Sashe 85
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Murmushi yayi ya dafa kafadunsa da hannayensa biyu yace “Aboulkhair relax, Mu’azzam din daka sani a baya bafa shine yanzu ba. Akwai improvement mai tarin yawa a lafiyarsa ta yanzu. I promised you i will be safe, kuma ga su Basma zasu debe min kewa I will not be aloneâ€.
Ya tsugunna a gabansa ya dora tafin hannunsa bisa tafin kafar kanin nasa.
“Ina neman gafarar ka, for all the inconveniences!!!â€.
Aboulkhair couldn’t keep it, banda ya rungume Mu’azzam da karfi ya saki kuka. A lokacin shima ya soma neman gafararsa, ya gaya masa yayi nadamar dawowa, da ya san abinda dawowarsa zata janyo kenan da ko kusa bai yi ta ba.
Da sauri Mu’azzam ya toshe masa baki yace “Ka isa ka kankare abinda Allah ya rubuta ne Aboulkhair? Bana son wannan maganar kar ka sake yin irin ta. Dawowar ka ta fiye min mata dari a doron duniya. Zan iya sake Aalimah amma kai bazan iya taba sake ka ba. Allah ya riga ya rubuta karshen zaman mu kenan. Wani wayo ko dabara ko dana sani bai isa ya kankare wannan kaddarar ba.
Ina mai kara gaya maka Zan iya sake Aalimah, amma kai bazan taba sake ka ba. Kai na yiwa laifi Aboulkhair dana biyewa zuciyata ta fada cikin soyayyar macen dana san ka tafi ka bari ne ba don ka daina so ba! Ka yarda dani a baya nayi duk kokarin da zan yi kada sabo ya shiga tsakanin mu, all my efforts was futile sabida nagartattun halayenta. But i trust myself now. I can manage a life without Aalimah. After all ta bani mafi darajar abinda zai debe min kewarta; ‘ya’ya har guda biyu a lokaci dayaâ€.
Yayi Murmushi mai taushi “so ka daina damuwa, ka bar ni in tafi sabida ofis da makarantar yara, insha Allah ba abinda zai faru damu sai alkhairi. Aalimah will soon come and regret her judgement ni kuma zan bata mamaki, na gama zama da ita kenan insha.....â€.
“.... Please Mu’az.....daina fadin haka, har zuwa abubuwan su lafa a zuciyar ta. Tension ne kawai ke damun ta ba wani abu ba. I’m sure da sannu zata huce, kuma komai zai koma daidai. Tunda da kanta tace ta zabi cigaba da zama da kai sabida ‘ya’yan dake tsakaninku, haka kuma sabida su ne zata huce bada jimawa ba. Alhmdulillah da ka yi amfani da hankali da tunanin ka wajen yin sakin da muslunci ke so.
Ni yanzu kallon Basma da Khaleesat nake yiwa Aalimah! Wallahi komai da ya dangance ce ta ya shafe daga kaina da zuciyata. Ni na jawo komai kuma ni zan gyara da yardar UBANGIJI, don Allah kada kayi fushi da itaâ€.
Mu’azzam ya hau girgiza kai. Ya dafa kafadar Aboulkhair, kana iya karantar kwantaccen bacin rai cikin kyawawan idanun sa. Abinda Aalimah tayi a court ya bata masa rai sosai, akalla in shi ta ki shi, to ta tuna kananan ‘ya’yan ta da za ta mayar marayun dole at a tender age. Cikin kaushin murya yace da Aboulkhair.
“For now, ka bar zancen Aalimah a tsakanin mu. Mu fuskanci muhimman abubuwan dake gaban mu, yadda zaka koma aikin ka, garin da zaka zabi zama da hijirar iyalinka. Aboulkhair dole ka baro Jeddah you don’t have a life there. You are a medical consultant not a shepherd (baka da rayuwa a can, kai likita ne mai matsayin consultatant ba makiyayi ba). Yanzu kokarin da zan yi dana koma shine na nemo takardunka dana ke ta boye dasu, na nema maka aiki a garin da ka zabi zamaâ€.
