← Book details Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 28

Sashe 5

Zurfin Ciki Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sun
gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu
tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani
bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka
amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?
suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi
karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida
abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye
ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi
haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san
ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a
masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt
kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma
muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke
kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka
shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a
tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita
kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt
da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame
su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da
gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to
yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi
shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,
tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya
kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai
tace, ina ganin xai fi mu haqura kada yaxo ni yayi
ta mun fada.nazir ya ce yanxun haka xaki ce?
ummi tace, um,sai da safenku.kada ku ja min
duka.sagir cikin jin haushi ya ce,ki xama
mangofak qarewan krt.sannan in kin gama wan
naki ya aure ki. ita dai ta shige gida.kusa da soro
ta iske umma da ya abba ta yo masa rakiya, tana
kuma ba shi aaki kan cewa yayi ta haquri,tace ina
fada maka ko yaushe ba fa fushi ko fada ne xai
saka matarka a hanya ba.lallashi da nashiha,ka
dunga koya mata giqki daka nutsu ka koya mata
ba gashi ka ce ta iya daidai gwargwado ba?abba
yace,hum lamarin yarinyan nan yayi nisa fa
umma,wankan jikinta ni xan koya mata? sallah fa
daga nake da ita.amma abin yaci tura.antynta
sau nawa tana xuwa tai mata fada duk a
cnxa,mkrtn ma ta qi xuwa.ni kuma da ce
ruwanta.umma cikin al'ajabi tace, sallah! sallai
ma bata san yi abba?abba yace umma baxan
mata sharri ba...

Ta ce Tabdi,to kuwa ba kuwa
kazantarta ta wuce jiki hr d zcy. wannan ita ce
kazanta mafi muni.

Don haka dole ne ka zage
damtse don ganin ta kama sallah,to menene
marabar arne d Muslmi in ba Sallah ba?Abba ya
ce Umma na mata nasiha na gaji.

Ta ce To kasa
ta a mkrntr Islamiyya,kila ta ji tsoran Allah in
tana jin Wa'azi.

Sannan ka dainga siyo mata
kasasuwan wa'azi.Abba ya ce Umma kaset nawa
na kawo mata bata sakawa,Kullum sai indiya da
Hausa fim,in naki sayan man fetur in tana da kudi
ta saya.

In kuma ba a ta da shi sai ta dauki
ittafin Hausa ta dukufa.umma ta ce Allah ya
kyauta,kaje kayi ta hkr tare da addu'a.

Ya kalli
Ummi,sannan ya ce ma umma,kada ta sake fita
gurin wadanan kananan yaran,sannan ya fita.

A
daki umma take tambayar Ummi daga ina suke?

Ta ce um,Umma kyale su ni sam ma ba su min
ba.

Umma ta ce to Allah dai ya miki za6i nagari.

Abba yana kwance a dakinsa ya yi lamo cikin
bargo,ya kasa amsa ma kanshi tarin tambayoyin
da ke yawo cikin kanshi.

Haka tambayoyi suke
zuwa masa daya-bayan-daya ,me yasa ya damu
da lamarin Ummi??me yasa da a ka yi sallama da
ita ya samu kanshi cikin wani tashin Hankali?

Me
ya sa ranar da zai je mata ziyara ya za6i ya sai
mata kayan kwalliya?

A fili ya ce,don tana
kanwata.Zuciyarshi ta ki amincewa da haka.

Me
yake shirin faruwa da ni ne? ya fada a fili.

Ya yi
juyi zuwa rigingine,sannan ya dauki filo ya manna
a kirjinshi, ya ci gaba da magana shi daya.

Bana
zaton cewa Son Ummi nake yi.don lkcn da na yi
tsananin Son Bishira bn ta6a samun kaina cikin
wannan yanayin ba.

Kai Allah ya tsare ni da Son
ummi,wannan mahaukaciyar
yarinyar..........bugun kofarshi da a ke yi ne ya
katse shi.

Murayar Bishira ce ta na cewa Babn
Walid!Babn Walid!!

Ya bude kofar da sauri,ta ce
Walid ne ke ta amai.

Ya fita ya dauki yaron daga
hannunta yana fadin Me zai hana shi amai,in ba a
ci sa'a ba har zawo sai ya yi,Saboda
kazantarki.Sam ba ki lura da me zai wawuro ya
tura bakinsa.

Ta ce Yau fa bai ci komai ba,tun da
safe yake wannan aman.Ya ce shi ne ba ki sanar
da ni ba?Ya cire masa kayan jikinsa wadanda ya
ji suna ta doka karni.. .

Ya isa igiyar shanya ya
ciri wasu yasa masa,sannan ya fita dashi.Wani
babban kyamis ya tafi da shi,mai kyamis din
likita ne,sai dai ba na yara ba ne,amma kowa
yazo sai ya duba shi.Nan dai ya masa bayani ya
ba su magunguna.

Sha biyu dai dai ya dawo,tana
zaune tana kallo ya ce "A'uzubillahi,wai ke kallon
nan masifa ya zamarmiki ne?to ki sani na kusan
fita da kayan kallon nan.

Ta ce,Tab,ka kaisu ina?
dadinta dai dafa gidan ubana a ka kawo su.

Ya
ce ta za su koma gidan uban naki.

Ta dafe kirji
"Zagina ka ke yi?ya dora mata dan a jiki "An
zage ki,ke din banza,kazama!yazube mata
maganguna ya fita.

Ya jima zaune a kofar
gidanshi dafe da kai,yana tunanin shin wai shi
kadai ne bai yi sa'ar mata ba,ko kuwa duk maza
ne.Ya tuna abokanshi 2 da suka yi aure.

