← Book details Kazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 44

Sashe 30

Kazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To da wa kike kama? Ni fa ba na ɗaukan ki matsayin kishiyata, baki ga ko da na zo gidan nan mijina Aminu bai haɗa mu waje guda ya nuna ki a matsayin matarsa uwar gidansa ba, wannan dalilin ya sa na ga baki da maraba da mai wanke-wanken, kuma ga shi dai cikin kwananki ya ƙara mini sati guda, kin ga kenan baki da wani muhimmanci"

Tun da ta fara faɗar baƙaƙen maganganu, abin ya yi wa Saddiqa ciwo amma kuma sai ta raina Zulaihar don haka take ganin ɓata lokaci ne da rashin girmama kai ta tsaya sa'insa da ita, amma sai ta yanke shawarar faɗa mata magana ɗaya zuwa biyu hakan ya sa ta ce

"Ni fa in na raina kasuwa ne ko sautu ba na bayarwa, kuma ina so ki sani kayan da suke samun wanki da guga ana tsafta ce su koyaushe, su ne kayan da mutum yake jin yana so ya sanya a jikinsa, amma in har kaya basa samun abubuwan da na lissafa to koyaushe mutum zai ji ba ya ma son au raɓe shi" Tana kaiwa nan a maganarta, ta juya ta cigaba da aikin gabanta.

Zulaiha kuwa saboda tsabar toshewar basira, bata fahimci kurman baƙin da Saddiqa ta karanta mata ba, bare ta gane magana Saddiqa ta faɗa a kan cewar Amunun da take kishi tun da ƘAZAMI ne ita bata ma sha'awar ya kusanci inda take.

Buguzum-buguzum ta juya ta bar kicin É—in.

*BAYAN KWANA BIYU*

Aminu ne bayan ya dawo daga kasuwa, suka rinƙa bala'i shi da Zulaiha, hakan ya sa ya fito ya bar mata ɗakin, don ya ga ko kaɗan bata raga masa.

Ɗakin Saddiqa ya nufa, ƙamshin turaren wuta ya cika ɗakin, tana zaune sanye cikin fararen riga da wando, gaban rigar an yi pink ɗin flower. Da sallama ya shigo tun da ta amsa masa ta maida hankali ga cin gaɗar da take. Zaunawa ya yiannu ya miƙa ya tsakura ya kai bakinsa.

Tun da ya zauna ta tsaya cak da cin gyaɗar, saboda warin rana da yake tashi daga jikinsa, amma haka ta daure, wani kallo ya yi mata mai cike da shauƙi sai ƙare mata kallo yake, cikin ƴar murya ya ce

"Saddiqa manyan mata, ana nan ana caɓa ado da kwalliya, kin yi kyau ɗakinki ƙamshi ko ina" Ya faɗa yana baza hanci, tare da tuno yadda ya baro ɗakin amarya da rabon ɗakin da shara, tun shekaran jiya da ya share da zai yi baƙi. Kallonsa ta yi ta ce

"Anya kuwa, ni ɗin ko dai ɓatan kai ka yi" Yana kafe ɗan ƙaramin bakinta da yake sheƙin lipstic ya ce

"Da ke nake mana" Duk kallonta da yake sai ya ji yana buƙatarta. Ƴar dariya ta yi ta ce

"Na gode" Yana wani ɗan kashe mata ido ya miƙa hannunsa zai kai jikinta, da sauri ta ɗan ja baya, cike da mamaki ya ce

"Kamar zan aikata haram" Ta ce

"Ni dai ban ce ba, amma dai a iya sani na, sai nan da kwana huɗu ne kwanakin amarya za su ƙare" Kamar ta ambaci sunan maƙiyarsa ya ce

"Wace amarya kuma" Banza ta masa.

Nan ya zauna yana ta ƙoƙarin kai hannunsa jikinta, amma ta ƙi bashi amsa, da ta gaji ma sai ta fito ta bar shi a ɗakin don duk ya haɗe ɗakin da warin rana.

