Sashe 18
Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
..........Kai tsaye gidan su fauziyya na nufa da dai wurin Umar nayi nufin zuwa sai nayi wani tunani sai kawai na nufi gidan su fauziyya
Duk yan gidan su sun sanni muna Kuma girmama juna don Haka da na SHIGA sai da muka gaisa da kowa kafin fauziyya ta kaini wurin maman su na gaida ita cikin sakin fuska ta amsa min na kuwa ji dadin yadda suke karbata babu nuna kyama bare suyi min daukar hanci irin Wanda Amaka kewa hausawa da musulmi Amma su Babu Ruwan su Basu Kuma tallata min addinin su ba kamar yadda Amaka ke zargin Wai hausawa ne ke neman jana na SHIGA jikin su shiyasa take Hana Ni mu Amala dasu
"Daga Ina kike haka Justina cikin uwar Ranar Nan? Na dubi fauziyya Ina Fadin. "Don Allah fauziyya wata Alfarma nake nema Kuma ya zamo sirri a tsakanin mu don bana son kowa yaji maganar nan Kuma ke nasan Zaki Rufa min Asiri ko ba Haka ba? Fauziyya Yar Amana tace kwarai kuwa Justina ai tsakanin mu Babu tonon Asiri ai mun wuce wannan wurin ki Kara sakawa Ranki mu fa musulmi muna da Amana fiye da zaton ki don Haka fada min abinda kike so nayi Miki Alfarma ko mamana ba zataji abinda Kika yarda Dani Kika fada min ba Zan tayaki boye sirrin ki daga Ni sai ke Sai Allah. Na Kuma gode da Kika zabeni a matsayin wadda Zaki fadawa sirrin ki.
"Na ce na gode fauziyya don Allah salla nake so na Fara Amma ban San ya zanyi ba Kuma bana son iyayena su San na Fara salla shine Naga ke kadai kike fada min yadda addinin ku yake Kuma na Faye mafarkai Akan Ina salla da karatun Nan da nake yawan saurare shine kawai na yanke shawarar in Fara salla don naji zuciya ta tafi aminta da salla fiye da abinda mukeyi a cikin addinin mu ko Babu komai addinin ku ya koyar daku Adalci ya koyar daku yiwa Wanda ma ba addinin Yake ba Adalci Kuma ya koyar daku saka kaya masu mutunci ya Kuma koyar daku ibada wadda zuciya ke nutsuwa idan anyita don Haka fauziyya na San iyayena ba zasu so na bar addinin su ba Amma Ni gaskiya nafi son musulunci fiye da addinin da na gada don da shine gaskiya da ban Faye mafarki dashi ba tunda ku ai ba kwa mafarki da namu addinin ko kunayi? Na tambayi fauziyya ta Kuma kada min Kai Alamar A a basayi nace to kin gani ?
Fauziyya tayi kabbara tana fadin "ALLAHU Akbar kabeeran Kai Amma nayi Miki murna Justina sai dai Kuma Ina tsoron abinda zai biyo baya idan mahaifan ki suka fuskanci kin bar addinin su don gaskiya bana son ki samu matsala da iyayen ki.........
