Sashe 31
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
A can kasar America kuma Abulkhair ya kira wayar Aalimah a karshen satin kamar yadda ya saba, inda gidan wayar Verizon wareless suka tabbatar masa ba’a amfani da layin, ya kira na Basma shi ma haka, sannan na Khaleesat, shi din ma dai babu. Tsoro da fargaba har ma da mamaki suka kama shi, musamman da ya gwada na Daddy shi ma haka. Wuninsa guda yana abu daya, amma ya kasa samun kowannensu. A karshe ya gwada na Mummy. Cikin sa’a sai ya same ta. Ya tambaye ta ko me ya samu wayoyin Daddy da na su Basma ya kasa samunsu? Nan take gaya masa ai suna Nijar yau satinsu daya. Ya ce ta ba sh lambar da ta ke magana da su.
Tsaki ta yi, ta ce, ita tunda suka tafi ba su yi waya ba, ba ta da lokacinsu. Ya san halin Mamanshi sarai in ya ci gaba da damunta, za su yi ta ba dadi, dole ya hakura, a kalla hankalinsa ya kwanta tunda lafiyarsu kalau. Ya ci gaba da rubuta jarrabawarsa cikin nutsuwa. Sai dai fa Aalimah na ciki kowanne bugun numfashinsa, tafiyar tasu ta tabbatar masa Daddy (takes the first step) ga gyaran rayuwarsa da iyaye da ‘yan uwansa.
Ana saura kwana uku su tafi Inna Kasisi ta kira manyan ‘ya’yanta da na Bintou maza, da shi Daddyn a babban falon Malam Raazee, shi ma Malam din yana zaune. Cewa ta yi Malam ya bude taron da addu’a, akwai damuwa a fuskar Daddy Ishaq don har zuwa lokacin Innar ba ta gama sake masa sosai ba. Kuka Inna Kasisi ta saka wani abu da ta dade ba ta yi shi ba, mace ce mai taurin zuciya kwarai da nuna ba ta da damuwa a kan komai, ko da tana da damuwar. Hankalin manyan ‘ya’yanta ciki har da Daddy ya yi matukar tashi. Lallashinta suka shiga yi suna rokon ta fada musu damuwarta, sun yi alkawarin magance mata ita muddin ba ta fi karfinsu ba. Sai da ta yi mai isarta, sannan ta ce, ba ta yarda Ishaq ya koma Amurka ba, ko dai ya kara aure ya bar matar a nan tare da su, shi ya koma din inyaso ya dinga zuwa in ya samu sarari, ko ya baro Amurka bakidaya ya zo ya zauna cikin ‘yan uwansa tare da iyalinsa.
Zufa ce kawai ta lullube Daddy, saboda cikin zabin nata duka babu mai sauki. He has a life where he live, a career, a family and everything. Ko zai baro Amurka ba lokaci daya ba. Zabinta na biyu kuma karin aure wani karin nauyi ne a gare shi da bai san yadda zai yi ya dinga sauke shi ba.
Bai ma taba hasaso wa kanshi irin wannan rayuwar ba (polygamy), duk da ita ya taso ya tarar a gidansu. Shirunsa ya sanya kowa da ke dakin ma ya yi shiru, ita kuma Inna ta ci gaba da sharbe. Malam ya yi gyaran murya don katse shirun, ya ce,
“To Ishaqu ka ji bukatar mahaifiyarka a kanka, wannan karon ina bayanta, kullum na kasance cikin bin ra’ayinku in dai bai saba wa addini ba, ina hana ta nata hakkin na uwa. Ka kara aure matar ta zauna da mu, ko ka dawo gidaâ€.
Da kyar Daddy ya iya hadiyar miyau, sannan ya muskuta, “Malam da Inna na ji batunku. Da man kowanne bakon haure a kasashen ketare dole watarana zai dawo gida. Ina da wannan niyyar ko Inna ba ta furta ba, amma ba zai yiwu a lokaci daya ba. Duka yaran karatu suke yi ba su gama ba, Mu’azzam ne kadai ya tsaya da kafafunsa.
Ni kuma sai ya kasance ina da abin yi a nan din kafin in dawo, don ba zai yiwu in zo in zame muku lalura ba. Magana ce ta WATARANA da babu wanda ya san wace rana ce. Maganar karin aure kuma Inna ni yanzu tsofai-tsofai da ni wane aure zan kara?
Gidana babu ko dakin ajiye mace, in kuma na ce a nan zan ajiye ta yanayin aikina ba zai bari in dinga zuwa akai-akai ba, zai zama akwai zalunci a ciki ta fannin matar. Inna ko za ki fadi wata alfarmar in yi miki bayan wannan?†Ya fada cikin taushin murya mai cike da ladabi da kwantar da kai, hadi da lallashi.
