Sashe 67
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Malam ga shi Inna Bintou ta ce a kawoâ€.
Hannu biyu ya sa ya karba ya ce, “Madalla da Bintou da jikanyar ta, an gaishe ku, madallahâ€.
Ta juya za ta fita, sai kuma ta dawo ta tsuguna.
“Malam Aunty Gumsu-Moiram ta yi min waya dazu tace in je in mata kwana biyu, na ce mata sai na tambaye ka tukunnaâ€.
Ya ce, “Ba yanzu ba Moiram ta yi hakkuri, bana so ki je ko’ina sai kin warware dukkanki, har yanzu ban ganki kamar yadda nasan ki ba, a bai wa Gumsu hakkuri inji niâ€.
Fuska a sake ta ce, “toh Malamâ€.
Ta juya ga Daddy ta gaishe shi cikin nutsuwa da sanyin muryarta.
Ya ce, “Anya Aalimah? Haka dan Adam zai rayu da damuwa bayan ba abin da za ta sa, ba abin da za ta hana? Dubi kasusuwan wuyanki, dubi idanunki yadda suka zuzzurma ciki. Don Allah don Annabi Aalimah ni Baban ABOULKHAIR ina mai cewa a karo na sau ba adadi, ki yi hakuri. Ki yi hakuri! Ki yi hakuri…â€.
Ko kafin ya kai karshe ya fahimci hawaye sun gangaro daga idanunta. Muryarta ba ta fita sosai. A sanda take cewa.
“Na yi hakuri Daddy, na dade da yin hakuri. Zuciyata ce ta ki daukar reality, ce min ta ke ba shi ne ya mutu ba, zai dawo. Don Allah Daddy da gaske ne??â€
Malam Raazee da Daddy Ishaq suka juyar da kai don share nasu hawayen.
Daddy ya ce, “Aalimah, wanda ya mutu ba ya dawowa. Ki yarda da ayar Ubangiji subhanahu wata’ala, kullu nafsin za’ikatul maut. Aboulkhair ba zai taba dawowa ba har abada. Ki bai wa rayuwarki da ke gaba kofa ko ya ya ne ta samu farin ciki kin ji Aalimah?â€
Daga kai kawai ta yi, don ba ta da abin da za ta yi bayan daga kan, ko ta yarda ko ba ta yarda ba, ya ce,
“Tashi je ki cikin ‘yan uwanki, Allah ya yi miki albarkaâ€.
Jiki babu lakka ta mike ta wuce cikin gida.
Bayan wucewarta da minti biyar daga Malam har dansa Ishaq babu wanda ya kara yin magana. Daga bisani Malam din yayi gyaran murya ya ce,
“Ni sai inyi ta wani tunani, a duk sanda Aalimah ta zo gabanaâ€.
Daddy ya ce,
“Tunanin mene ne Malam?â€
Malam ya girgiza kai, har da daga hannaye sama ya ce, “Uhum-um-umh-uhm, a bar kazar ‘yan boko cikin gashinta, yanzu in aka yi kokarin fige ta sai kun dawo da George Bush da Mungo Park gidan nan sabida kawo nassi na bijirewa da nuna kin amincewaâ€.
Murmushi Daddy ya yi, shi ma zuciyarsa ta yi nauyi. Babu mamaki idan ba irin tunaninsa Malam Raazee ke yi ba. Bai ja zancen da nisa ba ya yi wa Malam din sallama ya mike ya kwashi takalmansa ya fice don tafiya gidansa, wanda ba shi da nisa da gidan iyayensa trackable distance ne.
7/5/21, 8:20 AM - Buhainat: ADAMU DANKOLI
Mu’azzam ya mike daga kan abin sallarshi ya samu kujerar zaman mutum guda kusa da Kawun nasa wanda ke zaune cikin kujera ya zauna. Ya yi zurfi a tunanin da yake yi, har bai san sanda Mu’azzam ya zauna kusa da shi ba. Ajiyar zuciya ya saki lokacin da ya ji muryar nan ta Mu’azzam mai taushi da gardi a kunnuwan mai saurare na tambayarsa ko shi kadai ne?
Ya ce, “Eh, Harrison ya kawo niâ€.
“Ina Daddy da Mummy da wannan matar Daddyn mai surutu?â€
Daddy 1 yayi murmushi.
