Sashe 44
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*****
Watanni uku aka sanya auren Aboulkhair da Aalimah, Aboubacar da Basma. A wannan lokacin Aboulkhair ya haye jarrabawarsa ta specialty da suke kira primaries a Psychiatry, ya zama junior registrar. Shekaru biyu baya ya sake yin jarrabawa part 1 ya haye cike da dumbin nasara ya zama senior registrar in Psychiatry. Asibitin Desert Parkway dake garin Las Vegas nan ya tura takardunsa neman aiki, don kawai ya zauna kusa da dan uwansa ya kula da shi, shi ya sa bai nema a garin da iyayensa suke zaune ba.
A ganinsa Mu’azzam ya fi su bukatarsa kusa da shi duk da ya san Mu’az ba zai yarda su zauna gida guda ba sabida rashin son hayaniyarsa, amma a kalla suna gari daya, koyaushe yake son ganinsa zai je, zai maido da kulawarsa bakidaya wuyansa, tunda dama saboda shi ya karanci wannan bangaren.
Idan ya yi shekaru biyu ko uku yana practicing kuma zai koma John Hopkins ya sake yin wata jarrabawar part 2 suke kiranshi, idan har ya ci shi kenan ya zama cikakken consultant (neuro psychiatrist). Duka wannan wahala da jajircewa ba don kowa Aboulkhair ke yi ba, ba don kansa ba, ba don shiryawa kai future ba, sai don ya kula da lafiyar Yayansa Mu’azzam.
6/29/21, 9:00 AM - Buhainat: 6
Sanda ya shigo gidan, Aalimah na kwance a three seater, idanunta a lumshe kamar mai barci da carbi a hannunta. Ko kusa ba ta ji shigowarsa ba sai zamansa bayan ya kwashe kafafunta ya zauna a muhallinsu, ya maida su bisa cinyoyinsa. Yatsun kafar ya shiga kallo kamar yau ya fara ganinsu. A hankali ya shiga ja mata yatsun daya bayan daya, uffan bai ce ba, gabadaya tafukan kafar nata masu tsananin taushi da suka sha adon jan lalle suna cikin hannayensa. Aalimah ta dada runtse idonta, wani abu ne da bai taba faruwa da ita batun tashin ta. Wato jikinta ya kusanci na wani da namiji, balle wannan ba wani ba ne face mutumin da zuciya da ruhinta suka dade suna mafarkin mallaka, Aboulkhair ne, dan uwanta da a yanzu yake amsa sunan mijinta, mahadin rayuwarta.
Katon mayafin ya shiga zarewa a hankali yana kiran sunanta. Dagota ya yi bakidaya ya aza a jikinsa, bayan ya yi nasarar zare mayafin, ya saura daga Aalimah sai rigar barcin da Gumsu ta zaba mata, wadda a cewarta ita ce ta dace da wannan ranar a gare ta, kuma irinta ta zaba wa Basma. Sunanta kawai yake kira, yana so ta bude ido ya kalli kwayar idanunta da ya dade bai samu alfarmar gani ba.Yayin da hannayensa biyu ke karadewa suna rungume ta a dukkan jikinshi.
Wata irin ajiyar zuciya Aboulkhair da ita kanta Aalimah ke saukewa akai-akai, zuciyoyinsu na tuno musu tsawon lokacin da suka dauka suna dakon zuwan wannan ranar, shekaru biyar cif! Ashe komai in aka yi hakuri aka bi dokar Ubangiji, aka yi biyayya ga iyaye komai nisansa watarana za a kai ga cimmasa ta tsaftacciyar hanya.
A wannan rana mai dumbin tarihi cikin rayuwarta, Aboulkhair Ishaq Raazee ya tabbatar mata ya wahala ba kadan ba, cikin dakon kaunarta da jiran wannan muhimmiyar rana a gare shi, wadda ranakunta suka shude a daddafe tamkar ba za ta taba zuwa ba. Kaunar ya nuna mata filla-filla da wani irin salo mai tsayawa a zuciyar diya mace. Aalimah, ta yarda ta amince; a daren yau son da Aboulkhair ke mata ya rinjayi nata, duk da yadda a baya ta ke zaton zuciyarta mai kankanba ce a kansa. Tun tana sanya wa ranta juriya da ganin cewa, lamarin mai iyaka ne tunda dai Aboulkhair mai sonta ne, mai tausayinta ne, har ta amince wannan ita ce ranar rashin tausayi ta duniya a rayuwar Aboulkhair. Ba ta kuma da wani yunkuri da za ta iya na kwatar kai, ko ceton kai, sai yadda Aboulkhair ya ga dama da rayuwarta.
