← Book details Futuhatul Khair Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 24

Sashe 23

Futuhatul Khair Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Alhamdulillah kulawa dai dai gwargwado tana samu wajan Mama Bata barinta ita d'aya koina ta zauna Mama na wajan
Daga Asibiti kullum Sai an turo wata nurse ta kara duba lafiyar ta
Zaman gidan yamata dad'i, batada matsala Abdallah ya dawo fitina salamu alaikum, Mama tare suke kwana saboda Abba yaje umrah shiyasa Tare a gado d'aya suke bajewa
Daga gidan su kullum sai an kamata abinci, k'annenta kowa rige rigen zuwa dubata yake
Farouq yanamata waya akai akai, kullum burinsa Allah ya sauki Matarsa lafiya
4:30 dai dai na asubah FUTHA ce zaune kan dadduma bayan ta idar da nafeelfun ta carbi take ja, har akayi Assalatu tana kan dadduma Mama itama ta tashi lokacin
Tashin da zatayi danyin raka'atul fijr, habawa gaba d'aya mararta ta rik'e takasa katab'us haka Mama ta fito ta tarar da ita
Yan aikin gidan ta kirawo bayan taiwa driver waya kan ya fito da motor
Allah sarki har suka isa asibitin tanata mirk'ususu, sai yada kai take, tana yarfe hannu hawaye wani yanabin wani
A haka suka k'arasa da gudu aka d'auketa sai labour room, Haihuwa ce amma kuma lokacin baiyi ba, gashi wahala take Idan tayi nan saitayi nan
Har 7:00 ana abu d'aya ita takasa gayawa kowa ma, addu'a takemata sosai itama FUTUHATUL KHAIR bakinta salati da hailala yake yi ba wannan ihun da kwakwazo irin na sauran Mata
Shikuma acan kaida 8 yake mata waya, ya buga shiru har ba adadi jikinsa yabashi wani iri tun asubah daya farka
Jin ba'ayi picking ba gata Mama ya buga hakan yasa bashiri yaje office yai signing wasu takarddu yabiyo flight
10 dai dai awanann lokacin ta wahala ta jigata ita kuma Haihuwa tazo, gashi bata da wani k'arfin Iya komai
Allah cikin ikon sa kafin ma afaramata wasu abubuwan faya ta fashe cikin mintina k'alilan ta haifo Babyn ta Namiji k'ato tareda mabiyya suka fad'o
Adaidai nan ya shigo asibitin shima bayan bayanin daya amsa wajan yaran gidan su lokacin daya je
Yaro tabarkalllah an gyarashi an shafeshi da zaitun angoge sai bayan 4 hours kuma ayi wanka
Reception ya shiga nan yaga Mama a zaune da sauri ya k'arasa Mama yayah?
Bayani tamasa kafin yace komai, ankawo baby cikin farin shawl yaci fararen kayan sanyi ga gashin sa a kwance duk ya cika fuskar sa
K'aidar asibitin sune zasuyi maka komai, har maijegon su zasu bata kaya da pad bill shine dai zaiyi aiki
Masha Allah abinda yafito abakin su lokacin da suka amshi babyn, yana hannun su duka yaro k'ato dashi
Waya suka bugawa gidan su FUTHA, kafin wani lokacin sun cika asibitin yan uwansu duk sunzo
Hajiyan su itama saigata dayake anmata waya
Maman FUTHA tazo da tayi kamar bazata ba saboda kunya, tunani tai abin aina farin ciki ne, kuma futha dai ba ita tayi rainon taba bare ace da kunya mayafi ta yafa, shine fa ta tawo
Yan Asibiti da staffs kowa ma yasha kyauta kud'i kujeran Makkah haka sukabada biyar da wadda taka musu baby da wadda ta amsheta lokacin da aka kata, da wadda tayi jigila da ita tana lobour room haka yabisu da kujeran Makka
Basu suka baro asibitin ba sai wajan 2:00 ta farka taga dangi da yawa ga baby, bata karb'eshi ba ganin da mutane
Tarkatawa sukai akayi gidan Mama anan za'ayi jegon tunda anan aka fara rainon cikin Har kawo Haihuwar sa
Abdallah anyi k'ani yana kusa dashi kamr ya cinye saboda murna
Maman FUTHA daga Asibiti ta zarce gidan ta
Hajiya ce ta biyo su itace zatayi wanka tunda anzama d'aya Mama ta d'auki Hajiya kamar uwar mijinta
Angon k'arni dai yakasa fita daga ya ajiye baby zaizo yak'ara d'auka, abin dariya ma
Ruwa aka d'ora bayan ansiyo kayan cikin garwa, yana zafi baby aka fara yiwa kafin Uwar
Anyi daru wajan wanka dan ita kuka tasaka lokacin da Hajiya tace tashiga ruwa, gani tayi kamar ma tafasa yake cikin sa, ba yadda ta iya tanaji tana gani ta dannata da k'arfi
Da zafi amma ana yan mintuna saitaji dad'i harwani lumshe ido takeyi, bacci yana so yatafi da ita