Kawai sai Aboulkhair ya fashe da kuka, ya sake rungume Mu’azzam yana mai jin Aalimah da komai nata na kara yin wani irin NESA cikin dubban kilometres daga zuciyarsa… ji yake ko ita kadai ta saura ‘ya mace a duniya daga yau ya haramtawa kansa ita, ya barwa Mu’azzam iyalinsa. Haka Allah ya rubuta musu cewa zai fara aurenta, amma uwar ‘ya’yan Mu’azzam ce. Wannan itace rubutacciyar kaddararsu. Zai yi duk kokarin da zai iya na ganin cewa ta koma gaban ‘ya’yanta.
Da gari ya yi haske bayan sun yi wanka sun shirya tare suka tafi gidan Daddy don yin sallama dashi da Mummy, bai fada musu tun jiya ba cewa yau zai koma kada su dakatar da shi, ba ya jin akwai abinda zai yarda ya hana shi tafiyar nan tareda ‘ya’yan sa a yau ba sai gobe ba, don ita ce kadai kwanciyar hankalinsa, kamar yadda Aalimah tace rabuwa dashi shine kwanciyar hankalin ta. Zai nesanta kansa da ita, nesantawa da babu ranar waiwaye don ta samu kwanciyar hankalin da ta ke hangowa.
Ya saya kwayan idanunsa cikin bakin PRADA mai duhu ainun. Shadda ce fara kal (getzner) a jikin sa dinkin tazarce. Kasancewar ba kasafai yake irin wannan dressing din ba sai ya fito kala daban a yau. Hakika kalar mamansa ‘yar asalin kasar Nigeria yau ta nuna sosai a jikin sa. Ko turare bai iya ya fesa ba sabida yadda yake sauri ya bar kasar Niger, amma kamshin sa ya riga ya kama komai nasa.
Sanda suka shigo Daddy da matan sa guda biyu da Yesmin tare da yaran Gumsu hudu Nurat da kannenta su Ikhram suna karin kumallo. Daddy ya bisu da kallo suna shigowa, wani farin cikin sake ganin su a tare ya tsirga masa. Yayi godiya ga mahaliccinsa mai yawan hikima da kyautayi ga bayin Sa. Murmushi yayi yana ja musu kujera akan dining din. Har kasa suka tsugunna suka gaida iyayensu sannan suka zauna a kujerar da Daddy yayi musu tayi aka cigaba da karin kumallon tare da su. Gumsu ta daina surutu, ta yarda yanzu babu muhallin yinsa. Sosai ta kame bakinta.
Suna gamawa Mu’azzam yake gaya musu sallama yazo musu zai wuce yanzu sabida ofis, kuma tare da su Basma zai tafi. Mummy ta zaro ido tace “ka bar min su mana Mu’azzam yaya zaka yi da kananan yara har biyu?†Babu kunya Mu’azzam yace ai babu matsala zai iya kula dasu. Tare zasu dinga fita ya saukesu makaranta ya wuce ofis, sanda yake tasowa suke tashi suma, kuma zai daukar musu dattijuwa mai raino musulma.
Mummy zata sake magana Daddy ya tare ta yace “Allah ya tsare, ya kiyaye ku, yayi muku albarkaâ€. Ya mikawa Aboulkhair mukullin motarsa yace ya kai su filin jirgi. Ya kara da duban Aboulkhair sosai wani abu ya fado masa, da sauri yace “drive with care. Fasten your belt. Da bismillah da ayatul kursiyyu kafa bakwai kafin tukin motaâ€. Aboulkhair ya amsa, tare da cewa “insha Allahuâ€.
Gumsu dakinta ta shige hawaye na zubo mata na tausayin Mu’azzam. Haushin Aalimah ya cika ta, har cewa tayi a ranta ba ita ba Aalimah insha Allahu. Tunda bata da tausayi ko kankani, kanta kawai ta sani da maslahar kanta. In bata tausayawa Mu’azzam ba, ai ta ji tausayin kananan yaranta.
Gidan Malam Razee suka koma, shine yaso batawa Mu’azzam lokaci don cewa yayi sam bai yarda ya tafi ba, ya zauna har Aalimah ta huce a maida aurensu su koma tare. Abinda Mu’azzam bai taba yi masa ba yau yayi masa wato gardama. Nan ya gane da gaske yake tafiyar yake so kuma ya yi fushi da Aalimah fushi mai tsanani. Aboulkhair shi ya ciwo kan Kakan nasu da kyar ya hakura ya yarjewa Mu’azzam tafiyar. Don ya gaya masa (a matsayin sa na likita) Mu’azzam is okay. He can handle himself.