A tsayin daren bakidaya Aboulkhair bai dawo Aboulkhairinsa ba sai da ya fahimci Aalimah duk juriya da dauriyarta da ta ke yi domin ya samu nutsuwa, domin ya tabbatar ba shi kadai ya yi wahalar shekaru biyar ba, ita din kuma ya cutar da lafiyarta ba dan kadan ba.
Shi likita, ita mai bada magani, don haka taruwa suka yi suka taimaki kansu ba tare da taimakon kowa ba, ba tare da wani ya ji ya gani ba. Ko Gumsu da suka biyo yi musu sallama washegari ta yi tsokanar duniyar nan, Aalimah ba ta tanka ba, sai murmushi da rufe ido. Shi kuma suna zuwa ya bar gidan ko gaisawa ba su yi ba. Rana ta farko da ya ji yana jin kunyar Mummy a rayuwarsa. Ya gode wa Allah da Mu’az ba ya nan, kallon cikin idanunsa a yau ya tambaye shi ya amarya ta kwana babban tashin hankali ne a gare shi. Saboda Mu’az ya san komai nasa tamkar a tafin hannunshi, ko da kuwa bai furta masa ba.
Ba su dade ba suka yi sallama da ita suka tafi, direban Mu’az har Massachusetts zai kai su, ya hana su bi motar kasuwa, kuma ya ce kada su sa Aboulkhair tuki ya bar matarsa a garin ita kadai bata saba ba.
******
“Sun tafi?†Aboulkhair ya tambayi Aalimah daga bakin kofa, yana mai leko kansa dakin kamar mara gaskiya.
Murmushi ta yi ba tare da ta juyo ba ta ci gaba da shafa manta a lallausar fatar jikinta. Alamu sun nuna daga wanka ta fito.
Ya karasa shigowa dakin ya isa gare ta, ya rungume ta ta baya yana sunsunar bathrobbs din da ta yi amfani da shi, suka kama fatar jikinta da karfin gaske, yana wani lumshe idanu. A karshe ya juyo ta bakidaya suka fuskanci juna. Kallonta ya yi, kamar ya hadiye ta don so, hannayensa na bisa kafadunta, goshinsa hade da nata, karan hancinsu na zungurar na juna.
Ya ce, “Kwanta ‘yar Gumsu in duba stitches dinâ€.
Hannayenta biyu ta sa ta rufe fuskarta tare da yin baya da sauri za ta gudu. Da azama ya cafko ta.
“Mun wuce wannan stage din Aalimah, ki kwanta in dubaâ€.
Yadda ya yi maganar cikin seriousness ya sa ta bi umarninsa.
Rungume ta ya yi sosai, yana fadin, “I’m sorry Aal, really sorry. Ba Aboulkhair ba ne ya aikata wannan laifin sabon mijin Aalimah ne. Shi Aboulkhair ai kin san shi mai tausayi ne ko?â€.
Ya hau sumbatarta kusfa-kusfa yana rokonta ta yafe masa. Toshe masa baki ta yi da tausasan yatsunta.
“Aalimahr is nothing but his wife wadda Allah ya yi masa izinin ya zo mata sanda ya so, duk ta inda ya yi umarni, ita din gona ce a gare shi. In dai Aboulkhair ne yanzu ma ya maimaita goman laifin nan a shirye Aalimah take da karbarsa cikin kowanne hali Monsieur Aboulkhair. Na san ba rashin so ba ne, kauna ce. Kaunar ma ta Aboulkhair ga Aalimah, ‘yar asali, mai dogon tarihi, wadda ta cancanci bugawa a littafi da na iya rubutuâ€.
Murmushi Aboulkhair yake ta yi, wanda ke fitowa kai tsaye daga zuciyarsa, a lokaci guda yana mai cakuda yatsunsa cikin lallausar gashin kanta, ya ce,
“Gara da ba ki iya ba. haka kawai! Masu karantawar su ce… su ce…â€
Dariya Aalimah ta saki, ta ce, “Su ce me?â€
Karan hancinta ya kama ya ja da karfi, ya ce, “Na ki fada din, balle ki fara rubutun a kaina. Ki dai fara a kan wannan Gumsun uwar taki mai budurwar zuciyaâ€.
Dukkansu dariya suka saki suna kewarta.
Ya ce, “A duniya ina son Aunty Gumsu, amma kwanan nan tana shigar min hanci, she’sannoyingâ€.
Aalimah ta ce, “Ba ka ga abin da ta yi wa Basma ba, namu nafila ne. Har daga zanin gadon ta ke tana shiga da shi daki-daki wai wadanda ba su gani ba su zo su ganiâ€.
Ya girgiza kai, ya ce, “Shi ya sa na zage na wanke abuna kada ta dauki hoto ta tura Nigerâ€.