“Suna can gidanka, ga abinci ma na musamman mai surutun ta bani in kawo maka, amma su ma suna parking za su koma Boston, ashe ka damu da su ba ka nemansu?†Ya fada yana dan harararsa.
Murmushi ya yi, ya ce,
“Su ma ba sa nemana Oncle, especially Daddyâ€.
Da sauri ya katse shi, “Don sun san halinka ne, a zo dubaka ka ce an dame ka. Anya Mu’azzam ba za ka sauya hali ba? Ko kowa zai dame ka ai ban da iyaye! Zulaiha tausayi ta ke ba ni wallahi, ta damu da kai sosai, tana so ku dinga hira kuna tattauna al’amura amma ka ki ka ba ta dama, ina amfanin kadaici? Wane jin dadi ka ke samu a cikinsa?
Mai share musu wannan hawayen yau babu shi a doron kasa! Ina sake gaya maka Mu’azzam dole ka canza, ba aggressive tendency ba ko kai ka fi kowa zafin zuciya a duniya dole ka bude zuciyarka yanzu ka kaunaci mutanen dake zagaye da kai, ka rungume kannenka da iyayenka, ka ba su kulawa da farin cikin da mutum biyu za su ba su, in ba haka ba ka shirya gamonka da Allah ka ji na gaya maka.
In ma da lalura to da hali! Halin ka ne Mu’azzam rashin son mutane. Kai yanzu matsayin uba ka ke ga kannenka bakidaya, ba su Basma kadai ba har da su Aalimah. Don ba su da wanda ya fi ka.
Wanda ke sa su farin cikin yana mantar da su kai da wanzuwarka Allah ya yi ikonSa a kanshi, sabida kai din da baka son su kai yake so ka rayu tare dasu. Kuma dole mu karbi hukuncinsa da kyakkyawar zuciya. Ni na tafi, ka yi tunani a kan maganganu na da kyau. Allah ya kara maka lafiyaâ€.
Ya mike ya fita, bayan ya sunkuya ya sumbaci Mu’azzam din a goshinsa. Bin bayansa ya yi da kallo yana dan dingisawa akan kafar robarsa kamar mai son tashi ya bishi, yana mai tauna kowacce kalma da ke fitowa daga bakinsa, yana mai yarda da ita cikin aminci da gaskatawa. He must be a changed man, amma ta yaya? Shi kansa bai sani ba.
Kawu Mansur na nufin ya dauki dukkan halayen Aboulkhair ya yafa yanzu, wanda ba abu ne mai sauki a gare shi ba. Aboulkhair is what he is kawai, charming, jovial, cheerful and passionate. Yana bukatar wanda zai taimaka masa hakan ta kasance da shi shima. Gashi kuma bazai iya rayuwa da kowa cikin gidan sa bayan Aboulkhair ba. Kenan wannan canjin da Kawu Mansur ke masa fata ba abu ne mai sauki a gare shi ba.
Shi kam abin tausayi ne, shi kadai aka yiwa mutuwa haqiqa. With Aboulkhair aside things are always easy for him. Ba tare da shi ba bai san yaya rayuwa zata koma masa ba. Yanzu in ya bar asibiti bai san ta yaya zai fuskanci sabuwar rayuwar ba. Rayuwar da babu Aboulkhair a cikin ta. Yana rokon Allah ya bashi juriya da karfin gwiwar karbar rayuwa a duk yadda ta zo masa.
******
Daddy Mansour ya koma Niamey ya tadda iyalinsa da sabuwar kafarsa ta roba cike da ikhlasi, kada ku so ku tona farin cikin da iyalin Raazee suka kasance a ciki. Kwana daya, biyu, uku ya huta ya ce zai koma Nigeria don komawa bakin aikinsa, kafar ta zauna masa sosai wadda ba za ka taba zaton ba ta gaske ba ce, ban da dan dingisawa da yake yi in yana tafiya.
Aboubacar da Basma tuni sun wuce. Malam Raazee da Inna Kasisi suka ce su yi ta tafiya tunda sun ga cewa zama a kasashen da ba su da kowa shi ya fi musu, amma su bar musu Aalimah.
Ita ma Aalimah ko da Mama ta tuntube ta da zancen ta fi son zaman Yamai din a kan komawa Nigerian. A cewarta za ta kasance cikin kadaici in ta koma wanda shi ne babban abin da ke jefa ta cikin kewa da tunanin mijinta Aboulkhairi.
