← Book details Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 19

Sashe 9

Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Ai in Gaya Miki Aisha Mata na ganin tasku a Duniya Kar ma ace Allah yayiwa mijinki Rasuwa wayyo Allah na taba SHIGA wannan siradin na Rantse Miki da Allah aduk yawan yan uwan mijina aka Rasa samun zakaran da zai tallafa min da kwayar hatsi ke sai a shekara ma ban saka dayan su idons ba ga Yara har biyar baccin Sana a ta ai da Asiri ya tonu shiyasa yanzu da Naga baiwar Allah Nan tana Jan mota sai tausayin ta ya kamani don nasan akwai wani Al amari da ya sata hakan

Ammi tayi murmushi daidai da ta kawo su bakin babbar kasuwar central market ta gyara parking suka fito suna Miko Mata kudin ta suna Kuma binta da ADDU A ta fatan ALHERI ga Kuma kiyayewar Ubangiji ta karba tana godiya ban San lokacin da HAWAYE ya balle min ba na kife kaina a cinya ta Ina kuka inda najiyo Ammi na min magana cikin sanyin murya ..............

Labarin GARWASHI na kudine ga duk me bukatar Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669

Labarin daban yake da sauran Kar ku Bari ayi Babu ku

Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERI💃🏿
🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤

🍒🍒🍒 GARWASHI🍒🍒🍒
Page
17//18
Hadiza Bara'u Gidan iko

Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne

Sadaukarwa ga daukacin ZURIAR dake Rike zumunci tsakanin su da Allah ba don abinda suka hango ba ko Wanda zasu samu don yanzu zumunci ya zamo jari hujja

Gaisuwar girmama ga Haj Saliha Abubakar Abdullahi Zaria

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

............Muryar Ammi najiyo akaina cikin wata murya da na Gama fahimtar cikin Hali tayi maganar

"Kiyi hakuri Zahra komai Kika ga ya faru ga bawa Rubutacce ne bawa Kuma Bai Isa ya sauya shi ba. In ba Allah ba wa ya Isa yayi hakan? Nasan kinajin zafina Akan wannan hanyar da na dauko wadda nake ganin itace mafita Domin ko ya zame min Dole na tashi na Kare mutuncin ku tunda Dani a cikin Wanda sukayi sanadin zuwan ku Duniya Ashe ko ya Zama Dole na SHIGA na fita don ganin ba kuyi kukan Rasa wani Abu ba . Ba Zan sake Barin Abdullahi ya komawa aikin Nan Mai wahala ba nice ya kamata nayi tukin mota Amma ba fita garuruwa ba iyakata Nan cikin gari kawai na Kuma yi Miki alkawarin Kare mutunci na da naku in Sha Allah duk Runtsi duk wuya inaji ajikina Zahra akwai lokacin da komai zai zamo tarihi kamar ba ayi ba don Haka Daina kuka kinji ? ADDU A nake Rokon kiyi min Allah ya tsare Ni sharrin karfe da Kuma sharrin mutum da aljan

"Ammi ba haushin ki nakeji ba illa tausayin ki Ammi ban taba ganin mace na tukin taxi ba shiyasa nake tausaya Miki Kar kema wahala tayi Miki yawa irin wadda ta riski Yaya Abdullahi.....

"Babu komai Zahra Allah ya Rufa min Asiri don na lura Ubangiji ya saka min nasibi don kusan Dubu biyar na samu bayan na fidda Dubu biyun Mai da na siya kinga sai mu biya haj ladi kudin ta abinda na samo gobe Kuma sai mu siyo abinci mu aje in Sha Allah wahalar mu ma tazo karshe

Haka kuwa Ammi ta zage fita Aikin tuki Kuma tana samo kudi sosai inda na Gane shi Ubangiji da ka tashi da nufin kana son ya taimake ka to zai kuwa taimake ka sai dai Kuma Yaya Abdullahi dake kwance Bai San hakan ba Kuma ammi tace Kar mu sanar dashi don da yaji ba zai yarda ba Kuma gashi ba lafiya gareshi ba

Tuni aka biya haj ladi kudin hayarta muka zauna lafiya har ma Ammi ta samu kudin da ta siyawa Yaya Abdullahi magani ta Kuma siya Mana kayan abinci Wanda Rayuwa ta koya Mana cin dangogin su Wanda bamu waye su ba amma dole muka Saba tun muna ci cikin mu na baci muyi ta zawayi har muka Saba daga wannan sabon sauyin zuwa Wanda Muka sani muka Kuma Saba

Jikin Yaya Abdullahi yayi sauki har ya Soma tambayar kanshi yawan fitar da ammi takeyi Amma dai Bai tambaye ta ba Bai Kuma tambayi kowa ba inda a yau ya fito waje Yana zaune Yana kallon yadda mutane ke ta Kai kawon su kawai sai yaga Ammi ta shawo kwana cikin motar da aka mayar taxi Kuma ga Alama kamar garin take zaga wa