Lokacin da ta dawo, don dama ɓangaren Sumayya ta tafi, sai ta tarar da shi ba ya nan, baki ta taɓe ta ƙasa saka turaren wuta, ita tunaninta ma in sati biyun ya ƙare yadda za su dawo su yi rayuwa da shi.

Misalin ƙarfe biyu na dare, Aminu ya kasa bacci tun da ya ga shigar Saddiqa ya saka a ransa yau a ɗakinta zai kwana, sai dai Zulaiha uwar ƴan kishi yake tsoro, hakan ya sa ya yi bakam kamar mai bacci. Yanzu jin tana ta munshari ya lallaɓa ya sauka daga gadon, a hankali ya buɗe ɗakin ya fito ya mayar da ƙofar ya rufe.

Ɗakin Saddiqa ya je cikin sanɗa ya tura ƙofar ya shige, cike da farin cikin zai biya buƙatarsa a waje mai tsafta ya hau kan gadon. Saddiqa tana cikin bacci ta ji hayowar mutum kan gadon, kafin ta yi yunƙuri ta ji warin jikinsa ya sanar da ita wane ne. Tana shirin magana ya rungumota.

Zulaiha cikin bacci ta miƙa hannu don taɓo ango amma ta ji babu shi babu dalilinsa. Matsawa ta yi don duk tunaninta ko ya bata tazara ne, duk da ta san a kusa da juna suke kwana.

Tana mirginawa ta ji wayam, idanu ta buÉ—e don duk abin da take idanunta a rufe suke, kaf kan gadon ita kaÉ—ai ce.

Cike da mamaki ta tashi ta kunna fitila, ɗakin ta shiga ƙarewa kallo babu Aminu babu alamarsa, ko kan gadom sai wata singiletinsa da ta ci wani uban datti.

Bayi ta nufa amma Aminu ba ya ciki, cike da mamaki take tunanin ina zai je a cikin daren nan, don ta duba agogo ta ga ƙarfe biyu har ta gota.

Idanunta ta sauke a kan ƙofar ɗaki, ai kuwa ta ga alamar an buɗe ɗakin don ƙofar bata rufu sosai ba, a zuciyarta ta ce

'Ina Aminu yake? Wallahi yau za a yi bala'i idan har zargina ya zama gaskia' Ta faɗa a zuciyarta tana buɗe ƙofar ta fito....

ƘAZAMIN MIJI BOOK 1 FREE ne BOOK 2 NA KUƊI 500 MAI BUƘATA ZAI BIYA TA ASUSUN

Faiza abubakar 9030283375 opay shaidar biya ta 09025576222
[5/5, 6:25 PM] Mom mashkr & Afrah: https://chat.whatsapp.com/BcJ4LIJJQlfHRgfiJUnBJo

*KAZAMIN MIJI*

NA

MAMAN AFRAH

First Class Writer's Asso.📝

Daga marubuciyar:
Bonono rufin ƙofa...
Ruɓaɓɓiyar igiya
Ƴan adaidaita sahu
Ungozoma
Ƴar zaman wanka
Ƙara'in inna delu
Beelal
Jalli joga
Da sauran su.
*09025576222*

BOOK 1
PAGE 15

*YAYA SULE*

Soyayya mai ƙarfi ta ƙara kankama tsakaninsa da Salaha inda yake ƙara iya takunsa ga duka matan guda biyu, wato Salaha mai shirin shigowa gidansa sai kuma ita mai gayya mai aiki Amina, ta hakan yake cin karensa babu babbaka.

