← Book details Futuhatul Khair Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 24

Sashe 8

Futuhatul Khair Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka kowacce ta kwana da haushin kowacce, saida safe Chuchu ta shigo take cewa uwar gida, kin kanainaye komai, mijin ma ba'a aramin shiba, Zainab cewa tayi banganeba? ai a wajanki ya kwana
Ban kwana wajan ko wacce ba, dole ne? Kinga fice kibawa mutane waje, kinyi nasarar aurata amma bazakiyi nasarara samun jikina ba, insha Allah
Jikina, kinga ya nuna Zainab natane ita kad'ai, yana gama fad'a ya juya ya koma hanyar dayabiyo

Lallai bokanki yabaki sa'a, amma kisani wallahi sai kinzama abin tausayi, dama bason Allah na nuna miki ba, kingaje komai saike d'aya mu xuba ni dake aga mai nasara

Haka taqaraci maganarta ta fice, tana fita ita kuma tayi d'akin sa, kusan fad'a sukayi akan hakan amma yace itama idan tagaji dashi to tafita, ba yadda ta iya haka ta daure

Haka xaman yayi ta tafiya, wataran dad'i wataran mad'aci, mad'acin daga b'angaren dangin Abdul ne wad'anda ayanxu suka juyamata baya, ko Futha dasuke d'auka yanxu sun daina
Dad'in ta dasamun sauqinta mijinta babu abinda ya canja mata, saima k'ara kula da ita

Haka aka d'ebi shekara biyu, har yanzu Chuchu bata samu kan Abdul ba, duk yanda tayi, abin yaci tura

Lokacin FUTHA nada shekara 6 yarinya kamar ita tayi kanta

Muje zuwa dai

By
@ut@r h@jiy@
[11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/09 9:23 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💦✍🏻🌹🍇💦💖: *FUTUHATUL KHAIR*

*®NWA*

*©Zainab Y Hussain*

*Dedicated to FUTHA LUV*

_Page 63-64_

Har a wannan lokacin Allah bai qara bawa Zainab ciki ba, kuma bata saka damuwa arantaba, tasan cewa Allah shine mai komai, yanda yaso haka za'ayi

Tunda yabasu FUTHA ma, yaba su abu mai daraja, saboda 'yarta mai nutsuwa ce, duk da qarancin shekarunta

Yausu Chuchu an qudiri aniyar cewa kota halin qaqa sai tasamu zuciyar Abdul, koda hakan na nufin zatayi yawo tsirara

Dama ai tsirarar kike, tunda da auren ki kike kai, kanki wa miji Wanda bana kiba

Haka tunsafe tafice daga gidan, dama ai ba maganar tambaya, tunda ko kallon inda take bayayi

Iyayen sa kullum cikin fad'a suke masa, akan ya zab'i bare ya bar 'yar uwarsa, shiyasa yanxu kwata kwata basa shiga shirgin ta, itama data fuskanci haka, bata shiga nasu, sai dai duk qarshen sati zataje ta gaidasu

Ada can, yini take agidan, sai dare take tafiya, amma yanzu ko awa biyu bata iyawa

*Birnin gwari* shine garin da aka tafi, aka wuce tsaunuka, da bishiyu, sannan aka haura bukkar *Boka Nargas*, wanda idan ka ganshi, kai kace irin tsofin *gorilla* ne saboda bak'i da munu, gashi gajere

Haka suka tamfatsa cikin bukkar, yasan da zuwan su, tunda wata qawartace tayimasu hanyarsa, kuma shi bucking akeyi, bawai kaxo da ka ba

Suna shiga kafin yace komai, sukaga wani qullin abu cikin bakin wani qaton kifi, sosai suka razana saboda basu tab'a ganin kifi mai girma haka ba

Kud'auka yace, angayan komai, basai kun fad'a ba

wannan kullin, shi zaki d'auka tareda wan nan kan kifin, kisamu k'aton dutse ki d'oramasa, kinga bakinsa zai rufe, idansa zai rife, kunnansa zai rife, bazaiga kowa ba saike

kuma guri da kikasan idan aka ajiye babu mai zuwa balantana ya gani

Abu mafi sauqi, ki samu qasan gadonki, ko kid'ora dutsan, ko kisamu turmi na qarfe ki d'ora, tunda babu mai shiga cikin d'akin ki

