Sashe 18
Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan sun gaisa ta
sake mishi gaisuwa, shi kuma ya mata bangajiya,
dama tun da aka yi rasuwar bai zo ba.
Ya ce
"Zainab ina ganin da an gama hayaniyar bikin
Ummi zan turo".
Tayi shiru bata yanke ma kanta
shawarar matsawar ya cikata da zancan Ummi
yau kam za su yi ta ta kare.
Jin tayi shiru ya ce
kina jina Ummi... ta katse shi da sauri, "Ba Ummi
nake ba Sorry Zainabu.
Ya ci gaba bakina ne ya
saba da kiran Ummi, da yake daga ni sai ita ne a
gidan.
Yanzun haka auran nan da zata yi ina cikin
tsananin kewarta...Zainab ta ce ina Idris?
Don
Allah ni na hakura ka je ka auri Ummi, Abba ya
dubeta cikin tsananin mamaki. 38..
Me ki ke
fada?
Me Salis ya sanar da ke?
Ta ce Idris duk
wanda ya san so, minti biyar in ya zauna da ku
zai san kuna tsananin son junanku kuma ni na
tambayi Salis cikinku daya?
Ya ce min A'a tun
daga nan nasan cewa ku masoya ne, ta nufi
hanyar gida, da sauri ya sha gabanta.
Zainabu
kada muyi haka da ke, wallahi auranki zan yi.
Ta
ce, "Eh ai na san aurena zaka yi, amma ba sona
ka ke ba, don Allah ban hanya sonka in zai yi
ajalina ba zan aure ka ba, ya kauce ta wuce, ya
bita da kallo har ta shige.
Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. 21.
Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin.
Bishira na zaune ta zuba
tagumi tunanin danta take, ga Abba sam baya
sakar mata fuska, ya ce "Lafiya Mamina take
kuka?" Ya shiga ya dauketa Bishira ta ce, "Rigima
cee kawai, ya nufi kan madubi inda ya hangi
pampers ya dauki guda daya ya nufi dakinshi da
ita.
Bishira ta biyo shi itama ta zauna a gefen
katifa kusa da shi, cikin sanyin murya ta ce,
"Abban Walid don Allah kayi hakuri, ya ce me a
ka yi?
Ta ce, "Gani nayi kana ta fushi, ya ce ni
bana fushi wannan kadan kenan ki ka gani daga
cikin sakacinki, na tabbata kin fini jin bakin cikin
mutuwar yaron nan.
Musamman da ki ka zama
sanadi, amma don batun yawo ni na daina miki
fada, kiyi tayi illa dai zan nemo wadda zata dinga
lurar min da gida.
Ta ce me ka ke nufi?
Ya ce
aure zan yi".
Ta doki kirji tare da fadin, "Aure?" ya
ce, "Eh".
Ta soma kuka haba Baban Walid, wane
laifi na maka da zaka yanke min irin wannan
mummunan hukuncin?
Ya ce, "Don Allah fita, ta
ce sai ka fada min dalilin yin auranka, ba za ka
bar ni in ji da rashin dana ba ko? ta mike an
zugo ka an ce kayi aure, to bisimilla.
Ta fita ta
zari mayafi tayi gidan Umman Bashir.
Abba ya
rungume 'yarshi ya yi laf a kan katifa shawara ya
yanke zai tura magabanshi gidan su Zainabu ba
tare da ya sake bi ta kan Zainabun ba. * Umma
ta leko dakin Tsohuwa, Ummi kin san na ce miki
kizo ki kwashe kayanki daga dakina ki adana su
ko?
Kin san dai yau duk na nesa za su iso, ki cire
wadanda za ki bada.
Tsohuwa ta ce, "Suwaiba
yarinyar nan ina kallonta jiya bata runtsa ba,
sannan da Asubahi a zaune tayi sallah.
Umma ta
shiga dakin warwas take a kan gado, Umma ta
tasheta zaune Ummi ciwon kai ta keya ga jiri da
ta ke gani daga zaune. 39..
