na kara fahimtar cewa shi fa kome na rayuwa yana tsarin Ubangiji, ranar da muka cika kwanaki arba'in, muka ajiye wanka, sannan shi da kansa ya ce mata.
"Yadiko ki yi hakuri wata sati sai ki tayi don Allah!" Bata so ba, amma haka ta hakura.
Tafiya ce ta kama shi har na tsawon kwanaki biyar, a wannan lokacin yadiko ta shiga hada min wani hadin gyaran jiki da kanta ta shiga kasuwa tare da rakiyar Aunty Munah da tazo min, kamar nayi kuka haka tayi ta ha
a min magani har da tsumi tare da maganin sanyi ta hada min na fara sha, sai nayi ta fitsari na tsawon kwanaki uku, kafin ta bani gumba da zuma na cigaba sha, ranar da ya dawo tare da ita muka sha aiki da Aunty Munah, yana dawowa ya shigo suka gaisa, a daren ashe ta kira Ya Ado ya zo ya dauke su, sai gashi nan kuwa ya zo suka tafi sai da nayi kuka don takaici, shima bai san sun tafi ba, fitowa yayi ya ga ina kuka.
"Lafiya?" "Sun tafi mana!" Shiru yayi kafin ya ce min.
"Sorry zan bisu kin ji!" Gyada kai nayi ya wuce wurin da na ajiye yar ya dauke ta, yana fa
in.
"I miss you Mommy." "Nifa!" "Allah ya baki hakuri duk nayi miss dinku." Ya rungume ni yana murmushi.
Sai da naji ina ma rayuwarmu ya tsaya haka kada wani ya shiga cikin rayuwarmu, kada wani ya hana mu farin ciki.
"Muje kaci abinci, sai ta tafi sallah isha." "Bani tea na sha sai na fita, idan naci ba zan mori kaina ba!." Haka kuwa aka yi na wuce na cigaba da hada mishi, sannan nan kawo mishi na zauna ina kallonshi, ya sha yana kallon yarshi.
Yana gamawa ya ajiye ya nufi masallaci, nima nayi a gidan bayan na idar, na kara gyara jikina na sha zuma na, na gyara jikina da turare.
Dakinsa na wuce na gyara dakin kayan da ya dawo da shi, na shiga cirewa.
A hankali na gama sai dai me lipstick na samu ban tab'a ba.
Na mai da kome wurin zamanshi da zan wuce na ga wayarshi tayi haske.
Ban yi niyyar dubawa ba, na hango sunan Adaa.
Komawa nayi na shiga duba wayar ya saka mata security code yaushe ya fara saka security code a wayarshi?
Abin sai ya bani mamaki nayi ta kallon wayar hoton yarshi ce a kai, nayi kasa da kaina ina mamaki.
Kafin na sare ban kara magana ba, na ajiye na fita.
Har ya dawo ya ci abinci, muna ta hira sama-sama.
Tashi yayi ya shiga cikin dakin, bai fito ba nima kuma ban yi wani yunkurin zuwa dakin ba, na wuce zuwa dakina na gyarawa Yarinyata wurin kwanciya, na kwanta barci ya dauke ni.
Har zuwa sha biyu ko zai zo wallahi ban Ganshi ba, karshe na tashi na rufe kofar na kwanta ina kuka, sai wurin karfe daya da yaji kukan yarinyar ya zo yana buga kofar ban bude ba, haka ya gama buga kofar ya hakura.
Washi gari tun asuban fari na mata wanka na bata nono, na fita na hada kome na ajiye mishi nasan ba zai fita ba, amma sai na zabi shiru na zuba mishi idanun, wurin karfe goma na safe ina barci ya shigo dakin, ganin ko ina tsaf-tsaf sai ya sauke ajiyar zuciya sannan ya kwanta a baya, duminsa ne yasa na juya ina kallonshi.
Ban wani damu ba amma zai san ya tab'a har mutanen Bauchi.
Wurin sha daya da rabi mai kwalliya da Jasminah suka iso, ta zo ta min make-up bayan ta gama bata tafi ba domin aikin wannan ranar ya biya baki
aya, sai da na shirya cikin wata lace me laushi, na fito sai gashi tare da su Aunty Mom da Granny, wayyo Allah tun anan ta fara kiran yarinyar Annah, wani irin kauna take yiwa yarinyar mara iyaka, ni dai ban san me zancewa Ubangiji ba, hoto muka yi sosai, karfe biyu aka sake min kwalliya muka wuce family house
insu, haka ya ce min na shirya mu tafi, sai da na je muka fahimci ashe anan ake bikin sunan domin an cika wai baki har daga Ethiopia, ban da na Gombe.
Hajiya Zeenatu ta gaya min magana da sai da na kusan kuka amma nayi yake, domin cewa tayi.