Watanni uku aka sanya auren Aboulkhair da Aalimah, Aboubacar da Basma. A wannan lokacin Aboulkhair ya haye jarrabawarsa ta specialty da suke kira primaries a Psychiatry, ya zama junior registrar. Shekaru biyu baya ya sake yin jarrabawa part 1 ya haye cike da dumbin nasara ya zama senior registrar in Psychiatry. Asibitin Desert Parkway dake garin Las Vegas nan ya tura takardunsa neman aiki, don kawai ya zauna kusa da dan uwansa ya kula da shi, shi ya sa bai nema a garin da iyayensa suke zaune ba.
A ganinsa Mu’azzam ya fi su bukatarsa kusa da shi duk da ya san Mu’az ba zai yarda su zauna gida guda ba sabida rashin son hayaniyarsa, amma a kalla suna gari daya, koyaushe yake son ganinsa zai je, zai maido da kulawarsa bakidaya wuyansa, tunda dama saboda shi ya karanci wannan bangaren.
Idan ya yi shekaru biyu ko uku yana practicing kuma zai koma John Hopkins ya sake yin wata jarrabawar part 2 suke kiranshi, idan har ya ci shi kenan ya zama cikakken consultant (neuro psychiatrist). Duka wannan wahala da jajircewa ba don kowa Aboulkhair ke yi ba, ba don kansa ba, ba don shiryawa kai future ba, sai don ya kula da lafiyar Yayansa Mu’azzam.
6/29/21, 9:00 AM - Buhainat: 6
Sanda ya shigo gidan, Aalimah na kwance a three seater, idanunta a lumshe kamar mai barci da carbi a hannunta. Ko kusa ba ta ji shigowarsa ba sai zamansa bayan ya kwashe kafafunta ya zauna a muhallinsu, ya maida su bisa cinyoyinsa. Yatsun kafar ya shiga kallo kamar yau ya fara ganinsu. A hankali ya shiga ja mata yatsun daya bayan daya, uffan bai ce ba, gabadaya tafukan kafar nata masu tsananin taushi da suka sha adon jan lalle suna cikin hannayensa. Aalimah ta dada runtse idonta, wani abu ne da bai taba faruwa da ita batun tashin ta. Wato jikinta ya kusanci na wani da namiji, balle wannan ba wani ba ne face mutumin da zuciya da ruhinta suka dade suna mafarkin mallaka, Aboulkhair ne, dan uwanta da a yanzu yake amsa sunan mijinta, mahadin rayuwarta.
Katon mayafin ya shiga zarewa a hankali yana kiran sunanta. Dagota ya yi bakidaya ya aza a jikinsa, bayan ya yi nasarar zare mayafin, ya saura daga Aalimah sai rigar barcin da Gumsu ta zaba mata, wadda a cewarta ita ce ta dace da wannan ranar a gare ta, kuma irinta ta zaba wa Basma. Sunanta kawai yake kira, yana so ta bude ido ya kalli kwayar idanunta da ya dade bai samu alfarmar gani ba.Yayin da hannayensa biyu ke karadewa suna rungume ta a dukkan jikinshi.
Wata irin ajiyar zuciya Aboulkhair da ita kanta Aalimah ke saukewa akai-akai, zuciyoyinsu na tuno musu tsawon lokacin da suka dauka suna dakon zuwan wannan ranar, shekaru biyar cif! Ashe komai in aka yi hakuri aka bi dokar Ubangiji, aka yi biyayya ga iyaye komai nisansa watarana za a kai ga cimmasa ta tsaftacciyar hanya.
A wannan rana mai dumbin tarihi cikin rayuwarta, Aboulkhair Ishaq Raazee ya tabbatar mata ya wahala ba kadan ba, cikin dakon kaunarta da jiran wannan muhimmiyar rana a gare shi, wadda ranakunta suka shude a daddafe tamkar ba za ta taba zuwa ba. Kaunar ya nuna mata filla-filla da wani irin salo mai tsayawa a zuciyar diya mace. Aalimah, ta yarda ta amince; a daren yau son da Aboulkhair ke mata ya rinjayi nata, duk da yadda a baya ta ke zaton zuciyarta mai kankanba ce a kansa. Tun tana sanya wa ranta juriya da ganin cewa, lamarin mai iyaka ne tunda dai Aboulkhair mai sonta ne, mai tausayinta ne, har ta amince wannan ita ce ranar rashin tausayi ta duniya a rayuwar Aboulkhair. Ba ta kuma da wani yunkuri da za ta iya na kwatar kai, ko ceton kai, sai yadda Aboulkhair ya ga dama da rayuwarta.