Umma ta ce taso ki
dan watsa ruwa ki karya, mikewar da zata yi sai
ta sulale a kasa sumammiya, nan suka dau
salati, Toshuwa kam kuka ta saka.
Alhaji ya fito
wanka kenan ya ji Umma na salati, don haka
dakki ya shiga ya dauko waya ya kira Abba
lokacin yana kokarin shiga wanka.
Alhaji ya kira
shi, jin cewa Ummi ba lafiya zari mukullin mota
ya fito.
Sai da suka kai asibiti sannan ya lura da
silifas ya fito da jallabiyarshi ta wanka, Lkitan ma
bai zo ba lambarshi suka amsa Abba ya kira shi.
Ya duba Ummi sosai da kyar suka samu
numfashinta ya dawo, sun daura mata ruwa
sannan aka kaita wani daki.
Likitan ya ce su zo
ofishinsa, Ya kalli Alhaji ya ce, "Gaskiyar magana
yarinyar nan tana bukatar kulawarku, ciwonta
baya son sakaci.
Jininta ya hau ya wuce matakin
da zata iya samun mutuwar 6arin jiki.
Su Alhaji
suka dauki salati,, ya ci gaba da cewa yanzun dai
addu'a zamu ci gaba da yi.
Allah yasa in ta
farfado kada wata matsala ta biyo baya.
Sannan
ya basu takardar magunguna".
Alhaji ne ya amsa
don Abba fita yayi ya koma dakin da Ummi ke
kwance.
Idanu ya zub amata, sam bai san cewa
kuka yake ba, sai da Alhaji ya shigo ya dafa shi
tare da cewa, "Haba Abba ba girmanka ba ne
kuka.
Addu'a za ka yi Allah ya bata lafiya".
Ya
share hawaye.
Alhaji don Allah kada ka sanar da
Umma abinda Likitan ya ce, Alhajin ya ce ai
dama ba zan fada mata ba.
Bari in je sai tazo ga
takardar maganin inta zo sai ka siyo, ya ciro kudi
ya mika ma Abba, Abba ya ce a'a da kudi a
jikina.
Alhaji ya ce ka amsa ka kashe kudi cikin
kwanakin nan ina sane da duk lokacin da na ce
kazo ka siyo wani abu sai kawai in gan ka da shi
ban da kayan dakin da ka siya musu, Abba ya ce
ai ina da shi ne.
Bayan fitar Alhaji Abba yaja
kujera ya zauna ya zabga tagumi tare da tsura
ma Ummi ido, a zuciyarshi fadi yake ALLAH ka
tashi yarinyar nan lafiya, Allah kasa kar ko ina na
jikinta ya nakasa.
Alhaji ya fada wa Umma an ba
Ummi gado, don haka ta shirya su wuce.
Abba ya
tashi ya nufi ofishin Likitan, bayan ya kwankwasa
Lokitan ya ba shi izinin shiga, ya same shi yana
rubuce-rubuce.
Ba tare da ya dago kai ba ya ce,
"Zauna sai da ya kai aya rubutunshi sannan ya
dago kai ya kalli Abba "Ba dai mai jikin ba ce
ko?" Abba ya ce, "a'a ina son ne nima agwada
nawa jinin, Likitan ya ce kana jin jikinka ba dadi
ne?" Abba ya ce, "Eh da har yasa a dauko fayal
din Abba kuma ya tasa ya dauki abin gwaji.
Bayan ya gama ya zaunar, ya tsare Abba da ido
wai kun yi gadon ciwon nan ne?
Abba ya ce,
"A'a, Likitan ya ce, "Jininka ya hau, sai dai ba
sosai ba.
Kila don kai namiji ne kana kokarin
kauce ma abubuwa.
Zan rubuta maka magani na
sati daya, kuma ka dinga kokarin yin bacci a kalla
na wa shida kada ka dinga yawan tunani.
