← Book details Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 28

Sashe 6

Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yayi
dan tsaki,umma na gaji da auran nan ina ga
wannan karan xan yar da qwallon mangwaro in
huta ta quda. umma ta ce abba! abba!! me yasa
baka da haquri? ban xace ka haka ba abba,ina ce
jiyannan ka min alqawarin kawo qarshen duk
wata matsala tsakaninka da matanka?shin ban
fada maka hanyoyin da xaka bi ka xauna da
matarka lfy ba?ya kamo hannun ta,umma ba na
san bata ranki, ban san yadda xanyi da halin
yarinyan nan ba ne. jiya fa ina kwance taxo tace
min yarona amai naje kai shi kyamis,ina dawowa
na samu ta xauna tana kallon,ina mata magana
ta hayayyaqo min da asuba na tashe ta
sallah,wai dan yayi kashi shine ta hau xagin
yaron nan,wai dan iska. ni ko na bige mata baki
har da cukume ni da dambe fa.umma tace kaine
harda duka abba? dukan mace?ta xuba tagumi
tana kallon shi,ya ce umma xaginshi fa tayi,kuma
kin san dai ba kyau uwa ta dinga xagin danta.dan
ba haka kikai min tarbiyya ba.kalli rashin ji irin na
ummi, amma ban taba jin kin ce mata yar iska
ba.tace to ba sai ka xaunar da ita cikin tsanaki
ba?? .

Yayi shiru a xuciyarshi fadi yake umma ba
xata fahinta ba.tace, tashi kaje ka bata haquri, ka
lallasheta.matafa sai haquri,kasan da qashin
haqarqari aka yi su,dole ka ganta a karka
ce.saidai nasiha da lallashi,da xaran ka ce kan
dole xaka miqar da ita,sai ta karye.nan dai ta yi
ta ma abba fada, har sai da shi kanshi yaga
cewa eh,yayi saurin fushi.dan haka ya miqe ya
nufi gida da nufin bata baki.sai dai kuma kash!
lkcn da yaxo tuni tana gidansu.ya dawo ya sanar
da umma, tace to dole sai alhj yaji kenan.ta shiga
gun alhj yana shirin fita. yace yau dai suwaiba
akwai abin da ya dauke miki hankali daga kaina
ko? tace, me kagani? yace tunda kika fita ban
kuma jin duriyarki ba, hatta karin kumallo yau
uwata ce ta kawo min.ko taya ni shafa mai yau
ban samu ba, tace uhum, abba ne in gaya maka
na gani hankalinshi a duk tashe, matsala ce suka
samu da matarshi,wai ta yi yaji.alhj yace,yaji?
umma tace eh wai a ce kamar abba bai san
yadda xai yi haquri da mace ba, alhj yace ina
abban?ta ce yana daki yana karya wa.

Ya ce kira
min shi.abba ya xauna ya xayyane ma alhj komai
duk abubuwan da ke faruwa wanda take
masa,hatta batun sallah da bata san yi duk ya
fadia.alhj yayi shiru,can ya ce in ko haka ne ba
qaramin haquri kake yi ba, amma kaje xamu je
gidan.abba ya ce, ni dama xa a baita can dana
huta.alhj yace ba xa ayi haka ba haquri dai xa ka
ci gaba da yi.xuwan su alhj biyu gidan amma ba
suyi dace ba ance musu mahaifinta baya nan.
antynta kuwa ta kira shi a waya ya ce yana nan
xuwa gidanta.da dare suka je da ahmad sun
same ta ita da mijnta,anty ta tare su cikin fara'a
aka kawo musu kayan shaye shaye.nan dai abba
ya fada mata komai.ya qara da cewa ban sani ba
ko dan ni talaka ne shi yasa bishira bata ji
maganata? anty tace dame ka gaxa mata?
iskancintane kawai, wai bishira har da rashin
sallah,xa ko taci qaniyarta gun alhj.mijin anty
yace,tabdi lalle kana haquri nan dai suka ci gaba
da hira har mijin antyn yayi mishi alqawarin cewa
ya kawo takardunshi.MD din gidan rediyon
tarayya na jihar kd, amininshi ne.