"Fauziyya na shiryawa komai Koda kuwa zasu kasheni ne kamar yadda suke fada banajin zanyi nadama da mutuwa ta ke dai taimakeni ki fada min yadda zanyi ki Kuma Rike min sirrina Kar ki fadawa kowa
Fauziyya Yar Amana ta lakana min kalmar shahada tana karanta min Ina maimaitawa ta Kuma karanta min kadaitakar Ubangiji da tsarkake shi da matsayin sa shi Daya Tak bashi da abokanshi taraiya da Kuma shaidawa shi kadai Yake Haka Kuma Annabi MUHD S A W bawan ne Kuma manzon sa
Duk na biya Kuma naji zuciya ta ta yarda da abinda na biya din inda Kuma fauziyya ta fada min sai nayi wanka na SHIGA musulunci da kuma yadda ake wanka idan period tazo da Kuma wankan tsarki na zahiri da Kuma na mafarki duk ta koya min yayin da ta Soma sanar Dani salla da bangarori da ke gareta irin abinda Yake Dole da Wanda akayi sauki da Wanda akayi sassauci wato farali sunna mustahabbi duka dai inda tace sannu a hankali zata ke sanar Dani Kuma in fadawa Umar shima zai taimaka min ta wata fuskar don Haka Ina gidan su fauziyya akayi sallar zuhur muka tashi fauziyya ta fada min niyar daga cikin zuciya ta Zan kudura ta ta Kuma ce na kalli yadda zatayi Alwala duk abinda Naga tayi Nima nayi. Haka kuwa akayi muka yi salla ta Kuma fada min sai na Rage saka kayan da zasu Rika fidda min part din jikina wato masu bayyana tsiraici
Haka na dawo gida zuciya ta tamkar anyi Mata wanki babu komai nakeji Sai farin ciki da wani irin iska Mai sanyi Yana kada Ni sai najini tamkar bani ba don har nauyi sai naji na Rage na koma wata Yar shafal
Aduk lokacin da Zan duba Inga ya Kai Wanda fauziyya tace min nake salloli sau biyar azuhur da la asar magaruba da Isha I Sai subahi kowane ta fada min lokacin su duk da tace lokacin Yana sauyawa musamman idan yanayi ya sauya irin zafi zuwa sanyi ko damuna Amma tace idan ma yanayin ya sauya zata sanar Dani
Aduk lokacin da zanga lokacin sallar yayi Zan SHIGA dakina na Rufe na fada toilet nayi Alwala na zaro katon hijabi na Wanda nasiyo don salla na zurma nayi salla ta wadda duk lokacin da Zan gamata sai naji wani Dadi da farin ciki kafin na zauna Ina tunani sai Kuma in boye hijabi na kafin na bude dakin in fito Ina makale da hearphon a kunne na Ina sauraren karatun Alkur ani Mai girma Kuma Alkur anil Kareem Haka Yar Amana ta fada min sunan shi wato Mai girma
Nayi Shirin SHIGA kasuwa inda Zan fanshi Alkur ani don Ina son na Fara koyon karatun sa don Haka nayiwa Amaka bankwana na SHIGA kasuwa sai da kyar na samo shi don Haka kai tsaye na nufi wurin Umar don shigar da na fito da ita daga gida ba itace na shigo kasuwa da ita ba hijabi na Yana jakata Ina fitowa na zurma kayana don Haka Umar ma da ya ganni cikin hijabin sai da mamaki ya Kama shi ya zuba min ido Yana kallo na cikin kaunar da bata boyu ba yana ta murmushi Ni kuwa kunya ta kamani ganin irin kallon da Yake bina dashi. Ya kasa tankawa sai dai kallo na yake Bai Kuma fita daga mamakin da Yake ciki ba na Kara kashe shi da wani mamakin inda na fiddo Alkur ani daga cikin hijabina nace mishi nazo ne ya koya min karatun Alkur ani. ALLHU Akbar kabeeran Ni Kuma nayi maza nace Asshhadu An Lailaha illallahu wa Asshhadu Annan Muhammaur rasulullahi S A W
Umar Bai boye farin cikin da yayi ba da Kuma Jin abinda na furta Amma Kuma sai ya tambaye Ni ta Yaya hakan ta faru?
Na Gaya mishi duk yadda akayi da Kuma yadda mukayi da fauziyya har zuwa abubuwan da ta fada min Akan salloli da dukkan abinda ya shafi musulunci Ni Kuma nace Zan siyo Alkur ani nazo ka Fara koya min Kuma kaima Zan Roki Alfarmar ka Rufa min Asiri Kar ka fadawa kowa
Shima yayi min alkawarin Rike min sirrina Kuma yayi min alkawarin Zama min Dan uwa Kuma zai Dora Ni akan dukkan abinda ya shige min Duhu fiye da Wanda fauziyya tayi min tun daga wannan Rana ya Soma da koya min Alkur ani tun daga basmala zuwa fatiha da kula uzai Wanda tuni Yar Amana ta koya min su Kuma na iya tun da dasu nake salla Kuma yace Yana son ganin fauziyya Yar Amana don itace macen da ba zai taba mantawa da ita ba Wai don ta Kara taro mishi masoyiya . Na Rufe fuskata Ina Fadin yanzu ne kake Sona ko kuwa tun tuni? Yayi murmushi yace ai tun daga Ranar da na Fara ganinki kin Fadi na kamu da kaunar ki don a Ranar banyi bacci ba ke nayi ta gani sai dai Ina zullumin yadda Al amarin mu zai kasance sai gashi Allah da ikon shi kin zamo yadda nake Kinga kuwa ai Dole na godewa Allah na Kuma yabawa Yar Amana. Kunya ta hanani Zama na taso Ina Fadin Ni dai Zan tafi gida ya taso ya biyo Ni Wai yayi min Rakiya har bakin motata ya kawo Ni ya Kuma bude min Yana fadin Wai Baki ma fada min sunan da Kika canja ba ko ita Yar Amana Bata fada miki komai Baki ya canja na yanzu? Nace ta fada min kawai dai ban San sunan da Zan amsa bane.....