Kaga
kanwar nan taka, sai sa'ar gaske zata tashi
lafiya.
Ku dai cigaba da addu'a, zata yi bacci na
tsawon awa tara ko goma.
Ina son daidai lokacin
da zata farka ya kasance ta soma dora ido a kan
wanda suke shiri ko wanda ta fi so a cikin
mahaifanta ko danginta, Abba ya ce "To."
Lokacin da ya koma dakin su Umma sun zo har
da tsohuwa, nan Abba yake fada musu abinda
Likitan ya ce game da farkawa in tayi.
Koda bude
bakin tsohuwa sai cewa ta yi ai ko dai ba a bar
mai sunan Malam ba, tunda an ce wanda suke
shiri, don in taga mai sunan Malam karasawa
zata yi. * 22.
Duk da ana cikin wani hali sai da
su Alhaji suka murmusa.
Abba kam daure fuska
yayi yana kallon Tsohuwa, Umma ta ce, "Ai da ne
Tsohuwa.
Yanzun shiri suke tunda ta daina rashin
jinta".
Likitan ya shigo ya sake musu bayani
kamar yadda ya yi ma Abba, sannan ya ce su
bata guri kada zantukansu ya farkar da ita a
samu matsala.
Suka fito, Umma ta ce da Abba ya
tafi gurin aikinsa, su Alhaji ma suka fita tare da
Abba.
Fati ta je gidansu Sahabi dan uwansa yana
kankarar rake a kofar gida, inda yake saidawa ta
tambayi Sahabi.
Yaron ya ce mata ya ffita, ta ce
To in yazo kaa ce masa Ummi tana asibiti ba
lafiya, an bata gado.
Karfe uku ya iso asibitin
hankali a tashe, sun gaisa da Umma ta raka shi
dakin, hankalinshi ya tashi da ganin Amaryarshi
kwance a gadon.
Abba kam yana gurin aikinshi
amma hankalinshi na Asibiti, su Alhaji ma duk
nan suka nufo, Abba sai da yayi magriba sannan
ya shigo asibitin.
Jikinshi babu karfi, bai matsa
sai yaga farkawar Ummi ba ne saboda yasan da
gaske ba shi ne ya dace idanunta su soma arba
da shi ba, ya samu su Umma da su Alhaji.
Sahabi da abokansa duk suna gurin, ya gaida su
tare da tambayar ko ta farka?
Umma ta ce har
yanzun dai shiru.
Ya nufi cikin gurin Likitan suka
gaisa, ya ce Likita har yanzu ba ta farka ba.
Suka
jera zuwa dakin, Likiran yana cewa cikin wannan
dan takin zata farka, In sha Allahu.
Sun shiga
takin tana dan motsi suka nufi gadon Abba ya ce
Ummi.
Likitan ya daga mishi hannu alamar yayi
shiru ita kam daidai lokacin mafarkin Abba take
wai suna tafiya ya rike mata hannu sai ga
Sahabi.
Yana zuwa ya kama hannunta tana
tirjrewa, sai janta yake zai fita da ita, Abba yana
tsaye yana kallonsu.
Ita kuma sai kiran "Ya Abba!
Ya Abba!!
Take yi.
Likitan ya kara kunne gurin
bakinta ya dagowa yayi ya dube shi.
"Waye Yaya
Abba?" Abba ya ce ni ne.
Liitan ya ce, matsa
kusa, ya kama hannunta.
Ummi.
A hankali ta
bude ido.
Ya Abba!
Ya abba, zan sha ruwa, ya ce
to ya kalli likitan za ta sha ruwa, Likitan ya ce,
"A'a bari ta dan kara warwarewa tukunna.
Likitan
ya kama kafafunta ya dan matsa, sannu ko.
Ta
kalle shi, kin ji zafi?