A inda Amina, har yanzu tunaninta yake ƙara tabbatar mata da cewa ita kaɗai ce mamallakiyar Sule kuma ita kaɗai za ta rayu da shi, daga ita sai ƴaƴanta wannan ya sanya take cin duniyarta da tsinken tsire, tana huce hanci kanta yana fashewa ita a nata ganin ita ce mace ɗaya tamkar dubu a wajen mijinta. Hakan ya sanya idan zama ya haɗa su da Saddiqa take jefar mata da magana a fakaice, duba da yanzu Saddiqa bata fiya zuwa ɓangarensu ba, sai take cewa Saddiqa baƙin kishi ne yake nuƙurƙusarta shi ya sa bata son shiga cikin mutane, ta gwammace ra zauna a ɗaki ita kaɗai, idan ta faɗawa Saddiqa hakan sai dai ta yi dariya, don ita Saddiqa ta sani bata wani jin kishin Aminu, duk da dai idan ta ce bata son sa ta yi ƙarya tun da auren soyayya suka yi, amma kuma a duk sanda ta tuna ƙazantarsa da kuma irin mugayen halayensa da ya mata, na watsar da wasu daga cikin buƙatunta da Allah ya ɗora masa, sannan a gefe ɗaya ba ya son cikin jikinta haɗe da wulaƙanci in har ta tuna hakan tana jin son sa ya ragu da kaso mafi yawa daga cikin wanda take masa.

Amina ce zaune a bakin gadonta tana daddanna waya, hira suke da ƙawarta a akan zancen za a yi wa qata ƙawarsu kishiya, shi ne Amina take ta cika baki, tana cewa macen da ta isa ba a mata kishiya, tun da ga shi nan ita ko alama Sule ba ya ma sha'awar kula mace.

Murmushi ƙawar tata ta turo mata kafin ta mata rubutu kamar haka ta ce

"Amina, ki kiyayi namiji fa, shi namiji ɗan kunama ne baka gane zafin dafin jikinsa sai lokacin da ya harbeka, amma fa son mata da kuma ƙarin aure a ran kowane namiji yake, sai dai idan bashi da halin yi ko kuma lokacinsa bai yi ba, ko kuma dai bashi da rabon ƙarin auren har ya bar duniya" Amina tana gama karantawa ta mata replaya da cewa

"Ba za ki gane irin ɗinbin son da Sule take mini bane, ba na jin akwai wata ƴa mace da zai kalla da sunan soyayya bare har ya ji yana son aurenta, ni shaida ce babu abin da yake ɓoye mini" Ƙawar tata ta ce

"To ke in zai yi auren ko in yana kula Æ´an matan faÉ—a miki zai yi, bayan ya san bakya so kuma dai ya san yadda yake koÉ—a ki, ai akwai mazan dansuke baka komai a rufe" Amina ta ce

"Ki daian faɗa mini hakan Fauziyya, mijina nawa ne na ni kaɗai, sannan mijina yana cikin mazan da basu da rabon ƙara aure har su koma ga Allah, don haka mu yi wata hirar ba wannan ba, duk wacce kika ji za a yi wa kishiya a cikin ƙawayenmu ki faɗa mini, ni kuma ki ba a gayyace ni ba ,an je dannar ƙirji!"

Suna cikin chart ɗin ne wayar Sule da take a kan madubi ta shiga yin vibration, har ta share bata je ta duba ba, har kiran ya katse tun da shi yana wanka. Jin kiran ya ƙara shigowa a karo na biyu sai ta ajiye wayarta ta je kan madubin ta leƙa wayar, MAMUDA sunan da ta gani kenan yana yawo a kan screen ɗin wayar, mamaki al'ajabi haɗe da faɗuwar gaba suka dirar mata lokaci guda, tana tuna cewa jiya da dare ma har sun kwanta sai da ta ga MAMAUDAN nan ya kira shi, ƙarshe ya ce mata zai fita ya siyo panadol jikinsa yana masa zafi, da haka ta manta da maganar kiran tun da tun kiran farko ba a sake kira ba.

Ita kuma jin ya ce jikinsa yana zafi sai tausayinsa ya kamata, ta manta batun kiran MAMUDA. Yanzu ma sai ta fara tunanin dalilin da ya sa shi MAMAUDA zai ke kiransa koyaushe, duk da MAMAUDA ba suna mace bane amma dai ta É—an shiga shakku da taraddadi.
Chapter 30 · 0% Book details