← Book details Zuciyar Masoyi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 34

Sashe 14

Zuciyar Masoyi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Maganar ta Sosa ran mami matuka fiyye da tunanin mai karatu.
dan haka itama ta rinka fadar magana iya yadda zata huce.
ta kara da cewa randa duk mama hafsa ta tako gidan nan dole ayi wacce za'a yi .
Kuma wlh dole dole ayi yadda take so a karshen ta cewa dady kuma bazata taba amincewa da wasu can su lakawa Abdullah cikin banza ba.
byn ya rabu da yarinya sama da wata uku a dawo ace wai ciki gareta me yasa tun lokacin basu fadi hakan ba sai a yanzu .
mami tana huci ta kada kai ta bar part din dady ya zubawa kofar data fita ido "ko kwakwaran motse kasawa yayi.
saboda dacin da yake ji na bacin rai a wuyansa idansa yayi jawur tamkar zasu fito.
me yake shirin faruwa ne dashi da rayuwar gidan nasa .
yana nan zaune har tsawon mintina talatin bai bar gurin ba teema ce tashigo ta kofar da mami ta fita..
tana yi tana kallon bayanta .
kallon ta dady yayi .
Ya jima sannan ya dan hadiye miyo mai dacin daya tsaya masa a makoshi.
yace yaya dai teema .
Teema takaraso kusa dashi ta zauna.
yana kallonta Tace dady mami ce sai kwalla ta fara cika mata ido yace ya isa meyafaru da mamin ?
teema Tace dady kwata kwata mami ba ita bace ba yanzu .
kowama baya gabanta a yanzu .
dady mami bata da ra'ayin kanta a yanzu ta sake fashewa da wani kukan.

Dady ya rufe idonsa sai da ya barta ta danyi kukan sannan ya dakatar daita .
teema ta dan goge hawaye .
ta dan sharbe majina tace abin tsoro ma dady mami fa yanzu ko ibadarta bata gabanta sai tayi kwana biyu ko uku batayi ba.

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun abinda dady yake fada a ransa kennan yana cikin tashin hankali abinda mami ta gama yi masa a dazu .
sai ga teema tazo da wani "duk akan mami ya zubawa teema ido kawai ya kasa magana "yasan teema da natsuwa ya Kuma san yadda suke da mami.
koma meye zata iya fahimta.
tace na kula da haka sosai yanzu ibada ba a gabanta take ba .
ita dai a yanzu duk yadda zatayi ta farantawa wannan mama hafsa shitakeyi .

Teema ta dan kalli kofar data shigo ta rage murya sosai.
sannan ta kara matsowa kusa da dady tace ni dady ko wani hali mami take ciki ina ganin akwai sa hannu wannan mama hafsa din.
tana da alhakin a ciki saboda ranan nan naji tana cewa mami wai iyayen aunty Aisha sun mata asiri ita da brother Abdullah .
dan haka ta kawo wani abu tabata tace shi zata dinga garwashi tana turara jikinta dashi kullum .
Brother Abdullah kuwa ta bayar da wani abu baki a Leda wai a dinga masa abinci dashi .
wai duk asirin daaka musu zai karye.
kuma ta dinga jadadda mata sosai tayi kada tayi kuskure yin haka .
mami ta dinga yi wani lokacin ita mama hafsa da kanta ke karba tayi mata .

Dady ya zubawa teema ido sanda ta dago tana kallonsa yace Allah dai yasa teema ba labewa tayi ba ta ji abinda iyayenta sukeyi ba .

atsorace ta kalleshi idonta cike da Hawaye tace wlh dady ba labe nayi musu ba .
ita mama hafsa din ce idan tana yin wani abun sai kaga kmr bata Gani.
duk abinda zatayi wani lokacin muna gurin zatayi .
Amman wannan da naji din ma ina bedroom din mami ne "a kwance ta shigo ta Sami mami ta dauka ko ina bacci ne .
take gaya mata ahankali.
rannan kuma ina wanka ta hawo da sauri take cewa faiza wai ta zubawa brother Abdullah din maganin kuwa gashi can za'a tafi kai masa abinci "tasan ance kada maganin ya wuce jiya zuwa yau da rana.
ban ji abinda faizar tace mata ba.
Sai dai naji sun canza magana .
dady yace na dauka labe kika tsaya yi musu yace dan bbu kyau musamman ma idan iyaye ne.
tace A'A wlh yace to shikenan kuyi hakuri duk zan san abin yi in Allah yaso .
komai zai gyaru kinji .
Ta amsa ta tashi tana fita .
dady ya rike gefen hakarkarinsa ya Kuma dafe kirjinsa.
ya mike da kyar ya shiga bedroom dinsa ya zauna a gefen gado ya jawo durowa yana dudduba magungunansa .
ya sha wani bai iya kai hannushi ya dauko ba dan haka ya hakura ya kwanta dan ya dan huta ya dafe kirjinsa sosai da yake bugawa .

Abdullah kuwa yana fitowa daga part din dady salis ya tareshi "ga Dr sagir yazo yana nemansa "da hanzari ya karasa inda yake gabadaya ya rike hannuwan Dr sagir yana dariya.