Daddy 1, Mama Asi da ‘yammatansu uku; Sultana, Suhaima da Sabrina suka taho gida cike da alhinin halin da suka baro Aalimah a ciki.
Aalimah idan ta yi wanka da safe shi ke nan ko vaseline ba ya ganin fatar jikinta, balle kuma kwalli abin adon mata a idanunta. Hakika mutuwar Aboulkhair ta zo mata unexpectedly, a lokacin da ta ke at the zenith na jin dadin rayuwar auratayya. Ya lullube ta da dukkan so da kauna, ya maida ita sarauniya a cikin mata ‘yan uwanta. Don haka har zuwa yanzu da ake neman watanni shidda da rasuwarsa ta kasa karbar reality na rashin sa da sauki. Kullum mutuwarsa da kewarsa fresh suke dawo mata.
Har yanzu ji ta ke a jikinta kamar Aboulkhair ba mutuwa ya yi ba, ya je Boston ne bada jimawa ba zai dawo ya tadda ita, ya dauke ta su koma Las Vegas, su cigaba da rayuwar nan tasu mai ban sha’awa. Amma da ta ga watanni na shurawa da gasken-gaske babu ko waiwaye har an kwashi watanni kwarara guda tara, dole ta fara karbar reality na fara sabawa da rashin sa.
A kullum Inna Kasisi da Inna Bintou cikin tattashinta suke da nuna kulawa da kyautatawa. Abinci sai wanda ta zaba za’a dafa a gidan. ‘Yan uwanta kannenta su Balkissa dasu Rumana kullum kafafunsu na dakin Inna Bintou inda Aalimah ta ke, su kwaso labarai suyi ta bata na abubuwan da ke faruwa a gari, tamkar su goya ta don lallashi da son debe mata kewa. Dole ta fara sakin ranta, amma ba don ta yarda cewa za ta kara wata rayuwar farin ciki a gaba ba. Sai don ‘yan uwa, iyaye da kakanninta su yarda ba aikin banza suke yi ba, tana karbar rarrashinsu, kaunarsu da soyayyarsu.
Hannu biyu ya sa ya karba ya ce, “Madalla da Bintou da jikanyar ta, an gaishe ku, madallahâ€.
Ta juya za ta fita, sai kuma ta dawo ta tsuguna.
“Malam Aunty Gumsu-Moiram ta yi min waya dazu tace in je in mata kwana biyu, na ce mata sai na tambaye ka tukunnaâ€.
Ya ce, “Ba yanzu ba Moiram ta yi hakkuri, bana so ki je ko’ina sai kin warware dukkanki, har yanzu ban ganki kamar yadda nasan ki ba, a bai wa Gumsu hakkuri inji niâ€.
Fuska a sake ta ce, “toh Malamâ€.
Ta juya ga Daddy ta gaishe shi cikin nutsuwa da sanyin muryarta.
Ya ce, “Anya Aalimah? Haka dan Adam zai rayu da damuwa bayan ba abin da za ta sa, ba abin da za ta hana? Dubi kasusuwan wuyanki, dubi idanunki yadda suka zuzzurma ciki. Don Allah don Annabi Aalimah ni Baban ABOULKHAIR ina mai cewa a karo na sau ba adadi, ki yi hakuri. Ki yi hakuri! Ki yi hakuri…â€.
Ko kafin ya kai karshe ya fahimci hawaye sun gangaro daga idanunta. Muryarta ba ta fita sosai. A sanda take cewa.
“Na yi hakuri Daddy, na dade da yin hakuri. Zuciyata ce ta ki daukar reality, ce min ta ke ba shi ne ya mutu ba, zai dawo. Don Allah Daddy da gaske ne??â€
Malam Raazee da Daddy Ishaq suka juyar da kai don share nasu hawayen.
Daddy ya ce, “Aalimah, wanda ya mutu ba ya dawowa. Ki yarda da ayar Ubangiji subhanahu wata’ala, kullu nafsin za’ikatul maut. Aboulkhair ba zai taba dawowa ba har abada. Ki bai wa rayuwarki da ke gaba kofa ko ya ya ne ta samu farin ciki kin ji Aalimah?â€
Daga kai kawai ta yi, don ba ta da abin da za ta yi bayan daga kan, ko ta yarda ko ba ta yarda ba, ya ce,
“Tashi je ki cikin ‘yan uwanki, Allah ya yi miki albarkaâ€.
