← Book details Zuciyar Masoyi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 34

Sashe 13

Zuciyar Masoyi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dady yayi shr yana kallon mami ita kuwa ko gezau batayi ba .
sai ma ta tashi tayi ficewarta ,dady bai yi mata magana ba Abdullaha ma ya mike ,zai fita dady yace ya koma ya zauna sannan dady yanemi wayar side din su teema ya kirawo bayan yan mintina kadan sai gata ta sake shigowa a tun dazu da suka zo yi masa sannu da zuwa.
bai ce mata komai ba. Baya ga tambayar ta key part din Abdullah da akace yana gunta .
taje ta dauko ta dawo nan falon dady Abdullah yasa hannu zai karba Amman dady yace A'a .
ta Miko masa ya karba yace shikenan teema gud nig .
tana fita ya dawo da kallonsa kan Abdullah yace yashiga nan part dinsa ai akwai dakuna ya zabi duk wanda yayi masa ya kwanta a ciki.
Abdullah bai gane yadda Dady yake nufi ba iya tunaninsa shi dady zai bawa key part din nasa ya tafi can ya kwanta.
Amman sai yaga zura su cikin aljihun gaban doguwar rigar dake jikinsa.
Abdullah ya mike jiki a sanyaye yabi dakunan dake bangaren hagu da part din dady yake kwana ya shige ciki.

Har gari ya waye dady bai runtsa ba .
ita kanta mamin bata sake neman sa ba a daren tunda tabar part din nasa .
da safe abubuwa suka cigaba da daurewa dady kai a game da mami .
ita dai kawai hidimar biki take gobe daurin auren.

har Abdullah yazo ya gaishe shi ya sake ficewa gidan baki bai ce masa komai ba baya ga amsa gaisuwar da yayi.

Dama can ya kan dan zazzaga ma'aikatan gida lokacin zuwa lokacin to yau ma haka ce takasance tin karfe goma ya fito daga part dinsa .
gabadaya environment din gidan yayi clear.
tun asuban fari dan haka daga nan gidan baki ya wuce .

Har yammaci ranar bai shigo gidan ba mami kuma bata nemeshi ba shi .
kansa Abdullah bai ji wani abu daga dad din nasa ba.
dan haka shima office yayi wucewarsa yayi zamansa dan yadda yaga fuskar dady yau ko magana baya son yayi.
shi ma acan ya yini duk da anan hutu gobe daurin auren manager koda Dr sagir yazo nenanshi shima sai can ya sameshi .

Amman shi Abdullah ya kosa koma me zai faru gara ya faru dan ya riga yasan halin dadinsa.
idan yayi irin wannan shr to idan bom din yashi fashewa kowa sai ya shafa.
duk da yace ya hakura da Aisha zai iya yi rayuwar Sa haka ko ba macce.
Amman itama yakagu yaji abinda dady zaice a game daita.
duk da yaci alkawari n dady .
bai nemeta ba har gashi dadin yadawo kusan kwanaki dari da yan kwanaki kennan da rabuwarsu Amman har yau yana zaman jiran dady yaji abinda zai ce a kanta .

Da yammacin baki suka karaso daga abuja mawaftansu na can abuja wanda mami ta wakilta su zasu je a matsayin waliyan Abdullah.
hannu biyu biyu dady ya sauke su .
a gidan baki ganin su duk yadada tada hankali Abdullah shi dai yasan muddin ya auri faiza to yayi alkawari yabar Aisha kennan .
itama faiza baizaiyi rayuwa daita ba dan haka kasa zama yayi acikinsu dole yabar gurin duk da dady yana lura da halin daya shiga.

Aranar ma dady cewa Abdullah yayi ya kwana a inda ya kwana jiya.

Abdullah ya nemi su danyi magana har yana koro masa maganar mutane daya kora a company Amman dady ya daga masa hannu yace yaje ya kwanta .
zai neme shi akan hakan cikin sanyi jiki Abdullah yatashi ya barshi .
Amman a ranar shima kasa runtsawa yayi shi kadai yasan irin yadda ya dinga ji a jikinsa

Washegari garin ranar jumma'a kennan da yakama daurin auren Abdullah da faiza.
tun da safe da Abdullah ya shigo falon dady .
kallo daya dady yayi masa ya gane halin dayake ciki Amman har a lokacin bai ce dashi komai ba.
duk da yasan halin dady Amman har yashiga mamakinsa a ransa" Abdullah yayi dan Jim ....yana Jira ko dady zaice masa wani abu sai dai bai ji komai ba.
sai da zai tashi ya fita ne dady yace yabashi duka wayoyinsa Abdullah ya dago yana kallonsa da kansa yanuna masa alamun haka yake nufi.
Abdullah ya kwaso su duka ya mikawa masa sannan ya fita karfe takwas shima dady ya kulle koina na part dinsa ya fita gidan baki can ya iske Abdullah ..
Abdullah ya kwaso abinda za'a bada amatsayin sadakin faiza ya mikawa dady .
,dady ya jima yana jujjuyasu yana mamaki sabon halin da mami ta daukarwa kanta .
Abdullah ya nuna masa yadda mami tace ayi kennan.
dady ya girgiza kai kawai Abdullah ya fito zai shiga part din dady Amman yaga koina a kulle gashi part dinsa dady ya karbe key.

makullan gidansu da Aisha suma suna part dinsa na nan.
gashi dan gidan bakin dayake zuwa yana dan hutawa shima su dady suna ciki da baki .
yarasa ma ina zashi yayi tunanin tunda yarasa Aisharsa a yanzu duk abinda ya rasa sai yaji tamkar bbu wani damuwa a yanzu ko cewa akayi ya dinga kwana byn masallaci zai iya .

