Sashe 20
Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fati ta yi ta dariya
tare da cewa, "Ke yanzun sai ki iya wa Ummanku
wannan zance?" Ummi ta ce, "Sosai ma".
Fati ta
ce, "Ko ba ki sha ba yarinya sai kin sha zafi, ana
kawo ni ko dan kwana daya bai raga min ba".
Ummi dai ido ya raina fata.
Koda Abba ya zo
daukarta duk ta damu. ** ** 44.....
Tasalla ta
samu uwar Sahabi ta fada mata cewa, in dole ne
sai danta ya auri Ummi, to ta amso mishi karya
tambaya.
Don kuwa wata rana sai ta taso ta
ganshi ko da a hanya ne ta rasa samun hakan.
Inna ta tsure ta ce, sai a fasa babu dole, ita
dama tuni abin ya sire mata.
Ana gobe daurin
aure gidan su Ummi suna ta shiri Ummi na ta
kuka, wannan karon ba Umma ba har Alhaji da
Tsohuwa sun kule da wannan iskancin da Ummi
ke yi.
Alhaji ya ce "Ki sani uwata, wannan karon
ko kin tsokalo ciwon nan naki auren nan dole ne
babu fashi.
Idan yaso jinin naki ya tashi ya ta6o
sama ba zan kuma daga auran nan ba".
Lokacin
da Alhaji ke wannan fadan Abba yana gidan yana
zaune dakin Umma yayin da Ummi ke gefanshi
tana rusa kuka.
Umma ta shigo ya ce "Umma
don Allah ki lallashi Alhaji a dan daga bikin nan
mana".
Abba bai ta6a ganin ranar da Umma tayi
mishi irin wannan kallon da ta masa yanzu ba
tun tasowarshi.
Sannan bata ta6a daka masa irin
wannan tsawar ba ta ce "Kai!
Abba shiga
taitayinka, me yasa yanzun ka canza, ko kai ba
za ka hukunta Ummi ba da irin wannan yaro da
hankalin da take mana?
Don gidansu kanta a ka
soma aure?
To wannan karon ba za a daga bikin
ba, in yaso ta mutu, ke ko mutuwa ki ka yi
gawarki can gidan mijinki za a je a miki sutura".
Tsohuwa ma daga can tana yo nata fadan tare da
dauko tarihe-tarihen da tana cewa, "Lokacinsu
kaza-kaza".
Abba ya sake kallon Ummi,
matsanancin kukan da take yi yana daga mishi
hankali, ya mike tare da kama hannunta, "Zo
muje".
Ya bude mazaunin direba ya ce ta shiga,
shi ma ya koma ya shiga motar ya tasheta, tafiya
kawai suke ba tare da ya san in da suka dosa ba.
Kukan Ummi na tsikararshi, sun yi tafiya mai nisa
sannan ya tsaya a hankali cikin wata irin murya,
ya ce "Ummi ki fada min gaskiya kina son
Sahabi?" Ta dago ta dube shi, "Ni bana son shi".
"To me yasa ki ka fito da shi?" cikin dasasshiyar
murya ta ce, "Ba ni da yanda zan yi ne, saboda in
ban za6i Sahabi ba za a bani Bashir".
Ya ce, "To
ke yanzun fada min wa ki ke so?" Gabanshi ya
shiga faduwa don tsoron kada kunnenshi ya ji
mishi ta ce wani ba shi ba.
Ta kuro shi da ido
tamkar ta ce kai, amma sai take ganin in ta fada
mishi haka dan shirin da suka soma yanzun zai
wargaje, kila ma sai ya hada mata da duka.
Wasu
zafafan hawaye suka gangaro kan kumatunta,
daidai lokacin da yake cewa "Ko dan digo ki ka ji
son ko waye a ranki kada ki rufe min". 45...
Ta
girgiza kai "Ba na son kowa Ya Abba".
Cikin wani
irin yanayi ya dubeta, "Shi kenan, sai ki je ki
hakura da Sahabin a sannun kin so shi".