"Ai na zaba Miki shi tun tuni tin kafin yau din Nan sunan ki Aminatu idan Kuma munyi Aure sai na kiraki da abin Sona kunya ta kamani inda naji lallai sunan Aminatu ya burgeni sosai na Kuma yarda sunana kenan nayi mishi godiya nace Nima zabin nashi yayi min da haka mukayi sallama Yana Kara fada min lallai gobe goben Nan na kawo mishi Yar Amana yayi Mata tukwici nace mishi Zan kawo ta kuwa. Naja motata na nufi gida
Ina karasowa na hango motocin Nan da sukazo tare da yarima Gibson inda naji gaba na ya Fadi ban tsinke ba sai da na SHIGA gida bayan na cire hijabina na boye a mota na SHIGA gida na samu Amaka ta hado min akwatina Wai dama yanzu take nufin kirana don yarima Gibson ya Aiko a daukeni don naje nayi mishi Zaman dakin da Zan dawo da ciki Wanda suke fatan a zaman wata uku kadai na samo shi ba sai nayi zaman wata shida ba don Auren namu kusa kusa za ayi shi ba lokaci za a ja ba..............
.
Labarin GARWASHI na kudine ga duk Mai bukatar Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669
Kar ku Bari ayi Babu ku don labarin GARWASHI daban yake da sauran
Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERI🥰💃🏿😂
🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤
🍒🍒🍒 GARWASHI🍒🍒🍒
Page
39//40
Hadiza Bara'u Gidan iko
Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne
Sadaukarwa ga dukkan musulmin duniya wanda suka yarda da kaddara suka Kuma yarda Babu Mai yi face Allah suka Kuma dogara ga Ubangiji Allah ya kabamu mafita
Fatan ALHERI ga mahaifina dake kwance kushewa Allah kasaka Rahamar ka Akan sa da dukkan musulmin duniya Kuma muminai maza da Mata
Duk yan gidan su sun sanni muna Kuma girmama juna don Haka da na SHIGA sai da muka gaisa da kowa kafin fauziyya ta kaini wurin maman su na gaida ita cikin sakin fuska ta amsa min na kuwa ji dadin yadda suke karbata babu nuna kyama bare suyi min daukar hanci irin Wanda Amaka kewa hausawa da musulmi Amma su Babu Ruwan su Basu Kuma tallata min addinin su ba kamar yadda Amaka ke zargin Wai hausawa ne ke neman jana na SHIGA jikin su shiyasa take Hana Ni mu Amala dasu
"Daga Ina kike haka Justina cikin uwar Ranar Nan? Na dubi fauziyya Ina Fadin. "Don Allah fauziyya wata Alfarma nake nema Kuma ya zamo sirri a tsakanin mu don bana son kowa yaji maganar nan Kuma ke nasan Zaki Rufa min Asiri ko ba Haka ba? Fauziyya Yar Amana tace kwarai kuwa Justina ai tsakanin mu Babu tonon Asiri ai mun wuce wannan wurin ki Kara sakawa Ranki mu fa musulmi muna da Amana fiye da zaton ki don Haka fada min abinda kike so nayi Miki Alfarma ko mamana ba zataji abinda Kika yarda Dani Kika fada min ba Zan tayaki boye sirrin ki daga Ni sai ke Sai Allah. Na Kuma gode da Kika zabeni a matsayin wadda Zaki fadawa sirrin ki.
"Na ce na gode fauziyya don Allah salla nake so na Fara Amma ban San ya zanyi ba Kuma bana son iyayena su San na Fara salla shine Naga ke kadai kike fada min yadda addinin ku yake Kuma na Faye mafarkai Akan Ina salla da karatun Nan da nake yawan saurare shine kawai na yanke shawarar in Fara salla don naji zuciya ta tafi aminta da salla fiye da abinda mukeyi a cikin addinin mu ko Babu komai addinin ku ya koyar daku Adalci ya koyar daku yiwa Wanda ma ba addinin Yake ba Adalci Kuma ya koyar daku saka kaya masu mutunci ya Kuma koyar daku ibada wadda zuciya ke nutsuwa idan anyita don Haka fauziyya na San iyayena ba zasu so na bar addinin su ba Amma Ni gaskiya nafi son musulunci fiye da addinin da na gada don da shine gaskiya da ban Faye mafarki dashi ba tunda ku ai ba kwa mafarki da namu addinin ko kunayi? Na tambayi fauziyya ta Kuma kada min Kai Alamar A a basayi nace to kin gani ?