Tunanin yayi ya wuce office ya kwanta ya kulle kansa kawai.
dan haka ya sanarwa dady inda ya tafi koda za'a nemeshi .
tunda yaji mami tace tana son lallai idan an sauko za'a daura aure.

can ya yini daga shi sai salis sai ko tsirrarun ma'aikata.
har byn sallah la'asar sannan yayi tunanin ko dady ya masa guzirin ne shi ya zauna inyaso su sa tafi sokoto daurin auren .

Mami kuwa tun safen ranar ta kasa zaune ta kasa tsaye ba Abdullah ba dadinsa duk wayoyin Abdullah data nema duka a kashe suke.
ta aika gidan baki yafi sau goma bbu baki bbu Abdullah bare dady.
itama har yamma takasa sanin tudun dafawa dan ko har dady tanema a waya bata sameshi ba.
ga part dinsa koina a kulle.
sai kusan magariba sannan shima Abdullah ya baro company yasamu sallah a masallaci cikin gidan a sahu na karshe.
dan haka shine ya fara fitowa ,yayi gaba kadan musa driver ya karaso da sauri yana gaya masa dady yace ya jirashi to shima dadin din yake son Gani dan bbu waya ne a hannunsa .
da tun dazu ya nemeshi tare suka koma har part din dady suka ci abinci dady ya fara shirin yiwa Abdullah bayanin kennan .
sai ga mami tamkar anjihota tana tambayar ya batun daurin aure?dady ya zuba mata ido kmr me shirin shiga iska sannan yace tasamu waje ta zauna .
da kyar ta zauna din shi kuwa Abdullah kansa a sunkuye yake yana zaune kan karfet .

Dady ya dubi mami da kyau yace maganar daurin auren na dageta daga yau.
kuma na sallami kowa kmr yadda kika amincewa Abdullah to haka itama yarinyar da iyayenta sai naji daga garesu na farko kennan
tunda shi kika soma nema .

abu na biyu kuma nagode nagode da wulakanta min diyar yar'uwata da kikayi .
abunda ni bazan taba yi miki ba kennan har duniya ta nade a tunanina yarinyar ko b daga jinin take ba yakamata mata ki mutuntata
A saboda tana auren danki .
Amman duk na gode .
abu na karshe kuma da zan sanar miki yarinyar da kikayi kokarin raba Abdullah daita.
to ina yi miki albishir itace zata fara kawo miki jika a gidan nan .

Gabadayansu suka soma kallon dady ,dady yana murmushi sosai ya kalli Abdullah yace Aisha na dauke da ciki tun lokacin da kuka rabu .
haka tazu iyayenta suka bani tabbacin "sanda tabar hannuka ciki dake tare daita bai kai wata ba zuwa yanzu abinda da ake hasashe cikin ya shiga wata hudu .

Sauran kadan Abdullah ya narke a zaune a gurin saboda yadda yarinji a jikinsa.
hawaye ya fara zubo masa yana kallon dady da mami duk a lokacin daya.
fuskarsa ta nanu kmr ba daidai yaji abinda yace ba.
sai Kuma ya dinga murmushi yana zubda hawaye .
duka abubuwa masu mahimmanci a lokacin guda .
dady ya kalleshi yana masa murmushi shima dan tsabar abin farinciki da yajiyo ne yasa shi manta bakincikin abinda mami tayi masa . Kuma
ya fita a zuciyarsa .

Mami kuwa ta hade fuska tamau dan ita maganar takaici ta kara mata .
ta cewa dady ni ga abinda nake son ji takamaimai Amman ka fara min wata magana can .
Abdullah ya juyo yana kallon bakin mami tace shikenan hujjarka ta hanawa a daura aure a yau.
kana son mama hafsa tace banyi mata ba daidai ba kennan .
dady ya kalli Abdullah yace shikenan Abdullah zakana iya tafiya abunka .
sai na nemeka Abdullah ya mike dady ya kwaso wayoyinsa ya bashi .

har kusan tara na daren ranar mami na tare da dady tamkar wacce ranta zai fita daga jikinta tana fadan akan hana daurin auren dady yayi .
ita ba ma kowa take ji ba cikin al'amarin sai mama hafsa .
abinda ya kara girgiza dady kennan .
yadda take maganar cikin tsanyewar zuciya tana kuma fada masa duk abinda yazo bakinta kmr ba mijin ta ba .
yasan ta sosai tsahon shekaru da suka kwasa tare .
Amman bai santa da hakan ba.
ransa idan yayi dubu to duk yayi kaca kaca ya baci ya dubi mami sosai yace aure tsakanin Abdullah da yarinyar nan na haramta shi .
sai dai bayn raina mace daya na amince masa itace yarinyar da kika sa shi ya rabu daita sai dai kuma idan daga baya shi yayi ra'ayi dan kansa .
idan har da wani abu da zai faru to ni ishaq ina jiransa .
gashi nan ubangiji yana shirin nuna miki ikonsa a jikin yarinya .
Amman kin zauna kina hakilon banza.
dan haka duk abinda zai faru ya faru Allah yasa yankaki hafsa zatayi akan rashin yin auren to Bismillah.
Chapter 13 · 0% Book details