Muktar d
Jamilu,sam ba su da wannan matsalar,duk lkcn
da yaje gidansu tsaf matansu,ga mutunci da
mutanta mutane.

Shi kuma a cikin abokanshi
babu mai zuwa gidan sbd bata gainin kowa da
gashi.

'Yan uwanshi sai wanda ta za6a sannan
zata yi hulda da su.

'Yan garinsu kuwa can
陇ZAMFARA陇In suka zo kiri- kiri take nuna musu
kyama ga rowa,sam bata hulda da matan
abokanshi.

Ya numfasa zai bi shawarar Umma ya
gani, amma gaskiya Bishira ba matar zama ba
ce.

Tun da ya dawo sallarAsubahi dakinta ya
shiga tana ta shirga bacci.

Walid kuma ya yi
faca-faca cikin kashi ya tausasa zuciyarshi ya ce
"Bishira! .

Bishira!!Ya dan duki kafarta,sannan ta
tashi.

Ya ce Ki tashi ki gyara masa jiki kiyi
sallah.Ta ce,Tab, me ya yi?ya ce, "kashi ya
yi.kurum sai ya ji ta ce Tab,wannan akwai dan
iskan yaro.Yanzun dan ubanka kashi ka min?

Sam bai san lkcn da ya watsa mata mari a baki
ba,cikin murya mai karfi ya ce "kada ki kuskura ki
sake ce ma dana dan iska!kar ki sake zagar min
yaro kada ki yi wa dana baki.Ba zan dauki
wannan ba. .

Ta mike daga kan gadon tana kuka
Ni ka daka? wlh sai na rama.

Kasancewar lebe
baya raina duka,sai jini.Nan da nan sai kumburi.

Ta cakumo shi,wlh sai na rama.Ya hankadata kan
gado ya bar gidan.cikin zcyrshi yana fadin
,"Wannan fitina da me tayi kama?

Ita kam ruwa
ta dafa sannan ta wa yaron wanka, cukuikuiye
zanin gadon ta saka shi cikin baho,sannan tayi
kwaskwarima ta sabi danta baki suntum ta nufi
gida tana kuka.

Mahaifinta bai nan yana
Abuja,Hjy Zainu ta kalle ta bayan ta gama kero
karyarta.

Wai don yaro ya yi kashi ta ce yaron
bai kyauta ba shine ya hau ta da duka da zagi.

Hjy Zainu ta ce Amma wannan da muciya ya
dake ki ko?ta ce, Da hannu ne,nushina fa ya
dinga yi.

Hjy Zainu ta ce Ai kin gani ba yadda ba
a yi ba ki tsaya kiyi karatunki kin ki,kin kafe sai
kin aure shi,wannan matsiyacin?

Dama talaka
yana da wannan tsiyar.Yanzun za ki zauna mu
jiraZuwan Alhj,ba za ki koma ba.Ya dai baki
takardarki in yaso ki koma mkrnt.Su kuma su
dauki dan nasu.

Bishira dai tayi shiru,zcyrta tana
jinjina rabuwa da Abba d kuma danata.

Abba kam
gidansu ya nufa.Ummi ya soma cin karo da ita
tana sanye da doguwar rigar bacci,ta dora rigar
sanyu ta sakar ulu, a kai tana wanke baki da
busushi.

Ta dube shi,mmkn ganinshi tayi a
wannan lkcn.Sai da ta dauraye baki sannan ta ce
masa sannu da zuwa,ya amsa a hnkl bai san mai
yasa ya kasa dauke idanunshi daga kanta ba,hr
ta gama alwala tayi addu a ta mike.

Ta dube shi
da niyar yin magana,amma sai ta fasa don tana
tsoron kada ya daka mata tsawa.

Ta daga
labulan dakin Umma zata shiga.

Ya ce, "Ke!' ta
waiwayo cikin hada rai,domin ta tsani kiranta da
yake da ke!Ya ce Ummana fa?ta kalli dakin Alhj
Ba ta fito ba,,Ta shige ta zura hijabi ta tada
Sallah.

Ya shiga dakin ya zauna,yana kallonta
tana Sallah zcyrshi tana nazarin Rayuwar
Ummarshi.

Tun tasowarshi ya ke ganin kulawa da
kyautatawa da take yiwa Alhj Babba ga biyya,
sam bata wasa da dk wani abu nashi daga lkcn
da ya shigo gida ta gama sauraron kowa sai lkcn
da ya fita.

Bai ta6a jin sunyi sa'in-sa ba bare ta
daga murya sama da tasa.Shin sauran matan ba
su fahimci irin wannan ladabi ba ne?Ummi tana
addu'a zcyrta cike da tunanin shi kuma ya Abba
me ya kawo shi da wannan sassafen?

Muryar
Umma suka ji daga waje tana cewa,"Ummi in kin
idae ki fito ki share gidannan,ki wanke bayi,Ummi
ta ce To''.

Sam Umma ba ta san Abba ya shigo
ba,dmn da ta ba Ummi umurni sai ta sake
komawa dakin mijinta, Ummi ta wanke bayi
kansu,sannan ta share ko ina na gidan, ta kunna
risho ta dora ruwan karyawa, sannan ta shiga
firar doya.

Gyangyadi yake daga zaunw, Muryar
Ummanshi ce ta farkar da shi tana cewa, "A'aha!
ya bude ido cike da bacci.ZURFIN CIKI book 2 part 4
ZURFIN CIKI book 2 part 4
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:10
"A'aha! ya bude ido cike da bacci.

Ya kalle ta tare
da yin mika,ta ce "Lafiya"?

Ya ce,Umma lfyr
kenan.Ta zauna da sauri Me ya faru Kuma?
Chapter 5 · 0% Book details