← Book details Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 19

Sashe 19

Garwashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Kyautar wa ga Anty Aisha Bara'u Allah ya Baki lafiya yasa kaffara

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

...........Nayi turus Ina kallon Amaka da ta jido min akwatuna tamkar wadda zata bar garin gashi Kuma a yanzu babu abinda nake bukata irin sarari don na Rabi Umar na Kuma Kara sanin yadda Zan bautawa Ubangiji sai gashi Wai Amaka na fada min wai Zan tafi wani gari inda Zan kwaso zunubi Wanda Wai Zan tare a dakin wani Kato tamkar matar Auren shi ba Kuma Zan dawo ba sai da cikin shege Wanda su Kuma wannan cikin shine abin alfaharin su
"Kizo Mana kiyi wanka Kika tsaya Raba Mana kallo ko ko me kike nufi ne naga bakya murna da zuwa zaman dakin yarima Gibson?
Amaka ta katse Ni da fadin Haka Amma nayi shiru ban tanka Mata ba

"Wai bakiji abinda nake fada bane kike min shiru? Na fa kula da take taken ki Akan yaron Nan Dan gidan igwai Banga kina Rawar jiki akan shi ba halan Baki da labarin har Mata ke mutuwa saboda son shi?
"Wahala ce Bata ishi wadda ta mutu Akan shi Ni a idona Banga abin Rawar jiki Akan shi ba....

Ban Rufe bakina ba naji Mari Amaka ta kwado min
"Ai dama tuni nagane abinda kike nufi akan yaron Nan to Kuma kinyi karya Wallahi sai kin Aure shi Koda Zaki mutu sakaran banza marar tunani Baki San Rabo bane Aure a gidan igwai? Yar iska ki haifo Mana princess ba alfahari bane? Tashi maza kiyi wanka na kaiki in Kuma Roki ayi Miki ADDU A ki SHIGA da sa a kina zuwa ki samo ciki ko haihuwa ba Zan Bari kiyi a gaba na ba za ayi bikin ku ki haihu a can don su tabbar da ke din irin haihuwa ce

Haka nayi wanka Ina kuka na shirya aka loda Mana Kaya a mota inda Amaka ta Kira Maazi Nkem take sanar dashi Aiken da akayo daga gidan igwai na akai Ni inyi wa yarima Gibson zaman daki inda shima Maazi Nkem din ya cika da murna da farin ciki Wai zanjewa yarima Gibson zaman daki don Haka ya yi min ADDU AR inje cikin sa a Kuma Wai don baya kusa da har dashi cikin Wanda zasuyi min Rakiya don Haka da Amaka kawai muka tafi wadda ta Kira kawayen ta biyu madam go slow da Kuma maman Bose sukayi min Rakiya suna ta Kara kambama dacen da nayi na Sa ar da na tako har na dauki hankalin yarima Gibson da irin daular da Zan SHIGA sai suka SHIGA yi min fatan Ina SHIGA in samu ciki yadda Zan Kara martaba a agidan igwai

Haka muke tafe suna ta santin gidan sarautar suna Kuma Kara bawa Amaka shawara Wai ta nema min maganin makiya da mahassada saboda Matan da suke son Auren yarima Gibson yace baya son su to suna iya Hana mu zaman lafiya

Ina sauraren su da firarrakin su Wanda suka cika min kunne da tsabar haushi da takaici . Haka muka muka Isa jihar imo kasancewar motocin masu lafiya ne Kuma gudu suke tamkar jirgi shiyasa bamu Jima sosai ba muka Isa gidan igwai inda muka iske masu tarba sunyi dandanzon suna jiran karasowar mu inda Amaka da kawayen ta suka Soma Kara gyara min Ado na Wanda yasha murjanai Wanda sune karshen adon na gidan sarautar Suma kuma Kara fesheni da turaruka kala kala suna yafa min mayafina Wanda na janye daga kaina

Ahalin gidan igwai suka suka tarbe mu zuwa dakin mah inda aka sauke mu da nau ikan abinci irin namu da ma Wanda ba namun ba irin na turawa. Har falon hutawar igwai aka kaini na gaishe shi Yana Rike da hannu na Yana saka min Albarka Yana Kuma fatan na zamo farin cikin Gibson Wanda ya zamo shi kadai ne da namiji a wurin igwai sauran Yan uwan shi Mata ne shiyasa soyayyar shi daban take wurin igwai

A sashen mah muka kwana sai da su Amaka Zasu tafi ne suka Mika Ni dakin yarima Gibson dama Haka Al adar take uwar yarinya ce ke Kai yarta dakin da zatayi zaman ita da kawayen ta ko Yan uwan ta don Haka da muka shigo garin Amaka ta sanarwa kanwar ta ta karaso aka Rakani dakin na Gibson Wanda Amaka taja kunne na sosai akan karbar Gibson ko don nayi saurin yin ciki don na samu zarafin mamayar Ahalin gidan igwai yadda Za ayi hanzarin biki don ba Zan haihu a gida ba sai a gidan yarima Gibson

"Allah yasa kiyi wani Abu da zai Sosa Mana Rai kiga yadda zanyi Miki wallahi don na kula sai na taba lafiyar jikin ki ko zamu daidai ta don kema nan Haka dake kin iya iskanci to Allah yasa ayi wata banji kinyi ciki ba kiga yadda nake a zahiri don Rashin mutunci Zan kera Miki har sai kinyi nadamar sani na

Amaka tana Rike da kunne na take min wannan kashedin kafin tayi min wani shegen Rankwashi me tsananin zafi Suma kawayen ta madam go slow da mama Bose har ma da mama Ester kanwar Amaka duk shawarar saurin yin ciki suka bani Wai kuruciya ke damu na shiyasa ban San girman da ya sameni ba

Da Haka igwai ya hado su Amaka da shatarar Arziki suka taho inda Kuma aka SHIGA yanka min talo talo na tarbar yarima Gibson zuwa dakina tamkar dai ace yau din itace Ranar tarewa ta

Ina zaune Ina kallon yadda zamu Kare Ni da yarima Gibson Akan wannan banzar Al adar wadda ko da ban samu tsarkin musulunci ba ba Zan yarda da ita ba saboda Rashin sa ar da yarima Gibson ya tako ta Rashin son shi da nake bare Kuma yanzu da nagane abunda su Amaka suke farin cikin ya faru tsakanin mu ai Zina ce ita kuma Zina laifi ce Dan da Kuma aka haifa ta hanyar Zina shine shege da na nutsu sai nagane da yawan Ya'yan da yaren mu suke Haifa shegu ne Ni Kuma na kudure ba Zan taba haifar shege ba

Da sauri na Mike don ganin lokacin sallar magaruba ya yi inda na fada toilet din dakin da aka aje Ni da sunan shine dakin Gibson Wanda ya gaji da haduwa da kawar Rayuwa na SHIGA na dauro Alwala na Kuma bude kayana na jawo hijabi na zurma na tada salla

Ina cikin sallar ne naji an shigo Amma duk da Haka ban katse salla ta ba don na daura damarar nunawa kowa irin addinin da na zaba amutu ko ayi Rai...................

Labarin GARWASHI na kudine ga duk me bukatar son Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669

Kar ku Bari ayi Babu ku don labarin GARWASHI daban yake da sauran

Hadiza Bara'u Gidan iko ne sunana ke cewa saduwar ALHERI💃🏿🥰
Chapter 19 · 0% Book details