Amma budar bakin Inna kasisi sai cewa ta yi, ita ta riga ta gama magana, har ta tanadar masa matar, ta ji ta yarda ba zai iya dawowa Niamey yanzu ba, amma dole ya auri GUMSU!
Wata sabuwa inji ‘yan caca, shuka tsakiyar rani!
6/28/21, 7:33 AM - Buhainat: &&&&&&&&&&
****************************************************************************
17
Tsaki ta yi, ta ce, ita tunda suka tafi ba su yi waya ba, ba ta da lokacinsu. Ya san halin Mamanshi sarai in ya ci gaba da damunta, za su yi ta ba dadi, dole ya hakura, a kalla hankalinsa ya kwanta tunda lafiyarsu kalau. Ya ci gaba da rubuta jarrabawarsa cikin nutsuwa. Sai dai fa Aalimah na ciki kowanne bugun numfashinsa, tafiyar tasu ta tabbatar masa Daddy (takes the first step) ga gyaran rayuwarsa da iyaye da ‘yan uwansa.
Ana saura kwana uku su tafi Inna Kasisi ta kira manyan ‘ya’yanta da na Bintou maza, da shi Daddyn a babban falon Malam Raazee, shi ma Malam din yana zaune. Cewa ta yi Malam ya bude taron da addu’a, akwai damuwa a fuskar Daddy Ishaq don har zuwa lokacin Innar ba ta gama sake masa sosai ba. Kuka Inna Kasisi ta saka wani abu da ta dade ba ta yi shi ba, mace ce mai taurin zuciya kwarai da nuna ba ta da damuwa a kan komai, ko da tana da damuwar. Hankalin manyan ‘ya’yanta ciki har da Daddy ya yi matukar tashi. Lallashinta suka shiga yi suna rokon ta fada musu damuwarta, sun yi alkawarin magance mata ita muddin ba ta fi karfinsu ba. Sai da ta yi mai isarta, sannan ta ce, ba ta yarda Ishaq ya koma Amurka ba, ko dai ya kara aure ya bar matar a nan tare da su, shi ya koma din inyaso ya dinga zuwa in ya samu sarari, ko ya baro Amurka bakidaya ya zo ya zauna cikin ‘yan uwansa tare da iyalinsa.
Zufa ce kawai ta lullube Daddy, saboda cikin zabin nata duka babu mai sauki. He has a life where he live, a career, a family and everything. Ko zai baro Amurka ba lokaci daya ba. Zabinta na biyu kuma karin aure wani karin nauyi ne a gare shi da bai san yadda zai yi ya dinga sauke shi ba.
Bai ma taba hasaso wa kanshi irin wannan rayuwar ba (polygamy), duk da ita ya taso ya tarar a gidansu. Shirunsa ya sanya kowa da ke dakin ma ya yi shiru, ita kuma Inna ta ci gaba da sharbe. Malam ya yi gyaran murya don katse shirun, ya ce,
“To Ishaqu ka ji bukatar mahaifiyarka a kanka, wannan karon ina bayanta, kullum na kasance cikin bin ra’ayinku in dai bai saba wa addini ba, ina hana ta nata hakkin na uwa. Ka kara aure matar ta zauna da mu, ko ka dawo gidaâ€.
Da kyar Daddy ya iya hadiyar miyau, sannan ya muskuta, “Malam da Inna na ji batunku. Da man kowanne bakon haure a kasashen ketare dole watarana zai dawo gida. Ina da wannan niyyar ko Inna ba ta furta ba, amma ba zai yiwu a lokaci daya ba. Duka yaran karatu suke yi ba su gama ba, Mu’azzam ne kadai ya tsaya da kafafunsa.
Ni kuma sai ya kasance ina da abin yi a nan din kafin in dawo, don ba zai yiwu in zo in zame muku lalura ba. Magana ce ta WATARANA da babu wanda ya san wace rana ce. Maganar karin aure kuma Inna ni yanzu tsofai-tsofai da ni wane aure zan kara?
Gidana babu ko dakin ajiye mace, in kuma na ce a nan zan ajiye ta yanayin aikina ba zai bari in dinga zuwa akai-akai ba, zai zama akwai zalunci a ciki ta fannin matar. Inna ko za ki fadi wata alfarmar in yi miki bayan wannan?†Ya fada cikin taushin murya mai cike da ladabi da kwantar da kai, hadi da lallashi.
Amma budar bakin Inna kasisi sai cewa ta yi, ita ta riga ta gama magana, har ta tanadar masa matar, ta ji ta yarda ba zai iya dawowa Niamey yanzu ba, amma dole ya auri GUMSU!
Wata sabuwa inji ‘yan caca, shuka tsakiyar rani!
6/28/21, 7:33 AM - Buhainat: &&&&&&&&&&
****************************************************************************
17