← Book details Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 91

Sashe 6

Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

*****
Aalimah, ta ja dogon numfashi a yayin da tunaninta ya zo nan, tana kallon su Basma na shigowa falon, babu kamannin ‘ya’yan Auzinawa ko na Malam Bahaushe ko kadan a tare da su, sun fi kama da ‘ya’yan kasar Somalia. Fatar Babansu da ta mamansu bahaushiya ta cakude ta ba su wata irin colour da complexion mai ban sha’awa. Ga su da tsayi da mulmulallen jiki tubarkallah. Sunshades a idanun Basma da Khaleesat, dogayen wandunan jeans na mata da rigunan Armani collection a jikin kowaccensu. Khaleesa ta kusa kamo Basma a tsayi, babu dankwali a kansu gashin Abzin din ya kwanta a kafadunsu.
Basma a gaba, sai Yesmin biye da ita, sannan Khaleesa, Aunty Zulaiha da Daddy suka biyo bayansu.
Tsayawa ta yi a kofar kicin din ta harde hannayenta a kirjinta tana kallonsu da murmushi irin na ‘yan uwantaka. Khaleesat ce ta fara ganinta, ta zare sun shade dinta ta mutstsika idanunta ta ce,
“Daddy, am I dreaming? She looks so much like Aalimahâ€. (Daddy Mafarki nake yi? Ta yi kama sosai da Aalimah). Sannan ne hankalin kowa ya kai gare ta.
Aunty Zulaiha kam shaf! Ta manta da zuwanta, sai yanzu ta tuna. Take fuskarta ta sauya, ta wuce upstairs kai tsaye.
Basma ta yi cilli da jakarta ta yi kanta da dan banzan gudu, saura kadan su sha kasa su duka biyun, tana kakabin murna. Daddy ya wuce kujerun falon ya ajiye suitcasedinshi, yana rike da falmaran din suit din jikinshi. Gogaggen dan boko wanda ya ga jiya a Amurka yake kuma ganin yau, ga furfura nan tsilli-tsilli a kanshi, amma tsammani za ka yi Balarabe ne ba ba’abzine ba. Dogon hancin nan zur! Kamar na Babanta.
Kujera ya samu ya zauna a gajiye yana kallon Aalimah da ke tahowa, Basma da Khaleesa sun sako ta a tsakiya har gabansa, sun bi sun rirrike hannunta, bakinsu kamar zai tsage don farin ciki, kan kujerar suke kokarin zaunar da ita kusa da Daddyn, amma sai ta zame ta zauna a kasa daura da kafafunsa ta soma gaishe shi cikin harshen Hausa.
Cewa yake, “Tashi-tashi ‘yata ki zauna a kujera, kin sha hanya. Ki yi hakuri I couldn’t make it taking you from airport, I went to California for a meeting, dawowata kenan. Ina fatan kin ci abinci kin huta?â€
Murmushi ta yi, ta ce,
“Babu damuwa Daddy, kuma na ci abinciâ€.
Ya kalli Basma ya ce, “ Basma bani jakar canâ€.
Ta dauko jakar ta kawo masa babu ko russunawa kamar ta mikawa sa’anta, Aalimah ta ji wani iri a ranta. Budewa ya yi ya fiddo wasu takardu ya mika wa Basma, ya kuma mika wa Aalimahn wasu irinsu. Ya bawa kowaccensu biro ya ce ta sanya hannu karkashin dokokin jami’ar da za su je. Sai a lokacin ne Aalimah ta ga admission letter dinta da kwas din da Babanta ya zaba mata.
Zukar numfashi ta yi ta fesar, tana rokon Allah ya fidda ita kunyar iyayen ta, ta sha ji a bakin Yayanta Aboubacar how complicated pharmacy is (tsaurin kwas din harhada magunguna) lokacin da Daddy ya ce ya karanta shi don shine abinda Kakansa Prof. Kashim ya karanta ya kuma zauna akan (proffessorial chair) dinsa har mutuwar sa, ko don ya farantawa Mama, Aboubacar ya fitittike ya ce shi ba zai iya ba, Accounting yake so.
Nasiha sosai Daddyn ya yi musu a kan su tsare mutuncinsu, su maida hankali kan abin da ya kai su. Bai yarda da yin saurayi ko friendship da maza ba, duk kuma ranar da ya ga hakan zai cire kowaccensu ne ya yi mata aure. A karshe ya yi musu addu’a, ya gaya musu jibi za su fara registration.

3094856450
Sumayyah Kabara
Firstbank
Price 1&2 N400
6/28/21, 7:31 AM - Buhainat: 🌹 *Aalimah* 🌹
*
*SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI*

FREE PAGES 6
Chapter 6 · 0% Book details