Sashe 11
Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fatan ALHERI ga Uwa ta haj Sa adatu lawal Ade Allah ya Kara sutura da lafiya
Kyautar wa ga iyalan haj Saliha Abubakar Abdullahi Zaria mazan su da Matan su Allah ya daga lamarin ku
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
............."Ba Zaki Rabu da masu sallah ba ko? Bance Miki Kar ki kuma Zama kusa dasu ba? Ta fada tana zaro min idanu inda nake turo Baki gaba Ashe bansani ba na Kara bawa Amaka haushi sai kawai naji ta zaune Ni akaina da manyan kuturanta Wai naji nauyin ta akaina
Ta kuwa zaune Ni Tana fadin "Ai tunda dai na Raba ki da mutanen Nan mayaaudara masu tallatawa mutane Addinin su ko Bai nema ba matukar Baki Rabu da mu Amala dasu ba to Zan saka wuka in yanke kine matukar na karajin kinyi magana da masu salla
Sai da ta gaji don kanta kafin ta daga Ni Amma ko kadan banji Ina son in Rabu da kawaye na ba sai dai duk yadda Amaka zatayi sai dai tayi
Haka na ci gaba da Rayuwa cikin ukubar matsalar jinnu sai dai duk Ranar da ciwon ya motsa sai dai mu tare a Asibiti mu Kashi kudi mu dawo
A lokacin da na Gama karatu Maazi Nkem ya siya min mota me tsada na Soma SHIGA gari a kuma wannan lokacin ne na some tsanar zuwa coci inda Amaka ke Mika kokon barar ta ga malaman cocin Akan ciwona inda ake ta min ADDU A yayin da Maazi Nkem Yake bada kyautar kudi da Kaya ana kawowa coci yayin da Ni Kuma naji kwata kwata bana son zuwa cocin a duk Ranar lahadi Amaka Kan tusa Ni gaba muje wani lokacin ma a mota ta muke zuwa inda Kuma na Soma kalula da karyar ciwona tun Amaka Bata farga ba har dai ta gane son zuwa ne banayi ta Kuma ce ban Isa ba bisa Dole take tasani gaba muje Amma da mun Isa sai na fakaici idon ta sulale na bar cocin na koma gida
A cikin wannan lokacin ne Kuma na samu adimition din jama ar Legos a matakin farko inda Kuma muka sake hadewa da kawaye na na baya wato sumayya Ahmed yabo da fauziyya Yar Amana muka sake kullewa fiye da Baya
Zuwa wannan lokacin na farajin Ina Sha awar irin kayan da suke sakawa musamman hijabi da dogayen Raguna amma na San ko giyar wake Nasha ban Isa na Kai su gida ba bare Amaka ta gani bare na kaisu jikina
Na dubi sumayya bayan mun fito daga lacca nake duban ta cikin Sha awar shigar ta ta atamfa da katon hijabi harma da Nikabi
"Wai sumayya kin taba fada min ciwona bana Asibiti bane na Alkur ani ne ko? Tace Eh haka ne Justina hakan NE kawai zakuyi ki Rabu da ciwon ki don aljanu ne fa suke shigar mutum Kuma sunfi shigar Mata mafi yawan lokuta Matan dake yawan Zama babu Dan kwali ko Babu suturar kirki Suma Wai Sha awar Matan suke ku Kuma ba zaku iya saka irin kayan mu ba
Nace
"To Ni yanzu yaya zanyi da Alkur ani in warke ne sakawa ake a Ruwa koko yawo Zan Rika yi dashi? Sumayya tayi Dariya tana fadin
"A a karanta Miki za ayi sai kiga kin samu sauki Amma fa sai Allah ya yarda kinsan komai Allah ne ke yin shi
Nayi shiru don nasan Amaka ba zata yarda da hakan ba Dole nayi shiru Amma a Raina Ina tunanin Yaya za ayi ayi min karatu?