Amininshi ne
tun da abn da ya karanta kenan za a sama mishi
aiki.Abba ya yi ta godiya.

Bai san da wane baki
zai gode ma mijin anty ba,tun daga nemna auran
Bishira yake taimakoshi, darajar su shi da Anty
da Alhjn su Bishiran yake hkr da halayanta.

Ya zo
ya sanar da su Umman,Sun yi murna hr Alhj ya
ce dole ne in in masa godiya.

Umma ta ce To
Abba ka gani fa,ta dailin matarka gashi zaka
samu aiki,ka yi ta hkr fa.

Abba ya ce Umma ba fa
ta dalilinta ba,in Allah ya rubuto zan samu ta
hanyarshi sai ki gani,ko ban santa ba Allah ya
kawo sila.Ta ce To yanzun dai ita ce Silar,Allah
yasa albarka.Sai dai ba zan ji dadin tafiyarka
garin Kd ka barni nan ba.

Ya ce Umma ko ni
tunda ya ce kd ke kurum ni ke tunan.Umma tayi
Murmushi,Allah ya maka za6i na alkairi,dk in da
za ka je.Amin Ummata.

Mahaifin Bishira ya dawo
kuma Alhj ya tasa Abba sun je in da aka kirata
gata ga shi ga kuma iyayensu.

Abba ya jero duk
laifunkanta bai rage ko daya ba.

Sannan ya ce,shi
ma yana son ta fadi tsakani ga Allah me yake
mata wanda ba ta So?Nan fa a ka ce ta fadan,
sai ta shiga Kame-kame, Wai in ya shigo gida sai
ya yi ta fadace-fadace sannan ba ya zama a gida
sai tayi bacci,km ga abnci ta dafa amma sai ya
amso na Ummarshi ya c.

Alhjnta ya daka mata
tsawa."Yi min shiru,yaushe ki ka bar musulunci?

Ba kya sallah ko?sannan ki bude baki kina zagar
masa da a gabansa?Ya bige miki baki kin kwaso
kin taho gida,to a miki uban me?ya dubi Abba
"Idiris me yasa ma ka mata duka ba?Ai ke babu
abn da ya dace da ke irin duka.

Maza ki kakkabe
mayafinki ki koma gidanki,bana son in sake
ganinki da sunan yaji a gidana, .

Zan wulakanta
ki.

Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi
ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa
kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da
tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan
biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn
Alhjn Su Abba ya yi magana.

Hakuri za ka yi
ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa
karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za
su sake ba.

Abba ma ya yi godiya,sannan suka
masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana
kuka suka tafi.

Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a
kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin
zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta
fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci.

Ya
kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya
tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da
ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran.

Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu
ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar
nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada
ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan
shi ne adalci.

Bayan sun dawo Abba ya rakata
gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana
jiranshi.

Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara
tayi to ya kansace a gida.

Sannan fadan da ta ce
yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya
dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma
ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara
masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi
ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar
Islamiya tunda da ita a kusa.

Ya shiga ya same
ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna
kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan
ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba
ya ci gaba da mgn.

Kin san dai ina sonki ko??ta
dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga
ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba.

Ya yi
tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya
danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki
fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr
akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na
yafe miki. .

Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina
sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son
wannan kalma daga mazajensu.

Ya kira sunanta
ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya
fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara
mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar
dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta
farko da suka soma kwana a dakin nasa.

Washe
gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share
gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su
sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi
sallah ta yiwa yaro wanka.

Tayi Sallar,wankan ta
kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga.

Ya ce,To
t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya
fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito
da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana
kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima
sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. .

Ya cire
kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado
wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka
bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi.

Ya kira ta ya
ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya
dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan
iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to.

Nan ta
samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce
Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce
Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta.

Don Allah
ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka
tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce.

Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun
dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka
sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago
bai je ba.

Cikin satin dai babu laifi suna ta
shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar
jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai
dai ita gani take dk an takura mata,amma tana
jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar
farkonauresu.

Mitar da take masa kullum ya
daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a
gida suyi hira.

Ranar dai saiya gwada zama tun
da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida.

Tana
zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki
sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in
ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan
baki. .
Chapter 6 · 0% Book details