Aalimah bata jima da tashi daga barci ba suna karyawa da yaranta a falon Inna Bintou ta tsinkayi sallamar Mu’azzam a tsakar kanta. Sallamar data ratsa har cikin kashi da bargon ta. Wuta ta dauke mata na lokaci mai tsawo domin sosai muryar ta ratsa cikin kunnuwa da jijiyoyinta. Su Basma suka dangwarar mata da kofin shayin ta har ya bare a jikinta, basu bi ta kanta ba suka kwasa da gudu sai wurin mahaifinsu. Rage tsaho yayi ya bude musu hannuwa suka shige ciki yana sumbatarsu daya bayan daya, ba tare da bata lokaci ba yace.
“Oya! Kowa ya dauko jakar kayansa tafiya zamuyiâ€.
Nan da nan suka hau tsalle suka runtuma daki da gudu sai ga kowanne rike da takalminsa a hannu, janye da trolley din kayansa. Basma tace “Mummy ki tashi ki dauko kayan ki†Mu’azzam yace “No Bassy, Mummy will stay at home, tana da abun yiâ€. Ya hau saka musu takalmansu. Tana zaune kamar an dasa ta tana kallon ikon Allah. Zuciyar ta na wani irin raurawa. Ya iso har gabanta ya ajiye mata passport dinta bisa cinyar ta. Ya kama hannun ‘ya’yansa yaja jakunkunan suka fice. Inna Bintou nata yi musu addu’a yana amsawa suka fice daga dakin.
Aalimah ta rasa abun da zata yi a wannan lokacin, kawai sai ta dora hannayenta biyu aka ta rushe da wani irin kakkarfan kuka, ta yaya zai zo har gabanta ya kwashe mata ‘ya’ya? Zuwa wata uwa duniyar da babu mai kula dasu???
Inna Bintou yi tayi kamar bata san da ita a dakin ba ta dau mayafi ta yafa ta fice don yiwa ‘yan biyu rakiya bakin mota.
Ya tsugunna a gabansa ya dora tafin hannunsa bisa tafin kafar kanin nasa.
“Ina neman gafarar ka, for all the inconveniences!!!â€.
Aboulkhair couldn’t keep it, banda ya rungume Mu’azzam da karfi ya saki kuka. A lokacin shima ya soma neman gafararsa, ya gaya masa yayi nadamar dawowa, da ya san abinda dawowarsa zata janyo kenan da ko kusa bai yi ta ba.
Da sauri Mu’azzam ya toshe masa baki yace “Ka isa ka kankare abinda Allah ya rubuta ne Aboulkhair? Bana son wannan maganar kar ka sake yin irin ta. Dawowar ka ta fiye min mata dari a doron duniya. Zan iya sake Aalimah amma kai bazan iya taba sake ka ba. Allah ya riga ya rubuta karshen zaman mu kenan. Wani wayo ko dabara ko dana sani bai isa ya kankare wannan kaddarar ba.
Ina mai kara gaya maka Zan iya sake Aalimah, amma kai bazan taba sake ka ba. Kai na yiwa laifi Aboulkhair dana biyewa zuciyata ta fada cikin soyayyar macen dana san ka tafi ka bari ne ba don ka daina so ba! Ka yarda dani a baya nayi duk kokarin da zan yi kada sabo ya shiga tsakanin mu, all my efforts was futile sabida nagartattun halayenta. But i trust myself now. I can manage a life without Aalimah. After all ta bani mafi darajar abinda zai debe min kewarta; ‘ya’ya har guda biyu a lokaci dayaâ€.
Yayi Murmushi mai taushi “so ka daina damuwa, ka bar ni in tafi sabida ofis da makarantar yara, insha Allah ba abinda zai faru damu sai alkhairi. Aalimah will soon come and regret her judgement ni kuma zan bata mamaki, na gama zama da ita kenan insha.....â€.