Fauziyya tayi kabbara tana fadin "ALLAHU Akbar kabeeran Kai Amma nayi Miki murna Justina sai dai Kuma Ina tsoron abinda zai biyo baya idan mahaifan ki suka fuskanci kin bar addinin su don gaskiya bana son ki samu matsala da iyayen ki.........
"Fauziyya na shiryawa komai Koda kuwa zasu kasheni ne kamar yadda suke fada banajin zanyi nadama da mutuwa ta ke dai taimakeni ki fada min yadda zanyi ki Kuma Rike min sirrina Kar ki fadawa kowa
Fauziyya Yar Amana ta lakana min kalmar shahada tana karanta min Ina maimaitawa ta Kuma karanta min kadaitakar Ubangiji da tsarkake shi da matsayin sa shi Daya Tak bashi da abokanshi taraiya da Kuma shaidawa shi kadai Yake Haka Kuma Annabi MUHD S A W bawan ne Kuma manzon sa
Duk na biya Kuma naji zuciya ta ta yarda da abinda na biya din inda Kuma fauziyya ta fada min sai nayi wanka na SHIGA musulunci da kuma yadda ake wanka idan period tazo da Kuma wankan tsarki na zahiri da Kuma na mafarki duk ta koya min yayin da ta Soma sanar Dani salla da bangarori da ke gareta irin abinda Yake Dole da Wanda akayi sauki da Wanda akayi sassauci wato farali sunna mustahabbi duka dai inda tace sannu a hankali zata ke sanar Dani Kuma in fadawa Umar shima zai taimaka min ta wata fuskar don Haka Ina gidan su fauziyya akayi sallar zuhur muka tashi fauziyya ta fada min niyar daga cikin zuciya ta Zan kudura ta ta Kuma ce na kalli yadda zatayi Alwala duk abinda Naga tayi Nima nayi. Haka kuwa akayi muka yi salla ta Kuma fada min sai na Rage saka kayan da zasu Rika fidda min part din jikina wato masu bayyana tsiraici
Haka na dawo gida zuciya ta tamkar anyi Mata wanki babu komai nakeji Sai farin ciki da wani irin iska Mai sanyi Yana kada Ni sai najini tamkar bani ba don har nauyi sai naji na Rage na koma wata Yar shafal
Aduk lokacin da Zan duba Inga ya Kai Wanda fauziyya tace min nake salloli sau biyar azuhur da la asar magaruba da Isha I Sai subahi kowane ta fada min lokacin su duk da tace lokacin Yana sauyawa musamman idan yanayi ya sauya irin zafi zuwa sanyi ko damuna Amma tace idan ma yanayin ya sauya zata sanar Dani
Aduk lokacin da zanga lokacin sallar yayi Zan SHIGA dakina na Rufe na fada toilet nayi Alwala na zaro katon hijabi na Wanda nasiyo don salla na zurma nayi salla ta wadda duk lokacin da Zan gamata sai naji wani Dadi da farin ciki kafin na zauna Ina tunani sai Kuma in boye hijabi na kafin na bude dakin in fito Ina makale da hearphon a kunne na Ina sauraren karatun Alkur ani Mai girma Kuma Alkur anil Kareem Haka Yar Amana ta fada min sunan shi wato Mai girma
Nayi Shirin SHIGA kasuwa inda Zan fanshi Alkur ani don Ina son na Fara koyon karatun sa don Haka nayiwa Amaka bankwana na SHIGA kasuwa sai da kyar na samo shi don Haka kai tsaye na nufi wurin Umar don shigar da na fito da ita daga gida ba itace na shigo kasuwa da ita ba hijabi na Yana jakata Ina fitowa na zurma kayana don Haka Umar ma da ya ganni cikin hijabin sai da mamaki ya Kama shi ya zuba min ido Yana kallo na cikin kaunar da bata boyu ba yana ta murmushi Ni kuwa kunya ta kamani ganin irin kallon da Yake bina dashi. Ya kasa tankawa sai dai kallo na yake Bai Kuma fita daga mamakin da Yake ciki ba na Kara kashe shi da wani mamakin inda na fiddo Alkur ani daga cikin hijabina nace mishi nazo ne ya koya min karatun Alkur ani. ALLHU Akbar kabeeran Ni Kuma nayi maza nace Asshhadu An Lailaha illallahu wa Asshhadu Annan Muhammaur rasulullahi S A W
Umar Bai boye farin cikin da yayi ba da Kuma Jin abinda na furta Amma Kuma sai ya tambaye Ni ta Yaya hakan ta faru?
