Sashe 22
Kazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
'Allah ka fitar da ni, Allah ka rufa mini asiri kar wannan masifafiyar ta gano ni... Bai gama addu'ar ba ganin ta ƙaraso gabansa kamar an jefo ta sai ya ɗago kai yana kallon yadda take huci kamar wacce ta yi tseran gudu ya ce
"Ai ni blocking ɗin lambarsa ma zan yi in goge ta, yo ina dalili zai ke damuwa ina gida da iyalai na" Tana tsaye a kansa kiran ya sake shigowa MAMUDA shi ne abin da ta ga an rubuta da manyan baƙi, ajiyar zuciya ta sauke ganin sunan namiji har ta ji salama a ranta sai dai hanzari ba gudu ba yadda ƙwaƙwalwarta ta kai mata cewa kaf cikin abokansa bata san wani MAMUDA ba. Kallon tuhuma ta masa ta ce
"Daga kira ko É—agawa baka yi ba, sai ka ce wani blockin da goge lamba anya kana da gaskiya kuwa?" Wannan tambayar da ta masa shi ya sa shi saurin cewa
"Bari na É—aga na faÉ—a masa bani da kuÉ—in" Wani É—an sanyi ta ji a ranta, don har ta yarda da shi ta ce
"Yawwa É—auki amma ka saka a handsfree" Kallon ta ya yi ya ce
"Haka kawai kina matar aure sai na kunna miki muryar gardi ki ji" Ya faÉ—a yana muzurai da son nuna mata kishinta yake yi, É—an kallonsa ta yi tana mai nazartarsa ta ce
"Ikon Allah, in ce dai muryar mace ce take haramun namiji ya ji, kenan yaushe muryar namiji ma ta zama al'aura?" Ta faɗa tana kaiwa wayar hannunsa farmaki, janyewa ya yi yana sakin yaƙe tare da wayincewa ya ce
"Yo ai ni bana son kike jin muryar wani ƙato sai tawa" Wani daɗi ta ji don ita dai maganar soyayya ce rashin aikin yi da ɓata lokaci amma dai in dai fagen kishi ne to ita ce lamba ɗaya.
Sai da ya gama saƙa abin da zai ce sannan ya ɗaga wayar gabansa yana faɗuwa, don ya san ko kiran nan da Salaha budurwarsa ce da suke shan soyayya, ya san yanzu ta ƙufula tun da har katse kiran ya yi, sannan tana ta kira bai ɗauka ba, sannan babban abin ma bai taɓa faɗa mata yana da aure ba saboda ita ɗin ma ya lura tana da mugun kishi, shi kuma wannan ce ƙaddararsa wato mata masu kishin jaraba wanda ya wuce hankali.
Yana tuna irin rikicin da zai shiga a wajen Salaha, in ya kira ta da MAMUDA amma haka ya daure don da wata masifar gwara wata, da ya shiga tashin hankalin Amina ta san budurwarsa ce take kiransa gwara Salahar duk bala'i dai a waya za ta masa ko in ya je wajenta zance, yana ɗagawa idanunsa a kan Amina da ta kasa ta tsare, taimakonsa da Allah ya yi volume ɗin wayar ba a ƙure yake ba, bare ta ji muryar mai magana. Yana kai wayar kunnensa Salaha cikin shagwaɓaɓɓiyar muryarta mai kashe masa jiki da saka shi yin nutso a kogin ƙauna ta ce
"Hello haba babynah tun... Ya san dai bai wuce ƙorafi bane za ta masa a kan ƙin ɗaga wayar da wuri amma haka ya yi ƙundunbala ya ce
"Haba MAMUDA in ce dai mun gama magaa da kai, na ce maka bani da kuɗi amma ka dage kana ta kirana, shin a inanka taɓa gani an bada babu?" Salaha da sauri ta cire wayar a kunneta tana ƙara duba sunan wanda ta kira, duk da ta ji tabbas! Muryar Sule saurayinta ne amma kuma yadda ya amsa mata yana kiranta da sunan namiji wai MAMUDA bayan kuma ita ta fara yin magana, da a ce shi ya kira ta sai ta ce ko bai san ya kira ba.
Amina kuwa jin abin da ya ce, sai ta ji ta ƙara yarda da shi, tana sakin wani murmushi sai kallonsa take ya cigaba da faɗin.