“.... Please Mu’az.....daina fadin haka, har zuwa abubuwan su lafa a zuciyar ta. Tension ne kawai ke damun ta ba wani abu ba. I’m sure da sannu zata huce, kuma komai zai koma daidai. Tunda da kanta tace ta zabi cigaba da zama da kai sabida ‘ya’yan dake tsakaninku, haka kuma sabida su ne zata huce bada jimawa ba. Alhmdulillah da ka yi amfani da hankali da tunanin ka wajen yin sakin da muslunci ke so.
Ni yanzu kallon Basma da Khaleesat nake yiwa Aalimah! Wallahi komai da ya dangance ce ta ya shafe daga kaina da zuciyata. Ni na jawo komai kuma ni zan gyara da yardar UBANGIJI, don Allah kada kayi fushi da itaâ€.
Mu’azzam ya hau girgiza kai. Ya dafa kafadar Aboulkhair, kana iya karantar kwantaccen bacin rai cikin kyawawan idanun sa. Abinda Aalimah tayi a court ya bata masa rai sosai, akalla in shi ta ki shi, to ta tuna kananan ‘ya’yan ta da za ta mayar marayun dole at a tender age. Cikin kaushin murya yace da Aboulkhair.
“For now, ka bar zancen Aalimah a tsakanin mu. Mu fuskanci muhimman abubuwan dake gaban mu, yadda zaka koma aikin ka, garin da zaka zabi zama da hijirar iyalinka. Aboulkhair dole ka baro Jeddah you don’t have a life there. You are a medical consultant not a shepherd (baka da rayuwa a can, kai likita ne mai matsayin consultatant ba makiyayi ba). Yanzu kokarin da zan yi dana koma shine na nemo takardunka dana ke ta boye dasu, na nema maka aiki a garin da ka zabi zamaâ€.
Kawai sai Aboulkhair ya fashe da kuka, ya sake rungume Mu’azzam yana mai jin Aalimah da komai nata na kara yin wani irin NESA cikin dubban kilometres daga zuciyarsa… ji yake ko ita kadai ta saura ‘ya mace a duniya daga yau ya haramtawa kansa ita, ya barwa Mu’azzam iyalinsa. Haka Allah ya rubuta musu cewa zai fara aurenta, amma uwar ‘ya’yan Mu’azzam ce. Wannan itace rubutacciyar kaddararsu. Zai yi duk kokarin da zai iya na ganin cewa ta koma gaban ‘ya’yanta.
Da gari ya yi haske bayan sun yi wanka sun shirya tare suka tafi gidan Daddy don yin sallama dashi da Mummy, bai fada musu tun jiya ba cewa yau zai koma kada su dakatar da shi, ba ya jin akwai abinda zai yarda ya hana shi tafiyar nan tareda ‘ya’yan sa a yau ba sai gobe ba, don ita ce kadai kwanciyar hankalinsa, kamar yadda Aalimah tace rabuwa dashi shine kwanciyar hankalin ta. Zai nesanta kansa da ita, nesantawa da babu ranar waiwaye don ta samu kwanciyar hankalin da ta ke hangowa.
Ya saya kwayan idanunsa cikin bakin PRADA mai duhu ainun. Shadda ce fara kal (getzner) a jikin sa dinkin tazarce. Kasancewar ba kasafai yake irin wannan dressing din ba sai ya fito kala daban a yau. Hakika kalar mamansa ‘yar asalin kasar Nigeria yau ta nuna sosai a jikin sa. Ko turare bai iya ya fesa ba sabida yadda yake sauri ya bar kasar Niger, amma kamshin sa ya riga ya kama komai nasa.
Sanda suka shigo Daddy da matan sa guda biyu da Yesmin tare da yaran Gumsu hudu Nurat da kannenta su Ikhram suna karin kumallo. Daddy ya bisu da kallo suna shigowa, wani farin cikin sake ganin su a tare ya tsirga masa. Yayi godiya ga mahaliccinsa mai yawan hikima da kyautayi ga bayin Sa. Murmushi yayi yana ja musu kujera akan dining din. Har kasa suka tsugunna suka gaida iyayensu sannan suka zauna a kujerar da Daddy yayi musu tayi aka cigaba da karin kumallon tare da su. Gumsu ta daina surutu, ta yarda yanzu babu muhallin yinsa. Sosai ta kame bakinta.