Bata yi magana ba ya dauki
allira ya 6are ya dan soka mata a tafin kafa ta ja
kafafunta alamun taji zafi.
sake mishi gaisuwa, shi kuma ya mata bangajiya,
dama tun da aka yi rasuwar bai zo ba.
Ya ce
"Zainab ina ganin da an gama hayaniyar bikin
Ummi zan turo".
Tayi shiru bata yanke ma kanta
shawarar matsawar ya cikata da zancan Ummi
yau kam za su yi ta ta kare.
Jin tayi shiru ya ce
kina jina Ummi... ta katse shi da sauri, "Ba Ummi
nake ba Sorry Zainabu.
Ya ci gaba bakina ne ya
saba da kiran Ummi, da yake daga ni sai ita ne a
gidan.
Yanzun haka auran nan da zata yi ina cikin
tsananin kewarta...Zainab ta ce ina Idris?
Don
Allah ni na hakura ka je ka auri Ummi, Abba ya
dubeta cikin tsananin mamaki. 38..
Me ki ke
fada?
Me Salis ya sanar da ke?
Ta ce Idris duk
wanda ya san so, minti biyar in ya zauna da ku
zai san kuna tsananin son junanku kuma ni na
tambayi Salis cikinku daya?
Ya ce min A'a tun
daga nan nasan cewa ku masoya ne, ta nufi
hanyar gida, da sauri ya sha gabanta.
Zainabu
kada muyi haka da ke, wallahi auranki zan yi.
Ta
ce, "Eh ai na san aurena zaka yi, amma ba sona
ka ke ba, don Allah ban hanya sonka in zai yi
ajalina ba zan aure ka ba, ya kauce ta wuce, ya
bita da kallo har ta shige.
Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. 21.
Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin.
Bishira na zaune ta zuba
tagumi tunanin danta take, ga Abba sam baya
sakar mata fuska, ya ce "Lafiya Mamina take
kuka?" Ya shiga ya dauketa Bishira ta ce, "Rigima
cee kawai, ya nufi kan madubi inda ya hangi
pampers ya dauki guda daya ya nufi dakinshi da
ita.
Bishira ta biyo shi itama ta zauna a gefen
katifa kusa da shi, cikin sanyin murya ta ce,
"Abban Walid don Allah kayi hakuri, ya ce me a
ka yi?
Ta ce, "Gani nayi kana ta fushi, ya ce ni
bana fushi wannan kadan kenan ki ka gani daga
cikin sakacinki, na tabbata kin fini jin bakin cikin
mutuwar yaron nan.
Musamman da ki ka zama
sanadi, amma don batun yawo ni na daina miki
fada, kiyi tayi illa dai zan nemo wadda zata dinga
lurar min da gida.
Ta ce me ka ke nufi?
Ya ce
aure zan yi".
Ta doki kirji tare da fadin, "Aure?" ya
ce, "Eh".
Ta soma kuka haba Baban Walid, wane
laifi na maka da zaka yanke min irin wannan
mummunan hukuncin?
Ya ce, "Don Allah fita, ta
ce sai ka fada min dalilin yin auranka, ba za ka
bar ni in ji da rashin dana ba ko? ta mike an
zugo ka an ce kayi aure, to bisimilla.
Ta fita ta
zari mayafi tayi gidan Umman Bashir.
Abba ya
rungume 'yarshi ya yi laf a kan katifa shawara ya
yanke zai tura magabanshi gidan su Zainabu ba
tare da ya sake bi ta kan Zainabun ba. * Umma
ta leko dakin Tsohuwa, Ummi kin san na ce miki
kizo ki kwashe kayanki daga dakina ki adana su
ko?
Kin san dai yau duk na nesa za su iso, ki cire
wadanda za ki bada.
Tsohuwa ta ce, "Suwaiba
yarinyar nan ina kallonta jiya bata runtsa ba,
sannan da Asubahi a zaune tayi sallah.
Umma ta
shiga dakin warwas take a kan gado, Umma ta
tasheta zaune Ummi ciwon kai ta keya ga jiri da
ta ke gani daga zaune. 39..