"Don Allah ka nema a wani wajen" Salaha kuka ne kawai bata saki ba amma ranta ya yi mugun ɓaci, ta buɗe baki za ta fara zazzaga masa rashin mutunci ta ji ƙit ya kashe kiran, shi kuma da ya katse kiran bai ɗauke yatsansa ba sai da ya tabbatar ya kashe wayar gabaɗaya, don Amina tana ganin ya sauke wayar daga kunnensa ta koma mazauninta don haka bata ma lura cewa ya kashe wayar ba.
Salaha kuwa a zuciye ta ƙara kiransa, don ta sauke masa kwandon rashin mutunci, amma sai ta ji wayar ma a kashe. Wurgi ta yi da wayar a kan gadonta da take kwance, zuciyarta tana ƙuna don ita ta fara tunanin ko dai Sule wata budurwar ya sake shi ne yana gaban waccen ɗin ita ya maida ta MAMUDA.
Sule kuwa tun da ya kashe wayar nan, hankalinsa bai kwanta ba gabaÉ—aya hankalinsa, yana wajen Salaharsa, yanzu kuma bai san ya zai yi ya fita su yi waya ya kwantar mata da hankali ba, ya mata bayani hakan ya sa ya É—an kalli Amina ya ce
"Ni yaran nan duka sun yi bacci?" Bata É—ago ta kalle shi ba ta ce
"Eh duka sun yi bacci, kaima ka san da basu yi bacci ba da tuni suna nan" Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ya ce
"Ɗan haɗa mini ruwan shayi mai zafi sosai" Ɗan yatsina fuska ta yi don bata son tashi sai kuma ta tuna lipton ta ƙare cikin zaƙuwa ta ce masa
"Babu lipton fa" Wani murmushin gefen baki ya saki, don dama abin da yake hasashe kenan, shi ya sa ma ya ce a haɗa shayin, wani ƙaramin tsaki ya saki irin na kamar ba ya son ya fita sai ya ce
"Bana son fita, ga shi kuma ina son shan shayin" Kallonsa ta yi ta ce
"To ka fita shagon ƙofar gida ka siyo mana" Wani daɗi ne ya cika ransa ya tashi kamar ba ya so, yana riƙe da wayarsa ɗaya hannun kuma yana taɓa aljihu ya ce
"Bari na karɓo" Ya bata baya ya nufi ƙofar fita, sai murmushi yake matar sauti kamar daga sama sai ya ji ta ce
"Ɗan aramin wayarka, zan yi wani abu, ntwrk ɗina yana ɗaukewa, kafin ka dawo" Idanu ya zaro duk da bata gani, yana jin ta ruguza masa gabaɗaya shirin fita ya lallashi Salaha, ba a nan gizo yake saƙar ba ma, idan ta ga wayar a kashe sai ta tuhume shi dalilin hakan, wannan zai sanya ta zargi cewa da walakin goro a miya, ida kuwa hakan ta faru ya san tana buɗe wayar abu na farko da za ta fara yi shi ne kiran lambar nan mai ɗauke da sunan MAMUDA, cakwakiyar da zai shiga Allah ne kaɗai ya sani, don idan ta kira lambar MAMUDA Salaha za ta ɗauka, kowacce za ta ji muryar ƴar uwarta, da wane baki zai warware wannan badaƙalar, sannan ya san ma bai isa ya hana ta aron wayar ba, saboda hanawar ma wani sabon zargin ne.
Salaha bata san yana da mata ba har da yara biyu, ga shi ta ƙwallafa rai a kansa tana son aurensa, shi ma a nashi ɓangaren haka ne yana son ta da aure, amma yadda ya lura tana da tsananin kishi shi ya sa bai sanar da ita ba, ya bari sai abu ya zo dab amma gashi yau Amina za ta warware masa ƙullin da ya ƙulla. Sannan ita ma Amina bata san ma yana da wata budurwa da yake soyayya da ita ba, ita da kullin burinta ya dawwama da ita kaɗai a rayuwarsa bs tare da kishiya ba, kuma sai yake ɗora ta a kan cewa daga ita babu ƙari kuma duk da mugun kishinta amma yau da alama asirinsa yana dab da tonuwa, wannan shi ake kira rana zafi inuwa ƙuna.