Jiki babu lakka ta mike ta wuce cikin gida.
Bayan wucewarta da minti biyar daga Malam har dansa Ishaq babu wanda ya kara yin magana. Daga bisani Malam din yayi gyaran murya ya ce,
“Ni sai inyi ta wani tunani, a duk sanda Aalimah ta zo gabanaâ€.
Daddy ya ce,
“Tunanin mene ne Malam?â€
Malam ya girgiza kai, har da daga hannaye sama ya ce, “Uhum-um-umh-uhm, a bar kazar ‘yan boko cikin gashinta, yanzu in aka yi kokarin fige ta sai kun dawo da George Bush da Mungo Park gidan nan sabida kawo nassi na bijirewa da nuna kin amincewaâ€.
Murmushi Daddy ya yi, shi ma zuciyarsa ta yi nauyi. Babu mamaki idan ba irin tunaninsa Malam Raazee ke yi ba. Bai ja zancen da nisa ba ya yi wa Malam din sallama ya mike ya kwashi takalmansa ya fice don tafiya gidansa, wanda ba shi da nisa da gidan iyayensa trackable distance ne.
7/5/21, 8:20 AM - Buhainat: ADAMU DANKOLI
Mu’azzam ya mike daga kan abin sallarshi ya samu kujerar zaman mutum guda kusa da Kawun nasa wanda ke zaune cikin kujera ya zauna. Ya yi zurfi a tunanin da yake yi, har bai san sanda Mu’azzam ya zauna kusa da shi ba. Ajiyar zuciya ya saki lokacin da ya ji muryar nan ta Mu’azzam mai taushi da gardi a kunnuwan mai saurare na tambayarsa ko shi kadai ne?
Ya ce, “Eh, Harrison ya kawo niâ€.
“Ina Daddy da Mummy da wannan matar Daddyn mai surutu?â€
Daddy 1 yayi murmushi.
“Suna can gidanka, ga abinci ma na musamman mai surutun ta bani in kawo maka, amma su ma suna parking za su koma Boston, ashe ka damu da su ba ka nemansu?†Ya fada yana dan harararsa.
Murmushi ya yi, ya ce,
“Su ma ba sa nemana Oncle, especially Daddyâ€.
Da sauri ya katse shi, “Don sun san halinka ne, a zo dubaka ka ce an dame ka. Anya Mu’azzam ba za ka sauya hali ba? Ko kowa zai dame ka ai ban da iyaye! Zulaiha tausayi ta ke ba ni wallahi, ta damu da kai sosai, tana so ku dinga hira kuna tattauna al’amura amma ka ki ka ba ta dama, ina amfanin kadaici? Wane jin dadi ka ke samu a cikinsa?
Mai share musu wannan hawayen yau babu shi a doron kasa! Ina sake gaya maka Mu’azzam dole ka canza, ba aggressive tendency ba ko kai ka fi kowa zafin zuciya a duniya dole ka bude zuciyarka yanzu ka kaunaci mutanen dake zagaye da kai, ka rungume kannenka da iyayenka, ka ba su kulawa da farin cikin da mutum biyu za su ba su, in ba haka ba ka shirya gamonka da Allah ka ji na gaya maka.
In ma da lalura to da hali! Halin ka ne Mu’azzam rashin son mutane. Kai yanzu matsayin uba ka ke ga kannenka bakidaya, ba su Basma kadai ba har da su Aalimah. Don ba su da wanda ya fi ka.
Wanda ke sa su farin cikin yana mantar da su kai da wanzuwarka Allah ya yi ikonSa a kanshi, sabida kai din da baka son su kai yake so ka rayu tare dasu. Kuma dole mu karbi hukuncinsa da kyakkyawar zuciya. Ni na tafi, ka yi tunani a kan maganganu na da kyau. Allah ya kara maka lafiyaâ€.
Ya mike ya fita, bayan ya sunkuya ya sumbaci Mu’azzam din a goshinsa. Bin bayansa ya yi da kallo yana dan dingisawa akan kafar robarsa kamar mai son tashi ya bishi, yana mai tauna kowacce kalma da ke fitowa daga bakinsa, yana mai yarda da ita cikin aminci da gaskatawa. He must be a changed man, amma ta yaya? Shi kansa bai sani ba.