Wannan shawarar uwarta mahaifiya, itane tace haka, dariya yai yace kinyi dai dai, Ku zube Ku tafi, wannan kuma layar ki tabbata kinsata gurin d'umi, inda sanyi bazai shi gaba

Ma'anarta, bazai qara kusan tar taba, harsai randa layan sanyi ta ta b'ata

Haka suka ajiye masa kud'i, suka fito

Basu tsaya komai ba, a hanya, gida suka tawo, sunata sheqa dariya irinta arna

*Wannan shine mafari*

Zuwansu gida ba jimawa, suka fara aiwatar da qudirunsu, saida suka gama, tas sannan sukaje cikin kitchen, bayan gas cooker suka ajiye layar, amma saida suka cire one tile na gurin saboda sunsan zai iya d'aukan sanyi

Abdul yana office operation yagama, yana hutawa, yaji kansa yayi wani irin juyaeay, idansa ma haka, bakinsa yafi komai yimasa nauyi

Haka dai ya zauna, jin xaman ba dad'i yasaka shi fara tattara kayansa, zai koma gida

Tundaga gate yakejin wani feeling akan Chuchu, ko kallon part d'in Zainab baiyi ba, ya yi part d'in Chuchu

Yana shiga tana zaune, akan kujera, tana ganin sa tafara washe baki, zuwa yayi wajan ta, hannunta Yakama yace I'm sorry Chuchu for evrthin na zalunceki, na kuma tauyemiki haqqinki amatsayinki na mata waje na, saboda haka kiyiwa mijinki afuwa

Yanxu bashida lokacin kowa sai naki, dana babyna FUTHA

Sosai taji dad'in haka

Duniya sabuwa, ita kuma jin har anyi isha'i bai dawo ba, yasaka takira shi, lokacin yana tare da Chuchu

"Hello" Abban Futha shiru ina katsaya?

Wajan matar sa, mai qaunarsa, mai tattalinsa, ya tsaya, ko kinada abin cewa?

Babu tace, sosai tayi dauriya, saboda dama tayi mafarki akan haka, bata ce komai ba, saima addu'a datake ciga ba dayi

A haka aka d'auki lokaci ko leqe saidai taganshi ya dawo, Futha ce dai, xa'a turo a d'auketa

Iyayen sa basu damu da rashin saba, tunda suma basuda bakin magana, an kulle, kud'i kuwa kamar ruwa haka take maidasu wajan tambayar sa

Amma duk da wannan samun data yi masa, bata sami jikin saba, dan kuwa ko tab'ashi baya son tayi, haka tayi haquri tunda tana samun masu gidan rana

*Bayan shekara biyu*

A haka aka shafe wannan lokacin Abdul bai tab'a koda kallon b'arin Xainab ba, komai nasa kacokan yakoma gun ChuchChuchu

By
@ut@r h@jiy@

[11/10, 8:13 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [24/09 10:51 am] @ut@r h@jiy@💅🏻💦✍🏻🌹🍇💦💖: *FUTUHATUL KHAIR*

*®NWA*

*©Zainab Y Hussain*

*Dedicated to FUTHA Luv*

_Page 65-66_

Iyayen sa a wannan lokacin da ita kanta Meena yayarsa, hankali yafara zuwar musu, tunda ayanzu suna d'an hirar sa, kuma har suna yunqurin zuwa wajan sa

Chuchu yau bata nan, shiyasa 'yar aikin ta, yau take gyara kitchen harta wuce saita dawo taga wata Leda, lah aunty ko mancewa tayi da ita?

D'aukanta tayi, tasa a saman cabinet

Lokacin da Abdul ya shigo gidan lokacin yaji babu abinda yake so irin yajishi gashi ga Zainab

Haka ya shiga wajan ta, sosai taga abin kamar almara, baiyi wata magana da itaba, illa nuna mata yayi ta taimake shi, bata tsaya Jan ajiba, tunda itama tanada buqatar sa

Haka suka farantawa junan su, magana yake son, yimata amma ya kasa, ta lura da hakan shiyasa koda zai fita saidatayi tofi, a ruwa ta bashi qin karb'a yayi saida kyar

Inda suka tafi, badan komai sukaje ba, saidan 'yarsa, suna son itama ya mantata, nan da nan aka yimusu aikin, suka dawo

Haka xaman ya kasance Indai bata nan to Abdul yini yakeyi tareda Zainab, wani abin mamaki kuma yanxu tsakanin sa da FUTHA sai harara da duka, ko yaya tazo kusa dashi

