Sashe 84
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Aalimah ba za ta taba mancewa da wannan ranar ba. Rana mai dumbin tarihi a gareta. Ana tafka ruwan sama har da kankara kamar da bakin kwarya. Ranar da ta zama sirrin Mu’azzam, ya zama sirrinta shima, cikin wani yanayi mai ban mamaki a gare su bakidaya.
Tun abubuwa na tafiya gentle-gentle, har komai ya kwace wa Mu’azzam. Ya zama out of his control. Tsayin daren bakidaya za ta iya cewa, ko na minti talatin Mu’azzam bai barta ta huta ba. Har ita da kanta ta gane ba ta da wayo, abin da ta je ta sa likita ya yi masa.
Washegari ko da ya je office ma bai wuce awanni uku ba sai ga shi ya dawo a wani yanayi da dole ta amsa kiransa. Ya sake komawa office ba a yi closing ba ya dawo. Tsayin kwanaki bakwai a haka suke, tana kwarara kanta, tana karfafa gangar jikinta da zuciyarta. Ga dai biyan bukata ta samu, amma kuma shi Mu’azzam din tana tausaya masa. Ta kuma gane hakan zai iya zama barazana ga aikinsa, tunda ba ya maida hankali gare shi. Ba inda yake zuwa, ya daina kulla komai, in dai yana cikin gidan to aikin kenan, ko isasshen abinci ba ya iya ci, har ramewa ya yi, ita ma ta jigata ta rame. Don haka dole ta sake satar jiki ta sake garzayawa wajen likita Nebrass ta gaya masa kukanta, don an bai wa Mu’azzam query daga Chevron kan yana wasa da aiki yanzu, za’a iya sallamarsa ko rage masa matsayi daga yanzu zuwa kowanne lokaci idan bai gyara ba.
Dr. Nebrass ya zauna da taimakon wasu manyan likitoci ‘yan uwansa kan lamarin Mu’azzam. Domin sosai yake tausayawa Aalimah, ta damu da mijinta sosai, ya kuma gama fahimtar tana matukar son sa. A daya bangaren yana tausaya wa Mu’azzam din. Shekaru daidai kenan har goma sha biyar, yana rayuwa kan shan magani. Ya yi aure matar ta kasa jurewa. Ya warware maganinsa ya zama barazana ga aikinsa. Don sam Mu’azzam ya daina yin cikakkun awanni uku a office sai a jikin Aalimah. Daya daga cikinsu wanda ya zo daga asibitin Johns Hopkin, shi ne ya yi suggesting wani magani wanda yake ganin zai yi daidai da Mu’azzam, ya zauna lafiya da matarsa da kuma aikinsa.
Amma yana da matukar tsada. Amma da gudu Mu’azzam ya amince da wannan tsadadden maganin. Sai ya kasance Mu’azzam na yin sati ma bai bukaci sex ba, amma bayan cikar satin a duk ranar da abin ya juyo, Aalimah na ji a jikinta, amma ba ya wuce na kwana biyu, rabin albashinsa kuma na tafiya wajen sayen magunguna. Wannan ita ce rayuwar auren Aalimah da Mu’azzam a birnin Las Vegas.
Daidai wannan lokacin Aalimah ta fahimci yaron ciki a tare da ita.
A ranar data fahimci hakan, daki ta shige ta fuskanci alqibla ta yi sujudush-shukr ga Ubangijinta.
7/11/21, 9:41 PM - Buhainat: Don haka iyayen suka mika al’amarin kotun muslunci, inda kotu ta dankawa Aalimah mas’alar auren ta a tafin hannunta. Cewa in ta fi son zama da Aboulkhair za’a yi amfani da shari’ah, kotu ta yi wa Mu’azzam khul’i ta ci gaba da rayuwar aure da Aboulkhair, idan kuma ta zabi ci gaba da zama da mijinta uban ‘ya’yanta, to ta koma dakinta. Wannan karon babu wanda zai yi mata shisshigi. Sun ba ta dukkan damar ta da addini ya ba ta.