Umma ta ce taso ki
dan watsa ruwa ki karya, mikewar da zata yi sai
ta sulale a kasa sumammiya, nan suka dau
salati, Toshuwa kam kuka ta saka.
Alhaji ya fito
wanka kenan ya ji Umma na salati, don haka
dakki ya shiga ya dauko waya ya kira Abba
lokacin yana kokarin shiga wanka.
Alhaji ya kira
shi, jin cewa Ummi ba lafiya zari mukullin mota
ya fito.
Sai da suka kai asibiti sannan ya lura da
silifas ya fito da jallabiyarshi ta wanka, Lkitan ma
bai zo ba lambarshi suka amsa Abba ya kira shi.
Ya duba Ummi sosai da kyar suka samu
numfashinta ya dawo, sun daura mata ruwa
sannan aka kaita wani daki.
Likitan ya ce su zo
ofishinsa, Ya kalli Alhaji ya ce, "Gaskiyar magana
yarinyar nan tana bukatar kulawarku, ciwonta
baya son sakaci.
Jininta ya hau ya wuce matakin
da zata iya samun mutuwar 6arin jiki.
Su Alhaji
suka dauki salati,, ya ci gaba da cewa yanzun dai
addu'a zamu ci gaba da yi.
Allah yasa in ta
farfado kada wata matsala ta biyo baya.
Sannan
ya basu takardar magunguna".
Alhaji ne ya amsa
don Abba fita yayi ya koma dakin da Ummi ke
kwance.
Idanu ya zub amata, sam bai san cewa
kuka yake ba, sai da Alhaji ya shigo ya dafa shi
tare da cewa, "Haba Abba ba girmanka ba ne
kuka.
Addu'a za ka yi Allah ya bata lafiya".
Ya
share hawaye.
Alhaji don Allah kada ka sanar da
Umma abinda Likitan ya ce, Alhajin ya ce ai
dama ba zan fada mata ba.
Bari in je sai tazo ga
takardar maganin inta zo sai ka siyo, ya ciro kudi
ya mika ma Abba, Abba ya ce a'a da kudi a
jikina.
Alhaji ya ce ka amsa ka kashe kudi cikin
kwanakin nan ina sane da duk lokacin da na ce
kazo ka siyo wani abu sai kawai in gan ka da shi
ban da kayan dakin da ka siya musu, Abba ya ce
ai ina da shi ne.
Bayan fitar Alhaji Abba yaja
kujera ya zauna ya zabga tagumi tare da tsura
ma Ummi ido, a zuciyarshi fadi yake ALLAH ka
tashi yarinyar nan lafiya, Allah kasa kar ko ina na
jikinta ya nakasa.
Alhaji ya fada wa Umma an ba
Ummi gado, don haka ta shirya su wuce.
Abba ya
tashi ya nufi ofishin Likitan, bayan ya kwankwasa
Lokitan ya ba shi izinin shiga, ya same shi yana
rubuce-rubuce.
Ba tare da ya dago kai ba ya ce,
"Zauna sai da ya kai aya rubutunshi sannan ya
dago kai ya kalli Abba "Ba dai mai jikin ba ce
ko?" Abba ya ce, "a'a ina son ne nima agwada
nawa jinin, Likitan ya ce kana jin jikinka ba dadi
ne?" Abba ya ce, "Eh da har yasa a dauko fayal
din Abba kuma ya tasa ya dauki abin gwaji.
Bayan ya gama ya zaunar, ya tsare Abba da ido
wai kun yi gadon ciwon nan ne?
Abba ya ce,
"A'a, Likitan ya ce, "Jininka ya hau, sai dai ba
sosai ba.
Kila don kai namiji ne kana kokarin
kauce ma abubuwa.
Zan rubuta maka magani na
sati daya, kuma ka dinga kokarin yin bacci a kalla
na wa shida kada ka dinga yawan tunani.