Ya taso ya karaso daidai da tafito Rike da ledar da ta siyo Dan Raba Mana dangin makulashe ya karbi ledar suka shigo ciki Yana mata sannu da Zuwa ita Kuma tana murnar ganin ya Soma fitowa waje Alamar sauki ya samu

"Iska kake Sha ne Abdullahi? Masha Allah Allah ya Kara lafiya kaji ? Ya amsa da Ameen Ammi Amma ya Naga motar Nan anyi Mata fentin taxi? Ya fada Yana kallon Ammi wadda ta shiryawa tambayar tashi
"Sai dai kuyi hakuri Abdullahi Amma ai ya Zama Dole na Mike tsaye don na ga Baku yi kukan Rashi ba in kun Rasa Uba jajirtacce to tabbas Baku Rasa jajirtacciyar mahaifiya ba don Haka Kai ma inaga makaranta ya kamata ka koma don yadda na samu sa ar Nan abubuwa suna tafiyar min yadda ya Dace kaima na yanke shawarar ka koma karatu kawai.......

Ya Soma kada kanshi Alamar A a ba zai iya Barin ta da wannan dawainiyar ba. ......

"Ammi nine fa Ubangiji ya baku don kuyi alfahari da haihuwa ta . Nine Wanda Ubangiji ya kawo muku don na dauki takalifin ku keda Daddyn mu da Kuma kanne na to tunda Ubangiji Bai yarda Daddyn yaga Haka ba sai ke don me Zan Bari kiyi ta wahala Haka ? Don Haka don Allah don Annabi kiyi hakuri da fitar Nan nine Zan fita na Nemo muku duk abinda kuke so tunda na samu lafiya dama sai da wani ya fada min ulcer ce ke neman kamani da na fada mishi abinda nakeji shi Kuma yace akwai maganin Hausa da zai bani Zan Rabu da ita Yana a funtua ne in naje Zan neme shi ya bani shikenan Ammi don Allah don Annabi kar kice A a idan Kika ce a a kamar Baki yarda Zan zamo Miko abin alfahari ba....

Ammi bata yarda ba daga farko don cewa tayi bashi da lafiya ya Bari ya Kara samun sauki tukuna shi Kuma ya CE baya son yaga tana fitan ne don Haka ta hakura da fita shi Kuma ya zauna zaman shanye maganin shi kafin ya koma bakin aiki

Sati guda Daya Tak ya koma aiki inda Ni da kaina naji gaskiya bana son aikin Nan na Yaya Abdullahi hankali na ya Fi kwanciya Akan na ammi ban San Dalili ba ko da Yake dalilin ba zai wuce na kaddara ba wadda Ubangiji ke darsawa wasu Jin wani Abu da zasu yarda dashi ko Akasin hakan Wanda matukar suka bibiyi abin Nan da Basu yarda dashi ba sannu a hankali sai su Tara's da kaddara acikin shi kaddara kuma me ciwo a zuciya

Aikin Yaya Abdullahi ya Dore don yanzu har wata Yar kiba ya somayi bayan ya karbo maganin ulcer ya Kuma yi amfani dashi har ya warke daga cutar ulcer harkokin shi suka tafi daidai komai namu ya tafi daidai kamar dai irin Rayuwar da ta samemu a tsakar Rana guda Daya Tak

A dangin mahaifina kuwa shiru babu Wanda ya neme mu bare yaji ya muke Rayuwa ya muka Fadi ya muka tashi ko da Yake naso na yaudari kaina idan nace so nake Wai wani yazo da sunan duba mu ai ko a mafarki naga hakan Zan karyata suna wurin su muna namu sai ma Nana CE ke fada min wai Yan uwan Daddy sunzo Kan maganar gidan mu har ma sun saida shi Wanda ya siye shi ma yace Rushe shi zaiyi ya sake sabon Gini

Kasancewar makarantar mu daya da nana ta gidan mama kusan ma itace kawata ta kusa kusa don a tare ake kaimu makaranta a wani lokaci can da ya Jima da shafewar tarihin shi
Wannan magana ta Nana ta kadani ba kadan ba don da nadawo gida ma sai da na sanarwa ammi abinda nanar ta fada min

"To ya za ayi Zahra in ma Basu saida shi yanzu ba zasu saida shi Nan gaba Allah ya Baku mafiyin abinda kuka Rasa Ina Rokon Allah yayi muku gata fiye da Wanda mahaifin ku yayi nufin yi muku na amsa da Ameen ya Rabbil Alamin
Chapter 9 · 0% Book details