A tsayin daren bakidaya Aboulkhair bai dawo Aboulkhairinsa ba sai da ya fahimci Aalimah duk juriya da dauriyarta da ta ke yi domin ya samu nutsuwa, domin ya tabbatar ba shi kadai ya yi wahalar shekaru biyar ba, ita din kuma ya cutar da lafiyarta ba dan kadan ba.
Shi likita, ita mai bada magani, don haka taruwa suka yi suka taimaki kansu ba tare da taimakon kowa ba, ba tare da wani ya ji ya gani ba. Ko Gumsu da suka biyo yi musu sallama washegari ta yi tsokanar duniyar nan, Aalimah ba ta tanka ba, sai murmushi da rufe ido. Shi kuma suna zuwa ya bar gidan ko gaisawa ba su yi ba. Rana ta farko da ya ji yana jin kunyar Mummy a rayuwarsa. Ya gode wa Allah da Mu’az ba ya nan, kallon cikin idanunsa a yau ya tambaye shi ya amarya ta kwana babban tashin hankali ne a gare shi. Saboda Mu’az ya san komai nasa tamkar a tafin hannunshi, ko da kuwa bai furta masa ba.
Ba su dade ba suka yi sallama da ita suka tafi, direban Mu’az har Massachusetts zai kai su, ya hana su bi motar kasuwa, kuma ya ce kada su sa Aboulkhair tuki ya bar matarsa a garin ita kadai bata saba ba.
******
“Sun tafi?†Aboulkhair ya tambayi Aalimah daga bakin kofa, yana mai leko kansa dakin kamar mara gaskiya.
Murmushi ta yi ba tare da ta juyo ba ta ci gaba da shafa manta a lallausar fatar jikinta. Alamu sun nuna daga wanka ta fito.
Ya karasa shigowa dakin ya isa gare ta, ya rungume ta ta baya yana sunsunar bathrobbs din da ta yi amfani da shi, suka kama fatar jikinta da karfin gaske, yana wani lumshe idanu. A karshe ya juyo ta bakidaya suka fuskanci juna. Kallonta ya yi, kamar ya hadiye ta don so, hannayensa na bisa kafadunta, goshinsa hade da nata, karan hancinsu na zungurar na juna.
Ya ce, “Kwanta ‘yar Gumsu in duba stitches dinâ€.
Hannayenta biyu ta sa ta rufe fuskarta tare da yin baya da sauri za ta gudu. Da azama ya cafko ta.
“Mun wuce wannan stage din Aalimah, ki kwanta in dubaâ€.
Yadda ya yi maganar cikin seriousness ya sa ta bi umarninsa.
Rungume ta ya yi sosai, yana fadin, “I’m sorry Aal, really sorry. Ba Aboulkhair ba ne ya aikata wannan laifin sabon mijin Aalimah ne. Shi Aboulkhair ai kin san shi mai tausayi ne ko?â€.
Ya hau sumbatarta kusfa-kusfa yana rokonta ta yafe masa. Toshe masa baki ta yi da tausasan yatsunta.
“Aalimahr is nothing but his wife wadda Allah ya yi masa izinin ya zo mata sanda ya so, duk ta inda ya yi umarni, ita din gona ce a gare shi. In dai Aboulkhair ne yanzu ma ya maimaita goman laifin nan a shirye Aalimah take da karbarsa cikin kowanne hali Monsieur Aboulkhair. Na san ba rashin so ba ne, kauna ce. Kaunar ma ta Aboulkhair ga Aalimah, ‘yar asali, mai dogon tarihi, wadda ta cancanci bugawa a littafi da na iya rubutuâ€.
Murmushi Aboulkhair yake ta yi, wanda ke fitowa kai tsaye daga zuciyarsa, a lokaci guda yana mai cakuda yatsunsa cikin lallausar gashin kanta, ya ce,
“Gara da ba ki iya ba. haka kawai! Masu karantawar su ce… su ce…â€
Dariya Aalimah ta saki, ta ce, “Su ce me?â€
Karan hancinta ya kama ya ja da karfi, ya ce, “Na ki fada din, balle ki fara rubutun a kaina. Ki dai fara a kan wannan Gumsun uwar taki mai budurwar zuciyaâ€.
Dukkansu dariya suka saki suna kewarta.
Ya ce, “A duniya ina son Aunty Gumsu, amma kwanan nan tana shigar min hanci, she’sannoyingâ€.
Aalimah ta ce, “Ba ka ga abin da ta yi wa Basma ba, namu nafila ne. Har daga zanin gadon ta ke tana shiga da shi daki-daki wai wadanda ba su gani ba su zo su ganiâ€.
Ya girgiza kai, ya ce, “Shi ya sa na zage na wanke abuna kada ta dauki hoto ta tura Nigerâ€.