"Duk wannan hidimar akan y'a mace, ni na zata da ake boye cikin saboda d'a namiji za a ahaife ashe duk mu ne." Ban ce mata kome ba, domin idan nayi magaja nawa sai yayi zafi.
Bayan tafiyarta sai ga ta tare da wasu mata kamar yan boko irin Lagos Alaja din nan, suka zo yarbanci ta juya musu suka yi ta yin wasu abubuwan da ya sa na ce mata.
"Hajiya hala baki da tarihin jahar da na fito ko?
Ni yar jahar Bauchi ce, ina kuma alfahari da cewa ni namar kai ce ga kitse ga tauri, idan kika sake na saka ki a corner." Wani devilishly smile na mata, ina kallon cikin kwayar idanunta.
"Kada ki saka na kai ki inda ba zaki ji dadi ba." Ina fadar haka ta bala'in shiga hankalinta, fita suka yi ita da kawayenta.
Haka Yarta Mimi suka shigo kamar wani abin arziki, ta dauki Yarinyar sai da ta gama kallon yarinyar ta ce min.
"Anya wannan jinin KUMO ce kuwa ban ga tayi kalar fatar Kumo Family ba."
"Ba mamaki an saba number ta yadda kika kasance daban a cikin kumo family, domin duk kumo muna da manyan idanun naki kuwa kamar ta kwad'i." Inji Jasminah tana kallon Mimi, sai tayi shiru, tana kallon yarta.
"Yes kalle ni da kyau duk wani jinin kumo yana da dogon hanci dogon gashi, kai everything yaran kumo suna da shi hatta Bo
o da aka haifa jiya kalli gashi har yatsun hannunta sun nuna zata yi gashi, amma ke kuma ko goruba ys sallama miki rashin gashi, shima hasken fata baki ga lura cewa mai kike ta labtawa akanki ba." Duk Jarabar son ayi fada Jasminah ta sani, sai da ta kunyata yarinyar nan ta fita kuka, atow ka fada ne tsakani me baki mara kunya, haka ta fita daga parlourn, ni dai na zuba idanun ai kuwa can sai ga Hajiya Zeenatu ta shigo tana huci, kallonta Jasminah tayi irin kallon nan ne mara da
i, zata yi magana na rike hannunta.
Girgiza mata kai nayi ina murmushi, haka uwar ta gama zage-zage ta sannan ta fita a parlourn, abin bai yi dad'i ba domin Hajiya Khaulatu ta je ta ci mata mutunci wanda ya janyo katon tashin hankali a cikin gidan kamar zasu yi doke doke, dakyar aka gama lafiya Kannen Babanshi sun zo sun bani hakuri ni a lissafina kamar zasu kara biyo min ta baya ne, har muka dawo gida maganar ake nanatawa sai da Yadiko ta musu fada suka yi shiru, ashe wannan zuwan yadiko zama zata yi Umma zata koma Bauchi wai mijinta yana ta sintiri, duk sai naji ba dad'i.
Haka na tura mishi sako, aikuwa washi gari sai gashi da akwati ya shigo da shi suka gaisa, da yake kayan da aka mana na sunar basu kawo ba, kome ayin parkage dinsa ne, haka ya kawo mata ya saka dubu dari biyu a kai, tare da da godiya, dukkaninsu da suka zo sunan sai da aka musu shatara na arziki, suna da kwana biyu suka bar Lagos, a ranar kuma aka kawo kayan Yadiko tayi ta saka albarka.
Yanzu nasan ina wanka wato Yadiko sosai take wanke ni, Umma ai ni nake yi da kaina, Yadiko kuwa haka ta saka shi nimo mata ganyen lim, tayi ta zane ni da shi da sunan tana min wanka, ai sai da naji kamar zan yi hauka domin wankan ya saka ni jin wani irin tsoro da damuwa, sati uku nayi wani irin kwari sai yanzu na fahimci wankar tana gyara min lafiyata, domin kuwa idan nayi barci sosai, yarinyar ma idan ta sha ruwan zafi tuni take barci sai dai kukan dare da rikici.
Shima Yadiko take nuna min yadda zan yi, shima ganin Yadiko bata bada fuska sai ya kame kanshi ya daina nimana, abinci idan muka gama da ita xan jera zan koma daki yana dawowa zan zo na gaishe shi.
Bayan nan zan koma daki shima haka ta ce min, sauran kuma yayi da kanshi.
Sakon kewar da yayi, wani abun da yadiko take kara burge ni da shi da ta fito kiri ta gaya mishi gaskiya tare da cewa idan aka gama wankar da kanshi zai fahimci dalilin haka.
Sai bai kara nuna takura da yake ciki ba, haka muka cika wata guda, ranar Jasminah suka zo mana wuni ita da wata yarinya baka kyakyawa da ita anan take gaya min budurwa Taj ce, yarinyar ita ta yi mana abinci, da dare suka tafi gida, ya rage saura kwanaki goma yadiko ta sauke mana wanka.