Cikin
kuka ta ce, "Ya Abba Allah ni bana son shi, kai to
ka hada ni da ko waye mana".
Ranshi 6ace ya
dubeta cikin tsawa ya ce, "Ki rufa min baki tunda
ba ki ta6a son kowa ba ki zauna da wanda ki ka
za6i zama da shi.
In da kina son wani ne to da
sai in cije in tunkari su Alhaji, tunda kuwa babu
sai in ce musu me?" Ya fada mota, ya koma kofar
gidan.
Koda ya tsaya tafi minti uku sannan ta
fito, yana kallonta maimakon ya wuce gida sai
kawai ya nufi gidan Maman Iman makociyarsu da
suke shiri da ita.
Shima kanshi na kan sitiyarin
motar har ttsawon shudewar wasu dakiku,
sannan ya nufi gida. 27.
Misalin karfe tara
Umman Bashir ta rangada sallama a tsakar gidan,
Innar su Sahabi ta amsa tare da fadin "Shigo".
Sahura ta shiga tana tambayar "Ba kowa dai ko?"
Inna ta ce "Shigo mu kadai ne".
Bayan sun gaisa
ta ce "Ba ki sanni ba ko?" Inna ta ce, "Eh."
Sahura ta ce, "To ni dai tsakani ga Allah zuwa
nayi in ba ki shawara bisa ga yarinyar da danki
zai aura.
Tsakani ga Allah yarinyar ba ta da
mutunci, sannan iyayenta za su mallake miki da,
don ni kaina ya faru da ni".
Sahura don makirci ta
soma rishin kuka.
"Dana maigidana ya ba su riko,
ina sheda miki wannan zance 'yar uwa yanzun
tsakanina da shi sai ido, sun makkale shi komai
shi yake musu, ni ko da nayi wahalar ciki da
nakuda sai na tashi a banza.
To da yake an ce
ciwon 'ya mace na 'ya mace ne, shi ne nazo in
sanar da ke.
Amma in kin ji haushi kiyi hakuri".
Ta yunkura zata mike. 46...
Inna ta ce, "Zauna
'yar uwa, na gode.
Nima fa tuni auran nan ya fice
min a rai, dama da naga shi Sahabin ya dage ne
sai kuma suka aiko gobe azo za a daura aure sai
na hakura".
Kafiin Sahura tayi magana sai Sahabi
ya doka sallama, Inna ta ce "Yauwa zo nan".
Ya
nufo ta "Zauna kaji ma kunnenka".
Ya rage
tsawo, Inna ta ce "Baiwar Allah ya ki ka ce?" Nan
Sahura ta soma zuga sharri, ta kara da cewa
"Yaro ina ga ma za ka san dan nawa da suke riko
Abba a ke ce masa".
Cikin saurin baki ya ce, "Na
san shi".
Ta ce, "To dana ne da asiri suka amshe
min shi, sai dai Allah ya isa".
Ya tuna irin halayen
da Abban ke nuna mishi.
Yaa jinjina kai, sannan
ya dubi mahaifiyarshi "Inna to da Kawu yayo
binciken halayan iyayenta ai ana ta yabon
halinsu".
Inna ta ce, "Kin ji shi ko?
To bari kaji,
kwanaki ma Tasalla da ke bayan layin nan tazo
ta fadan irin wannan matsalar ban kama ba ne
don na asanta da shegiyar karya.
To kuwa an yi
biyu ba zan bari ai na uku ba, don haka a daran
ta tabbatar ma da danta an fasa gobe ya wuce
gurin Badariyya a daura, su kuma in sun ji shiru
sa ba wani can".
Cike da murna Sahura ta koma
gida. * Maman Iman tayi lallashin duniya amma
Ummi ta ki yin shiru, ga zazza6i tamkar wuta a
jikinta.
Sai kusan sha dayan dare sannan Maman
Iman ta rako ta gida, lokacin Umma tana ta
neman layin Abba a kashe.