Haka na kasance Ina ta fama da ciwo in ya tashi Nasha maganin bature in Kuma lahadi tayi na sulale Amaka tayi ta Sababi tana fadin ba zanje ayi min ADDU A ba to Allah yasa asake wata lahadin bakije ba kiga abinda zai faru
Ban damu ba Ni fatana kawai na samu Wanda zaiyi min karatun Nan don kullum abin ci gaba yake akasin da nake kwanciya ciwo yanzu bugeni ake na Fadi tamkar matacciya magani kuwa babu Wanda ba a Nemo min ba Amma babu wani ci gaba
Mun Isa jihar imo inda ake bikin Yar sarkin imo wanda ya kasance sarkin garin mu Kuma Wanda Maazi Nkem Yake matukar girmamawa tamkar ya duka ya bi ta kanshi ya wuce . Wannan girmamawa da Maazi Nkem yakewa sarki yasa suke matukar mutunci Wanda Nima na samu SHIGA a gidan nashi harma na zamo kawar onye wato Amarya don Haka da bikin ya tashi Maazi Nkem ya kwashemu har Amaka muka tafi halartar bikin gidan sarauta a jihar imo
Kai tsaye fadar sarki muka Fara Isa mukayi gaisuwa inda sarki ya dafa kaina Yana yabawa kyauwuna Yana Kuma yi min ADDU A cikin yabawa da nuna kauna
Aka Soma gudanar da shagalin biki irin na gidan sarauta inda Amaka ke can wurin matar sarki suna ta gudanar da nasu shagalin Nima Ina cikin su onye amarya wadda na ji Wai Dan sarkin aber ne zata Aura
Duk wasu Kaya na shagalin bikin an tanade su an Kuma Rabawa mahalar ta bikin Wanda Nima na samu kasona na wata Riga doguwa Mai hannun shime wadda aka Dan Rufe kirjin ta da wani less me shara shara Kuma aka tsuke kasan ta ta yadda ta bayyana kuturin Wanda ya sakata
Wurin da za ayi taron katon filine Wanda ya ke a cikin gidan sarautar inda Kuma aka hada wasu manyan manyan itace aka hada wuta tana ci ganga ganga . Shi dai wannan taron sunan shi agare amarya ce za a bawa namijin tantabara shi Kuma Angon abashi macen tantabara su fito fili inda wutar Nan take ci idan Amarya ta taba sanin wani namijn kafin Angon nata to tantabarin hannunta zai mutu idan kuwa Bata taba sani kowa ba to na tantabarar hannun Angon nata zata mutu..............
Labarin GARWASHI na kudine ga duk me son Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669
Kar ku Bari ayi Babu ku don wannan Labari daban yake da sauran
Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERI💃🏿
🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤
🍒🍒🍒 GARWASHI🍒🍒🍒
Page
23//24
Hadiza Bara'u Gidan iko
Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne
Sadaukarwa ga iyayena guda biyu Uwa da Uba Allah kayi musu Rahama kasa su tabbatacci agidan ALJANNAH madaukakiya da dukkan musulmin duniya
Yabawa ga masoyan Rubutun Gidan iko musamman masu comment sannun ku da kokari son so 🥰
Tukwici ne ga Anty Amina maman muhmd da Anty A'smau maman maama
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
.............Muna tsaye a filin Ina hagun onye dake Rike da tantabarar ta yayin bici ke ke damanta yayin da shima Ango Peter yake tare da abokanshi yarima Gibson Yayan Amarya Wanda ya zuba min ido Yana kallo na abinda na tsana kenan
Hatta Ahalin gidan sarkin sun fito filin don su ga yadda Wannan taro zai Kare Amma fa fuskar Uwar Amaryar cikin tsoro da zullumi don in har ya kasance yarta ta taba sanin wani namijn to karshen abin kunya ne a garesu Kuma abin kunya ga sarki da Ahalin gidan sa ace Yar gidan shi ta lalace kafin Aure don Haka kowa ke cikin taraddadi domin ko in har aka samu akasi shima Angon ba zai taba Auren ta ba don Haka acikin filin ma ba iyayen Amaryar ne kawai ba har da Ahalin gidan su Ango Peter kowa zuciya na bugawa musamman uwar amarya