Kya taso ai da kuka kika saka, yanzu kinfara jin gatan da ake miki shine zakiyi bacci, huum wani gata kindai azabtar dani wallahi gara Haihuwa da wankan Indai hakane, ni ko ihu banyi ba amma wannan ruwan kina zuban shi ihu nasaka
Kyaji dashi haka suke fito ana fad'a dariya yan d'akin suka ringa yi
Fadeela ana mata waya, dama ita a ready take, tunda taji ta koma gida, murna tai tace a turo mata photon babyn kafin suzo dan yau ko gobe zasu ganta
Kafin dare kowa yaji Haihuwar k'awayen ta wasu sunzo ma, na Lagos duk sunji
Kowa murna yake mata, mijinta dai bak'i sun hanashi sakat, daga ya shiga mutane zasu fara sallama
Shi yana so suyi magana me take so, dan da safe yake son komawa
Dole sai hak'uri yai da asubah ya shiga, nan Mama tace yabari Fadeela dasu Basmah suzo ayimasa waya Idan suka lissafa
Ok Mama nabar ayyuka, zan koma sallama yai musu Ji yake kamar ya tafi da Babyn tare da uwar y had'a yaringa d'aukan pics harsaida mama tace ya isa
Nan ma saidayace kullum aringa d'aukan pics na Babyn aturo masa
Tom za'a turo, ba kunya ita Uwar ma hartafika jin nauyin mutane, amma agabana kake wannan maganar
Kansa ya shafa yana murmushi yayi wa FUTHA peck a kumatu yai saurin fita yabarta dajin kunyay
Dariya Hajiya tai tace ga k'arshen kunya ya nuna
Kaya nagani na fad'a kakannin yaro suka masa, da suka dawo daga Saudi, kowa kuma burinsa yai musu abin bajinta jikokin su na farko kaya har kusan rasa inda zata saka tai
Fadeela dasu Sodangi Basmah Sahaf Stylich Munay Mrs Omar Aunty Nafee Aunty Jidda dukkansu sunzo yanzu sunzama kamar yan cikin gida
Tare dasu akayi lissafin komai da abubuwan rabo duka dasu akayi
A account d'in Stylich aka saka kud'in ma, kayan flour dasu lemo Abban FUTHA yace suje Hotel Su karb'a yayi magana
Yaro yazo da goshi, Kayan snacks duk Abban tane ya d'auki nauyin da lemo da ruwa
A gida suka ce za'ayi ba wata fita da za'ai, komai cikin tsari akeyin sa da gwanan cewa
Gobe ne suna, gida yacika ya tunbatsa da mutane yammatan dasu Fadeela gidan FUTHA suka Shiga itama anan ta zauna aka mata k'unshi ja da bak'i
Anan kuma suka ajiye komai da komai nasu, Har kayan sawar su danata
Abdallah yaga yan uwa cikin su yashiga tunda yasan wasu
Ango tun asubah yabiyo jirgi yazo, yace dashi za'ayi sunan
Yaro yaci sunan Muhammad Ahmad, za ana cemasa Sultan haka suka tsara
Taron suna anfara cikin nasara ba kace nace ba hayaniya abinci ne kowa yaci yakuma ya tafi da shi anyi hotuna na tarihi kowa kagani cikin annashuwa yake
Dangin Maman FUTHA gidan ta suka sauka, wasu kuma suna gidan su, Babyn aka kai musu ya jima itama daga k'arshe Farouq d'aukan ta yai yace taje ayi photo da ita tunda danginta suna can
Taji dad'i sosai, suna ya qayatu FUTHA tasha kayan barka sosai writers da basa bada komai sai dai aci a tashi wannan karan sun bada dan ya Hajja turmin Super ta bada Nafee Anker kuma set na overall guda biyu, Queen Meemi ita 5000k ta bada sunyi k'ok'ari sosai dai wannan karan
FUTHA tayi kyau, tasaka kaya masu kyau, daga super sai Swiss sai Sanata da Sharaton tayi kyau sosai
Fadeela matayi kyau, Abdallah shima kaya wajan set goma akayi masa banda wanda Fadeela ta kamasa tunda d'an gidan tane kai kowa a wajan ya fidda tsantsan kyau nasa
Taro ya tashi lafiya sai fatan Allah ya maida kowa gida lafiya
Wanka itada Babyn aka musu, shitafi bukata a yanzu dan ta gaji sosai
Kowa ma baccin sa yai da wuri, Sultan bashida rigima yanada hak'uri baya mata kuka duk jagwalgwalon daya sha na d'auka
Abban CHUCHU ya saitu ya dawo hanya, shima 50k da kayan baby haka ya Ka musu, wasu daga cikin yan gidan sunzo ba a nuna musu komai ba tunda duniya ta koya musu
Kowa dai yazo lafiya ya koma gida lafiya, kama daga na wasu garin Har na wata k'asar daban anbar Maijego da babyn ta da Hajiya mai wanka lafiya
Oga aiki ya tsare shi, sai dai waya, wajan two weeks kenan rabon ta dashi
FUTHA tayi kyau tayiwa k'iba mai ban sha'awa Hajiya Mama Maman ta dukkansu k'ok'arin su su gyara yar su.

*Remain Last page*

@ut@r h@jiy@
[11/10, 8:27 PM] ‪+234 809 308 3613‬: [10/11 9:39 am] @ut@r h@jiy@✍🏻💅🏻:

*FUTUHATUL KHAIR*

*®NWA*

*©Zainab Y Hussein*

*Dedicated to FUTHA LUV*

*_THE END, K'ARSHE_*
Chapter 23 · 0% Book details