*SUMAYYA*
Zaune take a bakin gado, tana ɗaure da zani ɗaurin ƙirji, Yaya Shafi'u ne ya shigo yana kallonta wani ɓacin rai ya turnuƙe shi, haka ya danne ya ce
"Ranke daɗe Hajia Sumayya" Wani kallon sheƙeƙe ta masa, don ta san wannan maganar da biyu ya faɗa ta ce
"Faɗi da ihu ka ƙara da wayyo, na san dai duk ranar da Allah ya kira ni babu wanda zai hana, don haka sai dai in ce Allah sa ka faɗa da bakin mala'iku" Kallonsa ya mayar kan Ruma da ta taso ta nufo shi za ta kama shi, da sauri ya riƙe hannun yarinyar don kar ta daƙuma masa kayansa ya ce
"Sumayya don Allah kalli yarinyar nan, wallahi wannan ko ƙauye aka je sai an bincika za a samu wanda zai bar ƴarsa a haka dagaje-dagaje da ƙazanta, kalli kwantsa a idanunsa, hanci duk majina, hannunta ta ci abinci duk manja ba a wanke mata ba, sannan shi kansa kayan jikinta babu tsaftacewa. Yanzu a haka kike ganin in ta girma ita ta tsafta ce jikinta bayan uwar da ta haife ta bata tsafta mata ba, duk abin da ake wa yaro shi yake kowa, kalli wandonta Allah kaɗai ya san adadin maimaicin da aka masa" Ya kai ƙarshen maganar yana ɗagowa ya kalleta jin bata ce komai ba, ganin ta zuba masa ido tana wani jijjiga jiki ya san kalamansa basu samu shiga ba, bare su samu matsugunni. Kallon ɗaya saura kwata ta masa ta ce
"Ka gama? Na ce ka gama? Sau nawa kake so na maimata maka cewar duk wanda ya raina tsayuwar wata hawa yake ya gyara ba, kullum magana ɗaya kamar karatu yanyanyanyan tun da ba ɗauka zan yi ba ya kamata ka haƙura ya shafa mini lafiya" Ta kai ƙarshen maganar taba sakin wata gyatsa, da alama ta yi over feeding saboda shegen ci kamar gara.
Hannun Ruma ya kama ya fita da ita, wanka mata hannun ya yi ya dawo da ita ɗakin ya cire mata kaya, banɗaki ya shiga zai mata wanka, pant ɗin Sumayya ya gani rataye babu wanki abin haushin ma jinin period ne a jiki amma saboda tsabagen ƙazanta ba za ta wanke ba ta rataye a haka.
"Ai ni blocking ɗin lambarsa ma zan yi in goge ta, yo ina dalili zai ke damuwa ina gida da iyalai na" Tana tsaye a kansa kiran ya sake shigowa MAMUDA shi ne abin da ta ga an rubuta da manyan baƙi, ajiyar zuciya ta sauke ganin sunan namiji har ta ji salama a ranta sai dai hanzari ba gudu ba yadda ƙwaƙwalwarta ta kai mata cewa kaf cikin abokansa bata san wani MAMUDA ba. Kallon tuhuma ta masa ta ce
"Daga kira ko É—agawa baka yi ba, sai ka ce wani blockin da goge lamba anya kana da gaskiya kuwa?" Wannan tambayar da ta masa shi ya sa shi saurin cewa
"Bari na É—aga na faÉ—a masa bani da kuÉ—in" Wani É—an sanyi ta ji a ranta, don har ta yarda da shi ta ce
"Yawwa É—auki amma ka saka a handsfree" Kallon ta ya yi ya ce
"Haka kawai kina matar aure sai na kunna miki muryar gardi ki ji" Ya faÉ—a yana muzurai da son nuna mata kishinta yake yi, É—an kallonsa ta yi tana mai nazartarsa ta ce
"Ikon Allah, in ce dai muryar mace ce take haramun namiji ya ji, kenan yaushe muryar namiji ma ta zama al'aura?" Ta faɗa tana kaiwa wayar hannunsa farmaki, janyewa ya yi yana sakin yaƙe tare da wayincewa ya ce
"Yo ai ni bana son kike jin muryar wani ƙato sai tawa" Wani daɗi ta ji don ita dai maganar soyayya ce rashin aikin yi da ɓata lokaci amma dai in dai fagen kishi ne to ita ce lamba ɗaya.