Ta ce, "A'a sun dawo
ne yanzun ni ke neman Abba in ji suna ina ne?"
Maman Iman ta ce, "Tun dazu tana gidanmu
zazza6i da ya rufe Ummin, na bata magani ta 'ki
sha". 47...
Umma ta ce "Rabu da ita kar Allah
yasa tasha, aure dai gobe babu fashim dubi irin
yanda a ka sa gidan su yaron nan wancan karon
suka kashe kudi gurin yin girki da sauransu ba a
yi bikin nan ba.
Yanzun a kuma dagawa daga
lokacin da muka samu?" Maman Iman ta ce, "Ai
ba zai yiwu ba, sai dai a bi ta da lallashi".
Umma
ta ce, "Mun daina lallashinta tunda ko mun
lallasheta aikin banza ne".
Maman Iman ta ce,
"To Allah ya kaimu gobem bari in shiga gida sai
mun shigo aiki da safe".
Umma ta ce, "To sai da
safe".
Ummi tana shiga dakin Umma taga baki
kwakkwance, ta ce a ranta "Mayu, don kalata sai
da wasu suka dada zuwa".
Tana fushi da
tsohuwa amma duk da haka dakin ta nufa, ta
kwanta a bayanta don ita tuni tayi bacci.
Nishin
kukanta ya farkar da Tsohuwar, kala bata ce
mata ba, sai sauka tayi ta shimfida a kasa ta
kwanta, sannan ta ce "Aniyarki ta biki Takwara".
Wannan dare gurin Ummi da Abba wani dare ne
mai cike da bakin ciki da tashin hankali, ko Sarkin
sata bacci ranar bai samu galaba gare su ba.
Dukkan su a kan kunnansu aka kira sallar farko,
Abba ya mike cikin rangaji, jin jikinshi yake yi
tamkar iska ta dauke shi saboda rashin karfi.
Ruwa ya diba ya watsa, wanka sannan yayo
alwala don yin nafila, addu'a yake Allah yasa
hakan shi ne mafi alkairi a gare shi.
Da ya dawo
Masallaci kwanciya yayi amma baccin ya ki bai
fita ba sai kusan takwas.
Koda yaga Bishira
zaune a tsakar gida tana karatun littafin sam bai
ji haushin rashin zuwanta gidan su Umma ba.
Nashi ganin duk wanda yaje tamkar yana murna
ne da rasa Umminshi da yayi, ita kuwa da gadara
ta fito don ya ji haushi, bata je ba yana son sanin
halin da Ummi take ciki amma ba ya ra'ayin
zuwa gidan su Umma.
Shagonshi ya bude ya
shiga ya dan zauna har zuwa tara, yana kallon
lokacin da Jama'a suka yi ta dafifin shiga layinsu
don halartar daurin auran.
Kurum sai ya samu
kansa da tare dan Aca6a ya hau ba tare da ya
shaida masa inda za su ba.
Koda dan Aca6an ya
tambaye shi ce masa ya yi mu je. 48....
Ita ko
Ummi ranar zaune tayi sallah ta koma ta kwanta,
duk kaikawon ai da 'yan shewe-shewen da jama'a
dangi da makota tana jin su.
Sai dai makoshinta
ya bushe ga zufa da ta rufeta, duk da yanayin ba
na zafi ba ne.
Karfe goma daidai shi ne lokacin
daurin auran, layin ya dinke da jama'a, Alhaji
ranshi a dame don bai ga Abba ba.
Ya kalli Alhaji
Karami, "Ina Abba ne?" Alhaji Karami ya ce,
"Abokan aikinshi ga su can sun zo ba a ganshi ba
son daukan daurin auran".
Alhaji ya ce, "Su dauka
mana nasan yana nan tafe".