Haka yayi ta sayayya yana kawowa gidan, idan na tambaye shi dalilin haka sai ya ce ina ruwana ranar da na mishi magana ban gane me yake nufi ba, budar bakinsa ya ce min..
"aure zanyi ko akwai matsala ne?" Daga ranar ban kara mishi magana ba, ana saura kwanaki uku ta ce min.
"Kina takure ko?" A kunyace na ce mata.
"A'a Yadiko!" Murmushi tayi ta ce min.
"Ki kula da kanki da Yarki, idan kin gama wanka jini ya dawo, ki kula da kwanakin kyankyasan kwanki, domin zaki kuma ciki.
Ki kula da kanki da Yarki don kin ga tana da lafiya da kuzari don Allah kada ki dauko wani cikin saboda wannan rawan kan da kuke da shi zaku iya samun wani cikin nan kusa wallahi." Ni dai ban kara magana ba, kuma ban kara motsi ko wani abu ba, sai dai na kara fahimtar cewa shi fa kome na rayuwa yana tsarin Ubangiji, ranar da muka cika kwanaki arba'in, muka ajiye wanka, sannan shi da kansa ya ce mata.
"Yadiko ki yi hakuri wata sati sai ki tayi don Allah!" Bata so ba, amma haka ta hakura.
Tafiya ce ta kama shi har na tsawon kwanaki biyar, a wannan lokacin yadiko ta shiga hada min wani hadin gyaran jiki da kanta ta shiga kasuwa tare da rakiyar Aunty Munah da tazo min, kamar nayi kuka haka tayi ta ha
a min magani har da tsumi tare da maganin sanyi ta hada min na fara sha, sai nayi ta fitsari na tsawon kwanaki uku, kafin ta bani gumba da zuma na cigaba sha, ranar da ya dawo tare da ita muka sha aiki da Aunty Munah, yana dawowa ya shigo suka gaisa, a daren ashe ta kira Ya Ado ya zo ya dauke su, sai gashi nan kuwa ya zo suka tafi sai da nayi kuka don takaici, shima bai san sun tafi ba, fitowa yayi ya ga ina kuka.
"Lafiya?" "Sun tafi mana!" Shiru yayi kafin ya ce min.
"Sorry zan bisu kin ji!" Gyada kai nayi ya wuce wurin da na ajiye yar ya dauke ta, yana fa
in.
"I miss you Mommy." "Nifa!" "Allah ya baki hakuri duk nayi miss dinku." Ya rungume ni yana murmushi.
Sai da naji ina ma rayuwarmu ya tsaya haka kada wani ya shiga cikin rayuwarmu, kada wani ya hana mu farin ciki.
"Muje kaci abinci, sai ta tafi sallah isha." "Bani tea na sha sai na fita, idan naci ba zan mori kaina ba!." Haka kuwa aka yi na wuce na cigaba da hada mishi, sannan nan kawo mishi na zauna ina kallonshi, ya sha yana kallon yarshi.
Yana gamawa ya ajiye ya nufi masallaci, nima nayi a gidan bayan na idar, na kara gyara jikina na sha zuma na, na gyara jikina da turare.
Dakinsa na wuce na gyara dakin kayan da ya dawo da shi, na shiga cirewa.
A hankali na gama sai dai me lipstick na samu ban tab'a ba.
Na mai da kome wurin zamanshi da zan wuce na ga wayarshi tayi haske.
Ban yi niyyar dubawa ba, na hango sunan Adaa.
Komawa nayi na shiga duba wayar ya saka mata security code yaushe ya fara saka security code a wayarshi?
Abin sai ya bani mamaki nayi ta kallon wayar hoton yarshi ce a kai, nayi kasa da kaina ina mamaki.
Kafin na sare ban kara magana ba, na ajiye na fita.
Har ya dawo ya ci abinci, muna ta hira sama-sama.
Tashi yayi ya shiga cikin dakin, bai fito ba nima kuma ban yi wani yunkurin zuwa dakin ba, na wuce zuwa dakina na gyarawa Yarinyata wurin kwanciya, na kwanta barci ya dauke ni.
Har zuwa sha biyu ko zai zo wallahi ban Ganshi ba, karshe na tashi na rufe kofar na kwanta ina kuka, sai wurin karfe daya da yaji kukan yarinyar ya zo yana buga kofar ban bude ba, haka ya gama buga kofar ya hakura.
Washi gari tun asuban fari na mata wanka na bata nono, na fita na hada kome na ajiye mishi nasan ba zai fita ba, amma sai na zabi shiru na zuba mishi idanun, wurin karfe goma na safe ina barci ya shigo dakin, ganin ko ina tsaf-tsaf sai ya sauke ajiyar zuciya sannan ya kwanta a baya, duminsa ne yasa na juya ina kallonshi.
Ban wani damu ba amma zai san ya tab'a har mutanen Bauchi.