Sai da ya gama saƙa abin da zai ce sannan ya ɗaga wayar gabansa yana faɗuwa, don ya san ko kiran nan da Salaha budurwarsa ce da suke shan soyayya, ya san yanzu ta ƙufula tun da har katse kiran ya yi, sannan tana ta kira bai ɗauka ba, sannan babban abin ma bai taɓa faɗa mata yana da aure ba saboda ita ɗin ma ya lura tana da mugun kishi, shi kuma wannan ce ƙaddararsa wato mata masu kishin jaraba wanda ya wuce hankali.
Yana tuna irin rikicin da zai shiga a wajen Salaha, in ya kira ta da MAMUDA amma haka ya daure don da wata masifar gwara wata, da ya shiga tashin hankalin Amina ta san budurwarsa ce take kiransa gwara Salahar duk bala'i dai a waya za ta masa ko in ya je wajenta zance, yana ɗagawa idanunsa a kan Amina da ta kasa ta tsare, taimakonsa da Allah ya yi volume ɗin wayar ba a ƙure yake ba, bare ta ji muryar mai magana. Yana kai wayar kunnensa Salaha cikin shagwaɓaɓɓiyar muryarta mai kashe masa jiki da saka shi yin nutso a kogin ƙauna ta ce
"Hello haba babynah tun... Ya san dai bai wuce ƙorafi bane za ta masa a kan ƙin ɗaga wayar da wuri amma haka ya yi ƙundunbala ya ce
"Haba MAMUDA in ce dai mun gama magaa da kai, na ce maka bani da kuɗi amma ka dage kana ta kirana, shin a inanka taɓa gani an bada babu?" Salaha da sauri ta cire wayar a kunneta tana ƙara duba sunan wanda ta kira, duk da ta ji tabbas! Muryar Sule saurayinta ne amma kuma yadda ya amsa mata yana kiranta da sunan namiji wai MAMUDA bayan kuma ita ta fara yin magana, da a ce shi ya kira ta sai ta ce ko bai san ya kira ba.
Amina kuwa jin abin da ya ce, sai ta ji ta ƙara yarda da shi, tana sakin wani murmushi sai kallonsa take ya cigaba da faɗin.
"Don Allah ka nema a wani wajen" Salaha kuka ne kawai bata saki ba amma ranta ya yi mugun ɓaci, ta buɗe baki za ta fara zazzaga masa rashin mutunci ta ji ƙit ya kashe kiran, shi kuma da ya katse kiran bai ɗauke yatsansa ba sai da ya tabbatar ya kashe wayar gabaɗaya, don Amina tana ganin ya sauke wayar daga kunnensa ta koma mazauninta don haka bata ma lura cewa ya kashe wayar ba.
Salaha kuwa a zuciye ta ƙara kiransa, don ta sauke masa kwandon rashin mutunci, amma sai ta ji wayar ma a kashe. Wurgi ta yi da wayar a kan gadonta da take kwance, zuciyarta tana ƙuna don ita ta fara tunanin ko dai Sule wata budurwar ya sake shi ne yana gaban waccen ɗin ita ya maida ta MAMUDA.
Sule kuwa tun da ya kashe wayar nan, hankalinsa bai kwanta ba gabaÉ—aya hankalinsa, yana wajen Salaharsa, yanzu kuma bai san ya zai yi ya fita su yi waya ya kwantar mata da hankali ba, ya mata bayani hakan ya sa ya É—an kalli Amina ya ce
"Ni yaran nan duka sun yi bacci?" Bata É—ago ta kalle shi ba ta ce
"Eh duka sun yi bacci, kaima ka san da basu yi bacci ba da tuni suna nan" Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ya ce
"Ɗan haɗa mini ruwan shayi mai zafi sosai" Ɗan yatsina fuska ta yi don bata son tashi sai kuma ta tuna lipton ta ƙare cikin zaƙuwa ta ce masa
"Babu lipton fa" Wani murmushin gefen baki ya saki, don dama abin da yake hasashe kenan, shi ya sa ma ya ce a haɗa shayin, wani ƙaramin tsaki ya saki irin na kamar ba ya son ya fita sai ya ce
"Bana son fita, ga shi kuma ina son shan shayin" Kallonsa ta yi ta ce
"To ka fita shagon ƙofar gida ka siyo mana" Wani daɗi ne ya cika ransa ya tashi kamar ba ya so, yana riƙe da wayarsa ɗaya hannun kuma yana taɓa aljihu ya ce
"Bari na karɓo" Ya bata baya ya nufi ƙofar fita, sai murmushi yake matar sauti kamar daga sama sai ya ji ta ce
"Ɗan aramin wayarka, zan yi wani abu, ntwrk ɗina yana ɗaukewa, kafin ka dawo" Idanu ya zaro duk da bata gani, yana jin ta ruguza masa gabaɗaya shirin fita ya lallashi Salaha, ba a nan gizo yake saƙar ba ma, idan ta ga wayar a kashe sai ta tuhume shi dalilin hakan, wannan zai sanya ta zargi cewa da walakin goro a miya, ida kuwa hakan ta faru ya san tana buɗe wayar abu na farko da za ta fara yi shi ne kiran lambar nan mai ɗauke da sunan MAMUDA, cakwakiyar da zai shiga Allah ne kaɗai ya sani, don idan ta kira lambar MAMUDA Salaha za ta ɗauka, kowacce za ta ji muryar ƴar uwarta, da wane baki zai warware wannan badaƙalar, sannan ya san ma bai isa ya hana ta aron wayar ba, saboda hanawar ma wani sabon zargin ne.