Suna gamawa Mu’azzam yake gaya musu sallama yazo musu zai wuce yanzu sabida ofis, kuma tare da su Basma zai tafi. Mummy ta zaro ido tace “ka bar min su mana Mu’azzam yaya zaka yi da kananan yara har biyu?†Babu kunya Mu’azzam yace ai babu matsala zai iya kula dasu. Tare zasu dinga fita ya saukesu makaranta ya wuce ofis, sanda yake tasowa suke tashi suma, kuma zai daukar musu dattijuwa mai raino musulma.
Mummy zata sake magana Daddy ya tare ta yace “Allah ya tsare, ya kiyaye ku, yayi muku albarkaâ€. Ya mikawa Aboulkhair mukullin motarsa yace ya kai su filin jirgi. Ya kara da duban Aboulkhair sosai wani abu ya fado masa, da sauri yace “drive with care. Fasten your belt. Da bismillah da ayatul kursiyyu kafa bakwai kafin tukin motaâ€. Aboulkhair ya amsa, tare da cewa “insha Allahuâ€.
Gumsu dakinta ta shige hawaye na zubo mata na tausayin Mu’azzam. Haushin Aalimah ya cika ta, har cewa tayi a ranta ba ita ba Aalimah insha Allahu. Tunda bata da tausayi ko kankani, kanta kawai ta sani da maslahar kanta. In bata tausayawa Mu’azzam ba, ai ta ji tausayin kananan yaranta.
Gidan Malam Razee suka koma, shine yaso batawa Mu’azzam lokaci don cewa yayi sam bai yarda ya tafi ba, ya zauna har Aalimah ta huce a maida aurensu su koma tare. Abinda Mu’azzam bai taba yi masa ba yau yayi masa wato gardama. Nan ya gane da gaske yake tafiyar yake so kuma ya yi fushi da Aalimah fushi mai tsanani. Aboulkhair shi ya ciwo kan Kakan nasu da kyar ya hakura ya yarjewa Mu’azzam tafiyar. Don ya gaya masa (a matsayin sa na likita) Mu’azzam is okay. He can handle himself.
Aalimah bata jima da tashi daga barci ba suna karyawa da yaranta a falon Inna Bintou ta tsinkayi sallamar Mu’azzam a tsakar kanta. Sallamar data ratsa har cikin kashi da bargon ta. Wuta ta dauke mata na lokaci mai tsawo domin sosai muryar ta ratsa cikin kunnuwa da jijiyoyinta. Su Basma suka dangwarar mata da kofin shayin ta har ya bare a jikinta, basu bi ta kanta ba suka kwasa da gudu sai wurin mahaifinsu. Rage tsaho yayi ya bude musu hannuwa suka shige ciki yana sumbatarsu daya bayan daya, ba tare da bata lokaci ba yace.
“Oya! Kowa ya dauko jakar kayansa tafiya zamuyiâ€.
Nan da nan suka hau tsalle suka runtuma daki da gudu sai ga kowanne rike da takalminsa a hannu, janye da trolley din kayansa. Basma tace “Mummy ki tashi ki dauko kayan ki†Mu’azzam yace “No Bassy, Mummy will stay at home, tana da abun yiâ€. Ya hau saka musu takalmansu. Tana zaune kamar an dasa ta tana kallon ikon Allah. Zuciyar ta na wani irin raurawa. Ya iso har gabanta ya ajiye mata passport dinta bisa cinyar ta. Ya kama hannun ‘ya’yansa yaja jakunkunan suka fice. Inna Bintou nata yi musu addu’a yana amsawa suka fice daga dakin.
Aalimah ta rasa abun da zata yi a wannan lokacin, kawai sai ta dora hannayenta biyu aka ta rushe da wani irin kakkarfan kuka, ta yaya zai zo har gabanta ya kwashe mata ‘ya’ya? Zuwa wata uwa duniyar da babu mai kula dasu???
Inna Bintou yi tayi kamar bata san da ita a dakin ba ta dau mayafi ta yafa ta fice don yiwa ‘yan biyu rakiya bakin mota.