Aalimah bata yi wata-wata ba ta ce ta zabi Mu’azzam ya cigaba da auren ta sabida ‘ya’yan dake tsakaninsu da wasu dalilai da dama. Sannan ta nisa, kafin ta dago idanunta cike da hawaye ta nemi kotu alfarmar tana son Mu’azzam ya sake ta (ba khul’i ba), bata da ra’ayin sake zama da ko dayan su alhalin duk suna raye, in har da gaske addini ita ya bawa zabi a hannunta, to ta zabi Mu’azzam, a gefen hakan tana neman alfarmar ya sake ta, ba kuma don ta komawa Aboulkhair ba, sai don rabuwa dasu bakidaya yafi mata kwanciyar hankali. Ba zata iya kallon daya ba, alhalin tana auren daya. Tana kuka take rokon Alkali mai shari’ah ya roka mata Mu’azzam wannan alfarmar in har da gaske an damka mata ragamar auren nata a hannunta babu takurawar kowa cikin iyayen su. To wannan shine zabin ta.
Gabadaya iyayen sai suka sadda kansu kasa. Alkali kuma yace wannan tsakaninta da mijin ta Mu’azzam ne amma kamar yadda tace ya roka mata alfarma sai ya maimaitawa Mu’azzam alfarmar da Aalimah ta roka daga gare shi.
Koda aka waiwayi Mu’azzam kan wannan alfarma da Aalimah ta nema, daburcewa yayi, wata irin kidima ya shiga irin wadda bai taba shiga a rayuwar sa ba, daga bisani ya karfafi kansa da ya ga irin kukan da Aalimah take yi a gaban kowa, ya ce shi da hannunsa bazai iya rubuta saki a gareta ba, amma ta je ya warware igiyar aurensu guda daya (a fatar bakinsa). Tunda abinda ta zaba kenan. Kuma ta ce shine kwanciyar hankalin ta. Yana mata fatan alkhairi a gabadayan tsayin rayuwarta ta gaba. Daga haka ya mike ya bar kotun.
Mummy sai ta fashe da kuka, ta kifa kanta cikin cinyoyinta tana ta yi, wannan wace irin kaddara ce ta fadowa rayuwar ‘ya’yanta haka! Aboulkhair kuma ya sunkuyar da kansa, hawaye na tsirgowa daga cikin idanunsa, cike da nadamar dawowar sa cikinsu.
Da ya san abinda zai tarar kenan, da abinda dawowar sa zata haifar a rayuwar Mu’azzam, da ko kusa bai yi gigin dawowa ba.
Da ya karasa rayuwarsa can inda yake, a matsayin matacce a garesu.
Bai so ya zamo barrier ga farin cikin rayuwar Mu’azzam ba!.
Bai so dawowarsa ta rusa kyakkyawar rayuwar Mu’azzam da iyalin sa ba!!
Ya yarda rabuwarsa da Aalimah a yanzu, daidai yake da maida hannun agogo baya!!!
Haka suka koma gida kowa jiki a mace. Kowa ka gani gidan Malam Raazee a wannan rana sai ka fahimci akwai babban al’amarin da ya taba zuciyarsa.
Walwalarsu ta ragu, kuzarinsu ya ragu, kowa jikinsa a sanyaye.
Amma Oncle Mainasara ya ji dadin wannan lamari. Ya tabbata wannan karon Dan sa Anas zai samu abinda ya dade yana so. Tsuntsu ne ya fado daga sama gasashshe.
A daren ranar Mu’azzam yayi booking zai tashi U.S a safiyar washegari tare da ‘ya’yansa.
Ko a fuska bai canzawa Aboulkhair ba, Aboulkhair din ne ya kasance cikin damuwar da har ta kai shi ga kuka akan cinyar Mu’azzam. Ba kukan Aalimah bata zabi zama da shi yake yi ba, kukan zamowar sa silar rugurgujewar farin cikin rayuwar Mu’azzam ne.
A ganinsa Mu’azzam bai cancanci haka daga gareshi ba. Me yasa ya kasa sadaukar masa da Aalimah tun a tashin farko?
Gashi yanzu an bata goma daya bata gyaru ba.
Ji yayi soyayyar Aaliman tana yin wani irin fiffike tana ficewa!!!
Domin Mu’azzam ya cancanci ya bashi rayuwarsa dungurungum in ana badawa.
Bai gayawa Aboulkhair yayi booking ba ganin halin damuwar da yake ciki ya kuma kasa tsaida hawayen idanunsa tun dawowar su daga kotu kada ya kara masa damuwa.
Baya so ya kara raunana shi.
Amma dole da asubahin ranar bayan sun dawo masallaci ya gaya masa zai tashi Las Vegas da karfe goma na safe, yana bashi shawara idan ya kara hutawa ya gaggauta zuwa ya taho da matarsa Sa’eedah.