Kawu Mansur na nufin ya dauki dukkan halayen Aboulkhair ya yafa yanzu, wanda ba abu ne mai sauki a gare shi ba. Aboulkhair is what he is kawai, charming, jovial, cheerful and passionate. Yana bukatar wanda zai taimaka masa hakan ta kasance da shi shima. Gashi kuma bazai iya rayuwa da kowa cikin gidan sa bayan Aboulkhair ba. Kenan wannan canjin da Kawu Mansur ke masa fata ba abu ne mai sauki a gare shi ba.
Shi kam abin tausayi ne, shi kadai aka yiwa mutuwa haqiqa. With Aboulkhair aside things are always easy for him. Ba tare da shi ba bai san yaya rayuwa zata koma masa ba. Yanzu in ya bar asibiti bai san ta yaya zai fuskanci sabuwar rayuwar ba. Rayuwar da babu Aboulkhair a cikin ta. Yana rokon Allah ya bashi juriya da karfin gwiwar karbar rayuwa a duk yadda ta zo masa.
******
Daddy Mansour ya koma Niamey ya tadda iyalinsa da sabuwar kafarsa ta roba cike da ikhlasi, kada ku so ku tona farin cikin da iyalin Raazee suka kasance a ciki. Kwana daya, biyu, uku ya huta ya ce zai koma Nigeria don komawa bakin aikinsa, kafar ta zauna masa sosai wadda ba za ka taba zaton ba ta gaske ba ce, ban da dan dingisawa da yake yi in yana tafiya.
Aboubacar da Basma tuni sun wuce. Malam Raazee da Inna Kasisi suka ce su yi ta tafiya tunda sun ga cewa zama a kasashen da ba su da kowa shi ya fi musu, amma su bar musu Aalimah.
Ita ma Aalimah ko da Mama ta tuntube ta da zancen ta fi son zaman Yamai din a kan komawa Nigerian. A cewarta za ta kasance cikin kadaici in ta koma wanda shi ne babban abin da ke jefa ta cikin kewa da tunanin mijinta Aboulkhairi.
Daddy 1, Mama Asi da ‘yammatansu uku; Sultana, Suhaima da Sabrina suka taho gida cike da alhinin halin da suka baro Aalimah a ciki.
Aalimah idan ta yi wanka da safe shi ke nan ko vaseline ba ya ganin fatar jikinta, balle kuma kwalli abin adon mata a idanunta. Hakika mutuwar Aboulkhair ta zo mata unexpectedly, a lokacin da ta ke at the zenith na jin dadin rayuwar auratayya. Ya lullube ta da dukkan so da kauna, ya maida ita sarauniya a cikin mata ‘yan uwanta. Don haka har zuwa yanzu da ake neman watanni shidda da rasuwarsa ta kasa karbar reality na rashin sa da sauki. Kullum mutuwarsa da kewarsa fresh suke dawo mata.
Har yanzu ji ta ke a jikinta kamar Aboulkhair ba mutuwa ya yi ba, ya je Boston ne bada jimawa ba zai dawo ya tadda ita, ya dauke ta su koma Las Vegas, su cigaba da rayuwar nan tasu mai ban sha’awa. Amma da ta ga watanni na shurawa da gasken-gaske babu ko waiwaye har an kwashi watanni kwarara guda tara, dole ta fara karbar reality na fara sabawa da rashin sa.
A kullum Inna Kasisi da Inna Bintou cikin tattashinta suke da nuna kulawa da kyautatawa. Abinci sai wanda ta zaba za’a dafa a gidan. ‘Yan uwanta kannenta su Balkissa dasu Rumana kullum kafafunsu na dakin Inna Bintou inda Aalimah ta ke, su kwaso labarai suyi ta bata na abubuwan da ke faruwa a gari, tamkar su goya ta don lallashi da son debe mata kewa. Dole ta fara sakin ranta, amma ba don ta yarda cewa za ta kara wata rayuwar farin ciki a gaba ba. Sai don ‘yan uwa, iyaye da kakanninta su yarda ba aikin banza suke yi ba, tana karbar rarrashinsu, kaunarsu da soyayyarsu.