Har sha daya ana ta
jiran 'yan gidan Ango shiru, su Alhaji suka tashi
dan aike gidan don a ce ana jiran wakilan ango.
tare da cewa, "Ke yanzun sai ki iya wa Ummanku
wannan zance?" Ummi ta ce, "Sosai ma".
Fati ta
ce, "Ko ba ki sha ba yarinya sai kin sha zafi, ana
kawo ni ko dan kwana daya bai raga min ba".
Ummi dai ido ya raina fata.
Koda Abba ya zo
daukarta duk ta damu. ** ** 44.....
Tasalla ta
samu uwar Sahabi ta fada mata cewa, in dole ne
sai danta ya auri Ummi, to ta amso mishi karya
tambaya.
Don kuwa wata rana sai ta taso ta
ganshi ko da a hanya ne ta rasa samun hakan.
Inna ta tsure ta ce, sai a fasa babu dole, ita
dama tuni abin ya sire mata.
Ana gobe daurin
aure gidan su Ummi suna ta shiri Ummi na ta
kuka, wannan karon ba Umma ba har Alhaji da
Tsohuwa sun kule da wannan iskancin da Ummi
ke yi.
Alhaji ya ce "Ki sani uwata, wannan karon
ko kin tsokalo ciwon nan naki auren nan dole ne
babu fashi.
Idan yaso jinin naki ya tashi ya ta6o
sama ba zan kuma daga auran nan ba".
Lokacin
da Alhaji ke wannan fadan Abba yana gidan yana
zaune dakin Umma yayin da Ummi ke gefanshi
tana rusa kuka.
Umma ta shigo ya ce "Umma
don Allah ki lallashi Alhaji a dan daga bikin nan
mana".
Abba bai ta6a ganin ranar da Umma tayi
mishi irin wannan kallon da ta masa yanzu ba
tun tasowarshi.
Sannan bata ta6a daka masa irin
wannan tsawar ba ta ce "Kai!
Abba shiga
taitayinka, me yasa yanzun ka canza, ko kai ba
za ka hukunta Ummi ba da irin wannan yaro da
hankalin da take mana?
Don gidansu kanta a ka
soma aure?
To wannan karon ba za a daga bikin
ba, in yaso ta mutu, ke ko mutuwa ki ka yi
gawarki can gidan mijinki za a je a miki sutura".
Tsohuwa ma daga can tana yo nata fadan tare da
dauko tarihe-tarihen da tana cewa, "Lokacinsu
kaza-kaza".
Abba ya sake kallon Ummi,
matsanancin kukan da take yi yana daga mishi
hankali, ya mike tare da kama hannunta, "Zo
muje".
Ya bude mazaunin direba ya ce ta shiga,
shi ma ya koma ya shiga motar ya tasheta, tafiya
kawai suke ba tare da ya san in da suka dosa ba.
Kukan Ummi na tsikararshi, sun yi tafiya mai nisa
sannan ya tsaya a hankali cikin wata irin murya,
ya ce "Ummi ki fada min gaskiya kina son
Sahabi?" Ta dago ta dube shi, "Ni bana son shi".
"To me yasa ki ka fito da shi?" cikin dasasshiyar
murya ta ce, "Ba ni da yanda zan yi ne, saboda in
ban za6i Sahabi ba za a bani Bashir".
Ya ce, "To
ke yanzun fada min wa ki ke so?" Gabanshi ya
shiga faduwa don tsoron kada kunnenshi ya ji
mishi ta ce wani ba shi ba.
Ta kuro shi da ido
tamkar ta ce kai, amma sai take ganin in ta fada
mishi haka dan shirin da suka soma yanzun zai
wargaje, kila ma sai ya hada mata da duka.
Wasu
zafafan hawaye suka gangaro kan kumatunta,
daidai lokacin da yake cewa "Ko dan digo ki ka ji
son ko waye a ranki kada ki rufe min". 45...
Ta
girgiza kai "Ba na son kowa Ya Abba".
Cikin wani
irin yanayi ya dubeta, "Shi kenan, sai ki je ki
hakura da Sahabin a sannun kin so shi".