Hankalin Aboulkhair ya kara tashi, shi ya manta da Sa’eedah. Fargabar halin da Mu’azzam zai fada in ya koma gida shi kadai da kananan yara ya addabi zuciyar sa. Ko bai fada ba Mu’azzam ya ga hakan a kwayar idonsa.
Tun abubuwa na tafiya gentle-gentle, har komai ya kwace wa Mu’azzam. Ya zama out of his control. Tsayin daren bakidaya za ta iya cewa, ko na minti talatin Mu’azzam bai barta ta huta ba. Har ita da kanta ta gane ba ta da wayo, abin da ta je ta sa likita ya yi masa.
Washegari ko da ya je office ma bai wuce awanni uku ba sai ga shi ya dawo a wani yanayi da dole ta amsa kiransa. Ya sake komawa office ba a yi closing ba ya dawo. Tsayin kwanaki bakwai a haka suke, tana kwarara kanta, tana karfafa gangar jikinta da zuciyarta. Ga dai biyan bukata ta samu, amma kuma shi Mu’azzam din tana tausaya masa. Ta kuma gane hakan zai iya zama barazana ga aikinsa, tunda ba ya maida hankali gare shi. Ba inda yake zuwa, ya daina kulla komai, in dai yana cikin gidan to aikin kenan, ko isasshen abinci ba ya iya ci, har ramewa ya yi, ita ma ta jigata ta rame. Don haka dole ta sake satar jiki ta sake garzayawa wajen likita Nebrass ta gaya masa kukanta, don an bai wa Mu’azzam query daga Chevron kan yana wasa da aiki yanzu, za’a iya sallamarsa ko rage masa matsayi daga yanzu zuwa kowanne lokaci idan bai gyara ba.
Dr. Nebrass ya zauna da taimakon wasu manyan likitoci ‘yan uwansa kan lamarin Mu’azzam. Domin sosai yake tausayawa Aalimah, ta damu da mijinta sosai, ya kuma gama fahimtar tana matukar son sa. A daya bangaren yana tausaya wa Mu’azzam din. Shekaru daidai kenan har goma sha biyar, yana rayuwa kan shan magani. Ya yi aure matar ta kasa jurewa. Ya warware maganinsa ya zama barazana ga aikinsa. Don sam Mu’azzam ya daina yin cikakkun awanni uku a office sai a jikin Aalimah. Daya daga cikinsu wanda ya zo daga asibitin Johns Hopkin, shi ne ya yi suggesting wani magani wanda yake ganin zai yi daidai da Mu’azzam, ya zauna lafiya da matarsa da kuma aikinsa.
Amma yana da matukar tsada. Amma da gudu Mu’azzam ya amince da wannan tsadadden maganin. Sai ya kasance Mu’azzam na yin sati ma bai bukaci sex ba, amma bayan cikar satin a duk ranar da abin ya juyo, Aalimah na ji a jikinta, amma ba ya wuce na kwana biyu, rabin albashinsa kuma na tafiya wajen sayen magunguna. Wannan ita ce rayuwar auren Aalimah da Mu’azzam a birnin Las Vegas.
Daidai wannan lokacin Aalimah ta fahimci yaron ciki a tare da ita.
A ranar data fahimci hakan, daki ta shige ta fuskanci alqibla ta yi sujudush-shukr ga Ubangijinta.
7/11/21, 9:41 PM - Buhainat: Don haka iyayen suka mika al’amarin kotun muslunci, inda kotu ta dankawa Aalimah mas’alar auren ta a tafin hannunta. Cewa in ta fi son zama da Aboulkhair za’a yi amfani da shari’ah, kotu ta yi wa Mu’azzam khul’i ta ci gaba da rayuwar aure da Aboulkhair, idan kuma ta zabi ci gaba da zama da mijinta uban ‘ya’yanta, to ta koma dakinta. Wannan karon babu wanda zai yi mata shisshigi. Sun ba ta dukkan damar ta da addini ya ba ta.
Aalimah bata yi wata-wata ba ta ce ta zabi Mu’azzam ya cigaba da auren ta sabida ‘ya’yan dake tsakaninsu da wasu dalilai da dama. Sannan ta nisa, kafin ta dago idanunta cike da hawaye ta nemi kotu alfarmar tana son Mu’azzam ya sake ta (ba khul’i ba), bata da ra’ayin sake zama da ko dayan su alhalin duk suna raye, in har da gaske addini ita ya bawa zabi a hannunta, to ta zabi Mu’azzam, a gefen hakan tana neman alfarmar ya sake ta, ba kuma don ta komawa Aboulkhair ba, sai don rabuwa dasu bakidaya yafi mata kwanciyar hankali. Ba zata iya kallon daya ba, alhalin tana auren daya. Tana kuka take rokon Alkali mai shari’ah ya roka mata Mu’azzam wannan alfarmar in har da gaske an damka mata ragamar auren nata a hannunta babu takurawar kowa cikin iyayen su. To wannan shine zabin ta.