A gefe na kuwa bana tare da komai sai nishadi don bikin ya kayatar Dani Kuma wannan Al ada tana burgeni ko Babu komai dai zai zaburar da Yan Mata kame kansu ko don irin wannan Rana da suke gudun fallasa ban sani ba ko don Ina tare da kewaye hausawa ne masu nuna min watsewar da ake a Jami a da Kuma na cikin gida yasa wannan Al adar ta burgeni? Ko ko dai don bana Ra ayin watsewar ne ? Oho Amma Kuma da yawa daga cikin yaren namu suna tur da Allah wadai da wannan tonon Asiri don da dayawa daga cikin Yan Matan dake Rasa budurcin nasu su Samarin ne ke batasu da Romon bakan su zasu Aure su wasu Kuma Yan uwan su NE na jiki ke karbe musu budurcin da ko mu muke girmama matar da takawo wa mijinta shi a gidan shi batayi saken da ta Rasa shi tun a waje ba
Kuma shi wannan tonon Asirin ba Wai sai a irin gidan sarauta ake you shi ba ko a gidajen talakawa suna alfahari da shi don suna ganin hanyace da ake wanke zukata daga zargi Ango zai karbi matar shi babu zargin ta zaga yawo ko wani ya Rigashi samun budurcin da suke wa kulafuci. Suma Kuma iyayen ta zasu San Basu bawa yarsu tarbiyar banzaba kowa dai zai Gane Babu cuta a cikin Auren su bare zargi.
Sai dai Kuma a gefe guda akwai wata Al ada da akeyi ga Ya'yan gidan sarauta musamman namijin da ke jiran gado wato yarima shi Kam idan zaiyi Aure Koda kuwa Yar gidan talaka ce zai aura sai anyi wata banzar Al ada wadda nake tsinewa a Raina don ba karamin haushi take bani ba har nake ganin in da nice matar da yariman zai Aura ba Zan taba yarda ba sai dai komai zai faru ya faru
Kyautar wa ga iyalan haj Saliha Abubakar Abdullahi Zaria mazan su da Matan su Allah ya daga lamarin ku
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
............."Ba Zaki Rabu da masu sallah ba ko? Bance Miki Kar ki kuma Zama kusa dasu ba? Ta fada tana zaro min idanu inda nake turo Baki gaba Ashe bansani ba na Kara bawa Amaka haushi sai kawai naji ta zaune Ni akaina da manyan kuturanta Wai naji nauyin ta akaina
Ta kuwa zaune Ni Tana fadin "Ai tunda dai na Raba ki da mutanen Nan mayaaudara masu tallatawa mutane Addinin su ko Bai nema ba matukar Baki Rabu da mu Amala dasu ba to Zan saka wuka in yanke kine matukar na karajin kinyi magana da masu salla
Sai da ta gaji don kanta kafin ta daga Ni Amma ko kadan banji Ina son in Rabu da kawaye na ba sai dai duk yadda Amaka zatayi sai dai tayi
Haka na ci gaba da Rayuwa cikin ukubar matsalar jinnu sai dai duk Ranar da ciwon ya motsa sai dai mu tare a Asibiti mu Kashi kudi mu dawo
A lokacin da na Gama karatu Maazi Nkem ya siya min mota me tsada na Soma SHIGA gari a kuma wannan lokacin ne na some tsanar zuwa coci inda Amaka ke Mika kokon barar ta ga malaman cocin Akan ciwona inda ake ta min ADDU A yayin da Maazi Nkem Yake bada kyautar kudi da Kaya ana kawowa coci yayin da Ni Kuma naji kwata kwata bana son zuwa cocin a duk Ranar lahadi Amaka Kan tusa Ni gaba muje wani lokacin ma a mota ta muke zuwa inda Kuma na Soma kalula da karyar ciwona tun Amaka Bata farga ba har dai ta gane son zuwa ne banayi ta Kuma ce ban Isa ba bisa Dole take tasani gaba muje Amma da mun Isa sai na fakaici idon ta sulale na bar cocin na koma gida