Ita kuma Zainab takasa fad'a a gida, duk da batasaka damuwa ba, amma dai kowa ya ganta saiya CE kin rame sai dai tayi dariya

Matsalar FUTHA da babanta, yasa ta yanke shawarar kaita gidan su Abdul

Haka akayi maidata gidan tayi, anan ma bata tsira ba, saboda har yanzu akwai ragowar asiri jikinsu

Lokacin data fuskanci bata gidan, takanas taje gidansu Abdul dan fad'awa Maman sa, sai ta ganta agidan

Gaisawa sukayi, anan ta yini lokacin da zata tafi batayi shawara da kowa ba, ta d'auketa, haka ta maidata wajanta makaranta ma, tadena zuwa, saiya kasance aikin komai itace lokacin tanada shekara 11, amma tasan me Kishiya take ciki

Itama tsareta akayi, ko gigin zuwa gurin uwar ta batayi

Rabo shine yakai Abdul wajan Zainab, dan yanzu cikine da ita wajan watansa 5 lokacin kuma yafara fitowa, yau ta dawo daga gun aiki tabiya dan ganin FUTHA, amma wayam tambaya tayi, a daqike Hajiya tace ai tana gidan Ku, wajan Chuchu

Bata qarasa ba, ta fita da sauri, sai gidan, FUTHA sunanta ta shiga kira, jin ana karanta yasa tafito da gudu muryan Umman ta tajiyo

A sukwane ta fito, me kikazo yimun a gida?, 'yata nazo d'auka mitsiyaciya Allah ya kusa tona asirin ki, mai raba mata da miji, d'a da uwar sa

Kinsan badan abinda kika yi ba, kebaki isan Abdul ya kalle kiba, Hajiyan sa ma haka, 'yata tafi k'arfinki, ko shine yabaki bai isaba, kiyi d'an kanki

Juyawar da zatayi sai ganin ciki tayi, kut ke Zainab iskanci kika koma? cikin waye wannan?, cikin mai gidan ne, ko shima sai ya nemi izininki? shashasha wahalalliya, haka ta janyo hannun 'yarta suka fice

Bata tsaya wata wata ba, ma'ajiyar ta, ta duba? wayam, Munay kina ina dan uwarki ina kika ajiyen ledar da kika gani?, lah asama na ajiye mantata kika yi ta fad'a baya, ai jibgarta tafata yi, ganin dai ta cuceta kuma tsayawar b'ata lokaci ne, yasaka tayi maza ta ajiye shi inda yake

Abdul koda yadawo, bai qara bi ta kan part d'in Zainab ba, masifa yashata kamar d'anta, hak'uri yafara bata, amma ko kallo bai isheta ba

Safiya nayi, aka tafi wajan boka, magani yabata ta tabata ta tsallake, haka akayi kuwa, tana xuwa ba sanya, haka ta xuba maganin

Lokacin da take zubawa, babu kowa, haka tagama ta koma part d'inta

lokacin ne FUTHA tana ta wasanta da ball suna hira itada Mamanta akan school nasu, wadda tace ta dad'e bata jeba, ball d'in data buga sai tayi hanyar waje, tana zuwa akaci sa'a ta tsalleke maganin da uwarta yakamata ace ta tasalleke, dan cikin jikinta ya zube

Amma akasin haka, yasa ta taka

Haka ta dawo, uwar tana magana amma bakinta yaqi ya bud'e dan tayi magana, tai tai takasa, kuka sukasaka baki d'ayan su

Asibiti ta kaita, akace komai normal, batada zab'in daya wuce addu'a, ita kuma tasaka agaba

Kwanaki na tafiya, FUTHA harta saba, da maganar kurame, daga ita har Mamanta, ciki kuma yanata girma abin sa

Ganin cikin yana nan, tayi tayi amma bai fita ba, sai tayanke shawarar sace FUTHA, shine ta d'auketa tabawa wani mutum akan ya taimaketa yakai wannan yarinyar wani gari nesa da Sokoto

Maqudan kud'i ta bashi, shikuma bai duba k'ank'antar taba, ya sunkuceta sai NIGER, anan ya ajiye ta agarin Duffa

Tafi tafi, harta kai Numeiy, anan ne Kaber ya tsinceta ya kaiwa Matarsa MEIMiE ita

*A dawo labari*
Chapter 8 · 0% Book details