Na Gaya mishi duk yadda akayi da Kuma yadda mukayi da fauziyya har zuwa abubuwan da ta fada min Akan salloli da dukkan abinda ya shafi musulunci Ni Kuma nace Zan siyo Alkur ani nazo ka Fara koya min Kuma kaima Zan Roki Alfarmar ka Rufa min Asiri Kar ka fadawa kowa
Shima yayi min alkawarin Rike min sirrina Kuma yayi min alkawarin Zama min Dan uwa Kuma zai Dora Ni akan dukkan abinda ya shige min Duhu fiye da Wanda fauziyya tayi min tun daga wannan Rana ya Soma da koya min Alkur ani tun daga basmala zuwa fatiha da kula uzai Wanda tuni Yar Amana ta koya min su Kuma na iya tun da dasu nake salla Kuma yace Yana son ganin fauziyya Yar Amana don itace macen da ba zai taba mantawa da ita ba Wai don ta Kara taro mishi masoyiya . Na Rufe fuskata Ina Fadin yanzu ne kake Sona ko kuwa tun tuni? Yayi murmushi yace ai tun daga Ranar da na Fara ganinki kin Fadi na kamu da kaunar ki don a Ranar banyi bacci ba ke nayi ta gani sai dai Ina zullumin yadda Al amarin mu zai kasance sai gashi Allah da ikon shi kin zamo yadda nake Kinga kuwa ai Dole na godewa Allah na Kuma yabawa Yar Amana. Kunya ta hanani Zama na taso Ina Fadin Ni dai Zan tafi gida ya taso ya biyo Ni Wai yayi min Rakiya har bakin motata ya kawo Ni ya Kuma bude min Yana fadin Wai Baki ma fada min sunan da Kika canja ba ko ita Yar Amana Bata fada miki komai Baki ya canja na yanzu? Nace ta fada min kawai dai ban San sunan da Zan amsa bane.....
"Ai na zaba Miki shi tun tuni tin kafin yau din Nan sunan ki Aminatu idan Kuma munyi Aure sai na kiraki da abin Sona kunya ta kamani inda naji lallai sunan Aminatu ya burgeni sosai na Kuma yarda sunana kenan nayi mishi godiya nace Nima zabin nashi yayi min da haka mukayi sallama Yana Kara fada min lallai gobe goben Nan na kawo mishi Yar Amana yayi Mata tukwici nace mishi Zan kawo ta kuwa. Naja motata na nufi gida
Ina karasowa na hango motocin Nan da sukazo tare da yarima Gibson inda naji gaba na ya Fadi ban tsinke ba sai da na SHIGA gida bayan na cire hijabina na boye a mota na SHIGA gida na samu Amaka ta hado min akwatina Wai dama yanzu take nufin kirana don yarima Gibson ya Aiko a daukeni don naje nayi mishi Zaman dakin da Zan dawo da ciki Wanda suke fatan a zaman wata uku kadai na samo shi ba sai nayi zaman wata shida ba don Auren namu kusa kusa za ayi shi ba lokaci za a ja ba..............
.
Labarin GARWASHI na kudine ga duk Mai bukatar Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669
Kar ku Bari ayi Babu ku don labarin GARWASHI daban yake da sauran
Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERI🥰💃🏿😂
🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤
🍒🍒🍒 GARWASHI🍒🍒🍒
Page
39//40
Hadiza Bara'u Gidan iko
Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne
Sadaukarwa ga dukkan musulmin duniya wanda suka yarda da kaddara suka Kuma yarda Babu Mai yi face Allah suka Kuma dogara ga Ubangiji Allah ya kabamu mafita
Fatan ALHERI ga mahaifina dake kwance kushewa Allah kasaka Rahamar ka Akan sa da dukkan musulmin duniya Kuma muminai maza da Mata