Salaha bata san yana da mata ba har da yara biyu, ga shi ta ƙwallafa rai a kansa tana son aurensa, shi ma a nashi ɓangaren haka ne yana son ta da aure, amma yadda ya lura tana da tsananin kishi shi ya sa bai sanar da ita ba, ya bari sai abu ya zo dab amma gashi yau Amina za ta warware masa ƙullin da ya ƙulla. Sannan ita ma Amina bata san ma yana da wata budurwa da yake soyayya da ita ba, ita da kullin burinta ya dawwama da ita kaɗai a rayuwarsa bs tare da kishiya ba, kuma sai yake ɗora ta a kan cewa daga ita babu ƙari kuma duk da mugun kishinta amma yau da alama asirinsa yana dab da tonuwa, wannan shi ake kira rana zafi inuwa ƙuna.
*SUMAYYA*
Zaune take a bakin gado, tana ɗaure da zani ɗaurin ƙirji, Yaya Shafi'u ne ya shigo yana kallonta wani ɓacin rai ya turnuƙe shi, haka ya danne ya ce
"Ranke daɗe Hajia Sumayya" Wani kallon sheƙeƙe ta masa, don ta san wannan maganar da biyu ya faɗa ta ce
"Faɗi da ihu ka ƙara da wayyo, na san dai duk ranar da Allah ya kira ni babu wanda zai hana, don haka sai dai in ce Allah sa ka faɗa da bakin mala'iku" Kallonsa ya mayar kan Ruma da ta taso ta nufo shi za ta kama shi, da sauri ya riƙe hannun yarinyar don kar ta daƙuma masa kayansa ya ce
"Sumayya don Allah kalli yarinyar nan, wallahi wannan ko ƙauye aka je sai an bincika za a samu wanda zai bar ƴarsa a haka dagaje-dagaje da ƙazanta, kalli kwantsa a idanunsa, hanci duk majina, hannunta ta ci abinci duk manja ba a wanke mata ba, sannan shi kansa kayan jikinta babu tsaftacewa. Yanzu a haka kike ganin in ta girma ita ta tsafta ce jikinta bayan uwar da ta haife ta bata tsafta mata ba, duk abin da ake wa yaro shi yake kowa, kalli wandonta Allah kaɗai ya san adadin maimaicin da aka masa" Ya kai ƙarshen maganar yana ɗagowa ya kalleta jin bata ce komai ba, ganin ta zuba masa ido tana wani jijjiga jiki ya san kalamansa basu samu shiga ba, bare su samu matsugunni. Kallon ɗaya saura kwata ta masa ta ce
"Ka gama? Na ce ka gama? Sau nawa kake so na maimata maka cewar duk wanda ya raina tsayuwar wata hawa yake ya gyara ba, kullum magana ɗaya kamar karatu yanyanyanyan tun da ba ɗauka zan yi ba ya kamata ka haƙura ya shafa mini lafiya" Ta kai ƙarshen maganar taba sakin wata gyatsa, da alama ta yi over feeding saboda shegen ci kamar gara.
Hannun Ruma ya kama ya fita da ita, wanka mata hannun ya yi ya dawo da ita ɗakin ya cire mata kaya, banɗaki ya shiga zai mata wanka, pant ɗin Sumayya ya gani rataye babu wanki abin haushin ma jinin period ne a jiki amma saboda tsabagen ƙazanta ba za ta wanke ba ta rataye a haka.