A cikin wannan lokacin ne Kuma na samu adimition din jama ar Legos a matakin farko inda Kuma muka sake hadewa da kawaye na na baya wato sumayya Ahmed yabo da fauziyya Yar Amana muka sake kullewa fiye da Baya
Zuwa wannan lokacin na farajin Ina Sha awar irin kayan da suke sakawa musamman hijabi da dogayen Raguna amma na San ko giyar wake Nasha ban Isa na Kai su gida ba bare Amaka ta gani bare na kaisu jikina
Na dubi sumayya bayan mun fito daga lacca nake duban ta cikin Sha awar shigar ta ta atamfa da katon hijabi harma da Nikabi
"Wai sumayya kin taba fada min ciwona bana Asibiti bane na Alkur ani ne ko? Tace Eh haka ne Justina hakan NE kawai zakuyi ki Rabu da ciwon ki don aljanu ne fa suke shigar mutum Kuma sunfi shigar Mata mafi yawan lokuta Matan dake yawan Zama babu Dan kwali ko Babu suturar kirki Suma Wai Sha awar Matan suke ku Kuma ba zaku iya saka irin kayan mu ba
Nace
"To Ni yanzu yaya zanyi da Alkur ani in warke ne sakawa ake a Ruwa koko yawo Zan Rika yi dashi? Sumayya tayi Dariya tana fadin
"A a karanta Miki za ayi sai kiga kin samu sauki Amma fa sai Allah ya yarda kinsan komai Allah ne ke yin shi
Nayi shiru don nasan Amaka ba zata yarda da hakan ba Dole nayi shiru Amma a Raina Ina tunanin Yaya za ayi ayi min karatu?
Haka na kasance Ina ta fama da ciwo in ya tashi Nasha maganin bature in Kuma lahadi tayi na sulale Amaka tayi ta Sababi tana fadin ba zanje ayi min ADDU A ba to Allah yasa asake wata lahadin bakije ba kiga abinda zai faru
Ban damu ba Ni fatana kawai na samu Wanda zaiyi min karatun Nan don kullum abin ci gaba yake akasin da nake kwanciya ciwo yanzu bugeni ake na Fadi tamkar matacciya magani kuwa babu Wanda ba a Nemo min ba Amma babu wani ci gaba
Mun Isa jihar imo inda ake bikin Yar sarkin imo wanda ya kasance sarkin garin mu Kuma Wanda Maazi Nkem Yake matukar girmamawa tamkar ya duka ya bi ta kanshi ya wuce . Wannan girmamawa da Maazi Nkem yakewa sarki yasa suke matukar mutunci Wanda Nima na samu SHIGA a gidan nashi harma na zamo kawar onye wato Amarya don Haka da bikin ya tashi Maazi Nkem ya kwashemu har Amaka muka tafi halartar bikin gidan sarauta a jihar imo
Kai tsaye fadar sarki muka Fara Isa mukayi gaisuwa inda sarki ya dafa kaina Yana yabawa kyauwuna Yana Kuma yi min ADDU A cikin yabawa da nuna kauna
Aka Soma gudanar da shagalin biki irin na gidan sarauta inda Amaka ke can wurin matar sarki suna ta gudanar da nasu shagalin Nima Ina cikin su onye amarya wadda na ji Wai Dan sarkin aber ne zata Aura
Duk wasu Kaya na shagalin bikin an tanade su an Kuma Rabawa mahalar ta bikin Wanda Nima na samu kasona na wata Riga doguwa Mai hannun shime wadda aka Dan Rufe kirjin ta da wani less me shara shara Kuma aka tsuke kasan ta ta yadda ta bayyana kuturin Wanda ya sakata
Wurin da za ayi taron katon filine Wanda ya ke a cikin gidan sarautar inda Kuma aka hada wasu manyan manyan itace aka hada wuta tana ci ganga ganga . Shi dai wannan taron sunan shi agare amarya ce za a bawa namijin tantabara shi Kuma Angon abashi macen tantabara su fito fili inda wutar Nan take ci idan Amarya ta taba sanin wani namijn kafin Angon nata to tantabarin hannunta zai mutu idan kuwa Bata taba sani kowa ba to na tantabarar hannun Angon nata zata mutu..............