Cikin
kuka ta ce, "Ya Abba Allah ni bana son shi, kai to
ka hada ni da ko waye mana".
Ranshi 6ace ya
dubeta cikin tsawa ya ce, "Ki rufa min baki tunda
ba ki ta6a son kowa ba ki zauna da wanda ki ka
za6i zama da shi.
In da kina son wani ne to da
sai in cije in tunkari su Alhaji, tunda kuwa babu
sai in ce musu me?" Ya fada mota, ya koma kofar
gidan.
Koda ya tsaya tafi minti uku sannan ta
fito, yana kallonta maimakon ya wuce gida sai
kawai ya nufi gidan Maman Iman makociyarsu da
suke shiri da ita.
Shima kanshi na kan sitiyarin
motar har ttsawon shudewar wasu dakiku,
sannan ya nufi gida. 27.
Misalin karfe tara
Umman Bashir ta rangada sallama a tsakar gidan,
Innar su Sahabi ta amsa tare da fadin "Shigo".
Sahura ta shiga tana tambayar "Ba kowa dai ko?"
Inna ta ce "Shigo mu kadai ne".
Bayan sun gaisa
ta ce "Ba ki sanni ba ko?" Inna ta ce, "Eh."
Sahura ta ce, "To ni dai tsakani ga Allah zuwa
nayi in ba ki shawara bisa ga yarinyar da danki
zai aura.
Tsakani ga Allah yarinyar ba ta da
mutunci, sannan iyayenta za su mallake miki da,
don ni kaina ya faru da ni".
Sahura don makirci ta
soma rishin kuka.
"Dana maigidana ya ba su riko,
ina sheda miki wannan zance 'yar uwa yanzun
tsakanina da shi sai ido, sun makkale shi komai
shi yake musu, ni ko da nayi wahalar ciki da
nakuda sai na tashi a banza.
To da yake an ce
ciwon 'ya mace na 'ya mace ne, shi ne nazo in
sanar da ke.
Amma in kin ji haushi kiyi hakuri".
Ta yunkura zata mike. 46...
Inna ta ce, "Zauna
'yar uwa, na gode.
Nima fa tuni auran nan ya fice
min a rai, dama da naga shi Sahabin ya dage ne
sai kuma suka aiko gobe azo za a daura aure sai
na hakura".
Kafiin Sahura tayi magana sai Sahabi
ya doka sallama, Inna ta ce "Yauwa zo nan".
Ya
nufo ta "Zauna kaji ma kunnenka".
Ya rage
tsawo, Inna ta ce "Baiwar Allah ya ki ka ce?" Nan
Sahura ta soma zuga sharri, ta kara da cewa
"Yaro ina ga ma za ka san dan nawa da suke riko
Abba a ke ce masa".
Cikin saurin baki ya ce, "Na
san shi".
Ta ce, "To dana ne da asiri suka amshe
min shi, sai dai Allah ya isa".
Ya tuna irin halayen
da Abban ke nuna mishi.
Yaa jinjina kai, sannan
ya dubi mahaifiyarshi "Inna to da Kawu yayo
binciken halayan iyayenta ai ana ta yabon
halinsu".
Inna ta ce, "Kin ji shi ko?
To bari kaji,
kwanaki ma Tasalla da ke bayan layin nan tazo
ta fadan irin wannan matsalar ban kama ba ne
don na asanta da shegiyar karya.
To kuwa an yi
biyu ba zan bari ai na uku ba, don haka a daran
ta tabbatar ma da danta an fasa gobe ya wuce
gurin Badariyya a daura, su kuma in sun ji shiru
sa ba wani can".
Cike da murna Sahura ta koma
gida. * Maman Iman tayi lallashin duniya amma
Ummi ta ki yin shiru, ga zazza6i tamkar wuta a
jikinta.
Sai kusan sha dayan dare sannan Maman
Iman ta rako ta gida, lokacin Umma tana ta
neman layin Abba a kashe.