Wow Abdullah yi dariya cike da farinciki yau ranarka ce 😃😃😃😃😃😃😃😃😃😃😃😃😃

MMN SUDAIS CE
[3/12, 3:02 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗
ZUCIYAR MASOYI
💖💖💖
💗💗💗💗💗

AISHA A BAGUDO

Page 65

Gabadaya ya rike hannuwan Dr sagir yana dariya.
yace doctor na taba gaya maka nayi mafarkin ni da Aisha muna tsakiyar macizai sun kewayemu" har wani me kyalli a cikinsu ya howa kaina ya sauka ya koma jikin Aisha daga nan na farka.
sau uku ana gaya min wadannan macizan dana Gani ya'ya ne..
gashi nafara jin kamshin cikin sananin farinciki yace doctor doctor doctor Aisha ciki gareta tunda muka rabu ban sani ba.

Dr sagir ya kalleshi da kyau yace friend waya gaya maka hakan?
yace dady bai je min daurin auren faiza ba.

sai yaje min bikon Aisha ya tarar ashe tana dauke da cikina .
Gabadaya shima Dr sagir hannuwansa ya jawo suka rungume juna suna murna.
Abdullah yace doctor kaima kana farinciki ko?
Dr sagir ya kasa magana sai dai yarinka girgiza masa kai .
sai da suka saki juna sannan Dr sagir ya sake miko hannu yace congrat...

Abdullah yace thank you doctor muje nayi sallar isha'i ka rakani gurinta yanzu zanje "bazan bari na kwana ban ganta ba
Dr sagir ya sake kallon.

Sai Abdullah ya idar da sallah ne Dr sagir yace friend ka bari zuwa gobe mana ,sai aje da manya Abdullah yace in mutu kennan.
Dr sagir yasa dariya yace baza ka mutu ba baban bby .
Abdullah ya mike ai maganar manya takare nima yanzu babba ne tunda zan zama uba.

Suka yi dariya ,Abdullah na kokarin fitowa Dr sagir yace are you serious friend zuwa zakayi .
ko ka manta sakin Aisha kayi Abdullah ya dago da sauri ya kalleshi Dr sagir ya amsa masa da haka ne ,"sannan ya Kuma cewa tsawon watanni kun rabu ka barta da ciki baka nemeta ba sannan yanzu kaje mata karfe tara na dare nasan abune mawuyaci ta kalleka.
idan da manya aciki sai a hadu a sulhunta.
a sake sabon aure jikin Abdullah ya danyi sanyi Dr sagir yace wlh gara ka kwana yau kana addu'a Allah yasa ba tayi fushi da kai mai tsanani ba .
,kaga gobe sai ka lallaba kuje da dady ma zaifi.

Har Dr sagir ya bar shi zuciyarsa natayi masa wasi wasi 'sau Tari idan wani abu na farinciki zai same shi sai garin ya daure masa" daga baya ya tsinke masa da alkhari.
tsawon watanni da yayi cikin ukubar rashinta har zuwa yau din .
daya zamanto inda zaije ya huta ma ya rasa a karshe gashi ya juye masa alkhari "zai zama uba nan da dan wani lokacin .
dan haka yasan koyaje da kyar in zai ji ko yaga wani abu na bacin zuciya .
dan haka ya murza sitiyarin motar sa shi kadai dan salis yariga yatashi daga aiki.

Amman har yashiga lungun gidansu shi kadai a kafa "ya tuna da wani ido zai kalli mlm abu" sai yau yake zuwa garesu cak yaja ya tsaya ya kasa karasawa .
gara zuwa da dadinsa zai fi har ya juya yaji yakasa tafiya ,nan yasamu jikin bango ya rabe" yana hango kofar gidan .
yana tuna akwai kadararsa a ciki "yana nan tsaye har yayyenta guda biyu suka zo suka shige gidan .
sannan ya hakura ya tafi duk da bai ganta ba Amman zuciyarsa ta masa dadi .
Yau ko ba komai zaiyi kwanan farinciki .
bayan yayi sallolin da ba zai iya kayyadewa ba .

Karfe shida wayar dady ta sameshi yana jiransa Abdullah yaisa cikin bedroom dinsa ya sameshi har zuwa lokacin yana kan abun sallar sa .
,cikin farinciki kmr yadda yaga dady ya karasa ya gaisheshi "dady ya karasa jan carbi sannan ya amsa "ya nuna masa nan kusa dashi da hannushi.

Abdullah ya matso ya zauna inda ya nuna masa cikin fara'a dady yace Abdullah Amman kayiwa Allah godeya da zai azurtaka da zuria ko Abdullah ya girgiza kai yana murmushi shima dadin dariya yayi .
yace a to dan nima tun jiya nake godiya ga Allah zai kara mu zuria a cikin gidana .
Abdullah baice komai ba illa murmushi daya sake. dady ya numfasa yace abinda yasa na nemeka tun yanzu nasan zakayi mamaki akan wannan Batun kuma ne yuwa zakaji wani bakon abu.
wanda ba mamaki bazai maka dadi ba .
kada ka taba sanya damuwa ko shakku a game da abinda ke jikin yarinyar nan Aisha .
ni dai na amince tabbas cikin dake jikinta na cikin gidan ne.
tun rabuwarku akwai wanda nayi waya na dora akan lamarin, to har likitan daya dubata na kwana uku da rabuwarku sai daya yayi min.
bayanin adadin kwanakin cikin dake tare daita a jiya.
dan haka komai maminka zata ce maka ka saurareta ne kawai ka amsa mata .
Amman kar ka bari maganar ta tayi tasiri agunka .
Abdullah ya daga kai dady yace Allah yayi muku albarka Amin Abdullah yakasa tashi daga gurin, dady ya fahimci yana son wani abu ne" yace uhm ina jinka da kyar Abdullah yace dady ita Aisha fa .
Chapter 14 · 0% Book details