Labarin GARWASHI na kudine ga duk me son Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669
Kar ku Bari ayi Babu ku don wannan Labari daban yake da sauran
Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERI💃🏿
🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤
🍒🍒🍒 GARWASHI🍒🍒🍒
Page
23//24
Hadiza Bara'u Gidan iko
Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne
Sadaukarwa ga iyayena guda biyu Uwa da Uba Allah kayi musu Rahama kasa su tabbatacci agidan ALJANNAH madaukakiya da dukkan musulmin duniya
Yabawa ga masoyan Rubutun Gidan iko musamman masu comment sannun ku da kokari son so 🥰
Tukwici ne ga Anty Amina maman muhmd da Anty A'smau maman maama
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
.............Muna tsaye a filin Ina hagun onye dake Rike da tantabarar ta yayin bici ke ke damanta yayin da shima Ango Peter yake tare da abokanshi yarima Gibson Yayan Amarya Wanda ya zuba min ido Yana kallo na abinda na tsana kenan
Hatta Ahalin gidan sarkin sun fito filin don su ga yadda Wannan taro zai Kare Amma fa fuskar Uwar Amaryar cikin tsoro da zullumi don in har ya kasance yarta ta taba sanin wani namijn to karshen abin kunya ne a garesu Kuma abin kunya ga sarki da Ahalin gidan sa ace Yar gidan shi ta lalace kafin Aure don Haka kowa ke cikin taraddadi domin ko in har aka samu akasi shima Angon ba zai taba Auren ta ba don Haka acikin filin ma ba iyayen Amaryar ne kawai ba har da Ahalin gidan su Ango Peter kowa zuciya na bugawa musamman uwar amarya
A gefe na kuwa bana tare da komai sai nishadi don bikin ya kayatar Dani Kuma wannan Al ada tana burgeni ko Babu komai dai zai zaburar da Yan Mata kame kansu ko don irin wannan Rana da suke gudun fallasa ban sani ba ko don Ina tare da kewaye hausawa ne masu nuna min watsewar da ake a Jami a da Kuma na cikin gida yasa wannan Al adar ta burgeni? Ko ko dai don bana Ra ayin watsewar ne ? Oho Amma Kuma da yawa daga cikin yaren namu suna tur da Allah wadai da wannan tonon Asiri don da dayawa daga cikin Yan Matan dake Rasa budurcin nasu su Samarin ne ke batasu da Romon bakan su zasu Aure su wasu Kuma Yan uwan su NE na jiki ke karbe musu budurcin da ko mu muke girmama matar da takawo wa mijinta shi a gidan shi batayi saken da ta Rasa shi tun a waje ba
Kuma shi wannan tonon Asirin ba Wai sai a irin gidan sarauta ake you shi ba ko a gidajen talakawa suna alfahari da shi don suna ganin hanyace da ake wanke zukata daga zargi Ango zai karbi matar shi babu zargin ta zaga yawo ko wani ya Rigashi samun budurcin da suke wa kulafuci. Suma Kuma iyayen ta zasu San Basu bawa yarsu tarbiyar banzaba kowa dai zai Gane Babu cuta a cikin Auren su bare zargi.
Sai dai Kuma a gefe guda akwai wata Al ada da akeyi ga Ya'yan gidan sarauta musamman namijin da ke jiran gado wato yarima shi Kam idan zaiyi Aure Koda kuwa Yar gidan talaka ce zai aura sai anyi wata banzar Al ada wadda nake tsinewa a Raina don ba karamin haushi take bani ba har nake ganin in da nice matar da yariman zai Aura ba Zan taba yarda ba sai dai komai zai faru ya faru