Ta ce, "A'a sun dawo
ne yanzun ni ke neman Abba in ji suna ina ne?"
Maman Iman ta ce, "Tun dazu tana gidanmu
zazza6i da ya rufe Ummin, na bata magani ta 'ki
sha". 47...
Umma ta ce "Rabu da ita kar Allah
yasa tasha, aure dai gobe babu fashim dubi irin
yanda a ka sa gidan su yaron nan wancan karon
suka kashe kudi gurin yin girki da sauransu ba a
yi bikin nan ba.
Yanzun a kuma dagawa daga
lokacin da muka samu?" Maman Iman ta ce, "Ai
ba zai yiwu ba, sai dai a bi ta da lallashi".
Umma
ta ce, "Mun daina lallashinta tunda ko mun
lallasheta aikin banza ne".
Maman Iman ta ce,
"To Allah ya kaimu gobem bari in shiga gida sai
mun shigo aiki da safe".
Umma ta ce, "To sai da
safe".
Ummi tana shiga dakin Umma taga baki
kwakkwance, ta ce a ranta "Mayu, don kalata sai
da wasu suka dada zuwa".
Tana fushi da
tsohuwa amma duk da haka dakin ta nufa, ta
kwanta a bayanta don ita tuni tayi bacci.
Nishin
kukanta ya farkar da Tsohuwar, kala bata ce
mata ba, sai sauka tayi ta shimfida a kasa ta
kwanta, sannan ta ce "Aniyarki ta biki Takwara".
Wannan dare gurin Ummi da Abba wani dare ne
mai cike da bakin ciki da tashin hankali, ko Sarkin
sata bacci ranar bai samu galaba gare su ba.
Dukkan su a kan kunnansu aka kira sallar farko,
Abba ya mike cikin rangaji, jin jikinshi yake yi
tamkar iska ta dauke shi saboda rashin karfi.
Ruwa ya diba ya watsa, wanka sannan yayo
alwala don yin nafila, addu'a yake Allah yasa
hakan shi ne mafi alkairi a gare shi.
Da ya dawo
Masallaci kwanciya yayi amma baccin ya ki bai
fita ba sai kusan takwas.
Koda yaga Bishira
zaune a tsakar gida tana karatun littafin sam bai
ji haushin rashin zuwanta gidan su Umma ba.
Nashi ganin duk wanda yaje tamkar yana murna
ne da rasa Umminshi da yayi, ita kuwa da gadara
ta fito don ya ji haushi, bata je ba yana son sanin
halin da Ummi take ciki amma ba ya ra'ayin
zuwa gidan su Umma.
Shagonshi ya bude ya
shiga ya dan zauna har zuwa tara, yana kallon
lokacin da Jama'a suka yi ta dafifin shiga layinsu
don halartar daurin auran.
Kurum sai ya samu
kansa da tare dan Aca6a ya hau ba tare da ya
shaida masa inda za su ba.
Koda dan Aca6an ya
tambaye shi ce masa ya yi mu je. 48....
Ita ko
Ummi ranar zaune tayi sallah ta koma ta kwanta,
duk kaikawon ai da 'yan shewe-shewen da jama'a
dangi da makota tana jin su.
Sai dai makoshinta
ya bushe ga zufa da ta rufeta, duk da yanayin ba
na zafi ba ne.
Karfe goma daidai shi ne lokacin
daurin auran, layin ya dinke da jama'a, Alhaji
ranshi a dame don bai ga Abba ba.
Ya kalli Alhaji
Karami, "Ina Abba ne?" Alhaji Karami ya ce,
"Abokan aikinshi ga su can sun zo ba a ganshi ba
son daukan daurin auran".
Alhaji ya ce, "Su dauka
mana nasan yana nan tafe".
Har sha daya ana ta
jiran 'yan gidan Ango shiru, su Alhaji suka tashi
dan aike gidan don a ce ana jiran wakilan ango.