Gabadaya iyayen sai suka sadda kansu kasa. Alkali kuma yace wannan tsakaninta da mijin ta Mu’azzam ne amma kamar yadda tace ya roka mata alfarma sai ya maimaitawa Mu’azzam alfarmar da Aalimah ta roka daga gare shi.
Koda aka waiwayi Mu’azzam kan wannan alfarma da Aalimah ta nema, daburcewa yayi, wata irin kidima ya shiga irin wadda bai taba shiga a rayuwar sa ba, daga bisani ya karfafi kansa da ya ga irin kukan da Aalimah take yi a gaban kowa, ya ce shi da hannunsa bazai iya rubuta saki a gareta ba, amma ta je ya warware igiyar aurensu guda daya (a fatar bakinsa). Tunda abinda ta zaba kenan. Kuma ta ce shine kwanciyar hankalin ta. Yana mata fatan alkhairi a gabadayan tsayin rayuwarta ta gaba. Daga haka ya mike ya bar kotun.
Mummy sai ta fashe da kuka, ta kifa kanta cikin cinyoyinta tana ta yi, wannan wace irin kaddara ce ta fadowa rayuwar ‘ya’yanta haka! Aboulkhair kuma ya sunkuyar da kansa, hawaye na tsirgowa daga cikin idanunsa, cike da nadamar dawowar sa cikinsu.
Da ya san abinda zai tarar kenan, da abinda dawowar sa zata haifar a rayuwar Mu’azzam, da ko kusa bai yi gigin dawowa ba.
Da ya karasa rayuwarsa can inda yake, a matsayin matacce a garesu.
Bai so ya zamo barrier ga farin cikin rayuwar Mu’azzam ba!.
Bai so dawowarsa ta rusa kyakkyawar rayuwar Mu’azzam da iyalin sa ba!!
Ya yarda rabuwarsa da Aalimah a yanzu, daidai yake da maida hannun agogo baya!!!
Haka suka koma gida kowa jiki a mace. Kowa ka gani gidan Malam Raazee a wannan rana sai ka fahimci akwai babban al’amarin da ya taba zuciyarsa.
Walwalarsu ta ragu, kuzarinsu ya ragu, kowa jikinsa a sanyaye.
Amma Oncle Mainasara ya ji dadin wannan lamari. Ya tabbata wannan karon Dan sa Anas zai samu abinda ya dade yana so. Tsuntsu ne ya fado daga sama gasashshe.
A daren ranar Mu’azzam yayi booking zai tashi U.S a safiyar washegari tare da ‘ya’yansa.
Ko a fuska bai canzawa Aboulkhair ba, Aboulkhair din ne ya kasance cikin damuwar da har ta kai shi ga kuka akan cinyar Mu’azzam. Ba kukan Aalimah bata zabi zama da shi yake yi ba, kukan zamowar sa silar rugurgujewar farin cikin rayuwar Mu’azzam ne.
A ganinsa Mu’azzam bai cancanci haka daga gareshi ba. Me yasa ya kasa sadaukar masa da Aalimah tun a tashin farko?
Gashi yanzu an bata goma daya bata gyaru ba.
Ji yayi soyayyar Aaliman tana yin wani irin fiffike tana ficewa!!!
Domin Mu’azzam ya cancanci ya bashi rayuwarsa dungurungum in ana badawa.
Bai gayawa Aboulkhair yayi booking ba ganin halin damuwar da yake ciki ya kuma kasa tsaida hawayen idanunsa tun dawowar su daga kotu kada ya kara masa damuwa.
Baya so ya kara raunana shi.
Amma dole da asubahin ranar bayan sun dawo masallaci ya gaya masa zai tashi Las Vegas da karfe goma na safe, yana bashi shawara idan ya kara hutawa ya gaggauta zuwa ya taho da matarsa Sa’eedah.
Hankalin Aboulkhair ya kara tashi, shi ya manta da Sa’eedah. Fargabar halin da Mu’azzam zai fada in ya koma gida shi kadai da kananan yara ya addabi zuciyar sa. Ko bai fada ba Mu’azzam ya ga hakan a kwayar idonsa.