Kaga
kanwar nan taka, sai sa'ar gaske zata tashi
lafiya.
Ku dai cigaba da addu'a, zata yi bacci na
tsawon awa tara ko goma.
Ina son daidai lokacin
da zata farka ya kasance ta soma dora ido a kan
wanda suke shiri ko wanda ta fi so a cikin
mahaifanta ko danginta, Abba ya ce "To."
Lokacin da ya koma dakin su Umma sun zo har
da tsohuwa, nan Abba yake fada musu abinda
Likitan ya ce game da farkawa in tayi.
Koda bude
bakin tsohuwa sai cewa ta yi ai ko dai ba a bar
mai sunan Malam ba, tunda an ce wanda suke
shiri, don in taga mai sunan Malam karasawa
zata yi. * 22.
Duk da ana cikin wani hali sai da
su Alhaji suka murmusa.
Abba kam daure fuska
yayi yana kallon Tsohuwa, Umma ta ce, "Ai da ne
Tsohuwa.
Yanzun shiri suke tunda ta daina rashin
jinta".
Likitan ya shigo ya sake musu bayani
kamar yadda ya yi ma Abba, sannan ya ce su
bata guri kada zantukansu ya farkar da ita a
samu matsala.
Suka fito, Umma ta ce da Abba ya
tafi gurin aikinsa, su Alhaji ma suka fita tare da
Abba.
Fati ta je gidansu Sahabi dan uwansa yana
kankarar rake a kofar gida, inda yake saidawa ta
tambayi Sahabi.
Yaron ya ce mata ya ffita, ta ce
To in yazo kaa ce masa Ummi tana asibiti ba
lafiya, an bata gado.
Karfe uku ya iso asibitin
hankali a tashe, sun gaisa da Umma ta raka shi
dakin, hankalinshi ya tashi da ganin Amaryarshi
kwance a gadon.
Abba kam yana gurin aikinshi
amma hankalinshi na Asibiti, su Alhaji ma duk
nan suka nufo, Abba sai da yayi magriba sannan
ya shigo asibitin.
Jikinshi babu karfi, bai matsa
sai yaga farkawar Ummi ba ne saboda yasan da
gaske ba shi ne ya dace idanunta su soma arba
da shi ba, ya samu su Umma da su Alhaji.
Sahabi da abokansa duk suna gurin, ya gaida su
tare da tambayar ko ta farka?
Umma ta ce har
yanzun dai shiru.
Ya nufi cikin gurin Likitan suka
gaisa, ya ce Likita har yanzu ba ta farka ba.
Suka
jera zuwa dakin, Likiran yana cewa cikin wannan
dan takin zata farka, In sha Allahu.
Sun shiga
takin tana dan motsi suka nufi gadon Abba ya ce
Ummi.
Likitan ya daga mishi hannu alamar yayi
shiru ita kam daidai lokacin mafarkin Abba take
wai suna tafiya ya rike mata hannu sai ga
Sahabi.
Yana zuwa ya kama hannunta tana
tirjrewa, sai janta yake zai fita da ita, Abba yana
tsaye yana kallonsu.
Ita kuma sai kiran "Ya Abba!
Ya Abba!!
Take yi.
Likitan ya kara kunne gurin
bakinta ya dagowa yayi ya dube shi.
"Waye Yaya
Abba?" Abba ya ce ni ne.
Liitan ya ce, matsa
kusa, ya kama hannunta.
Ummi.
A hankali ta
bude ido.
Ya Abba!
Ya abba, zan sha ruwa, ya ce
to ya kalli likitan za ta sha ruwa, Likitan ya ce,
"A'a bari ta dan kara warwarewa tukunna.
Likitan
ya kama kafafunta ya dan matsa, sannu ko.
Ta
kalle shi, kin ji zafi?
Bata yi magana ba ya dauki
allira ya 6are ya dan soka mata a tafin kafa ta ja
kafafunta alamun taji zafi.