Sashe 8
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari jajibarin ɗaurin aure duk su Amina sun hallara don yin aiki da wayar Fati Affa ya yi amfani ya kira Ruƙayya, cikin faɗuwar gaba ta ɗauka jin muryar Affa duk sai tsoro ya kamata, shi kenan Umma ta rasu, haka ta raya a zuciyarta, ya ce Ruƙayya ko zaki iya zuwa gida sai ki koma ranar Lahadi." Nan take tace waya rasu Affa? Ya ce a'a babu wanda ya rasu,ko gobe ma zaki iya zuwa, kada ki damu ba wani abu bane.
Sam bata cikin haiyacin ta gani take an ɓoye mata ne babu wanda bata kira ba cikin Yayyanta amma duk sun ce ba komai kuma basu san kiran da Affa yake mata ba,kona menene?.
Nuraddeen ta kira take sanar dashi abin da yake faruwa, yazo gurinta suna tattauna maganar ya ce ta ƙwantar da hankalinta insha Allahu babu komai, kuma ta bar tafiyar sai gobe, tun da yau lokaci ya ƙure,
*** **** ****
Tun Asubahi tana cikin motar mocopolo duk ta ƙosa ta ganta gida dan jin meke faruwa?.
Wayewar garin wato ranar ɗaurin aure ai kada kuso kuga ango wanda dama ƙwana ya yi bai runtsa ba,nafilfili yake yi yana roƙon Allah kar ya kawo sanadin fasa auran. Da safen ne yana fitowa wanka.
Zainab ta kirashi inda take mishi ƙorafin rashin kiranta tunda ta dawo, har ga Allah shi yama manta da wata Zainab baya tuna komai sai Pretty ɗin shi. Ya ce "Kiyi haƙuri abubuwa sun min yawa yasu Hajiya?" Ta ce lafiya,dama ina son kuɗi ne. Ya ce me zakiyi dasu ne? Bana baki dubu hamsin da zaki tafi ba? Ta ce To ai anayin kayan faɗar kishiya kuma ba kai min ba, ya ce aiko ita ma Pretty ɗin ba riga na mata kayan ba tukunna, ta ce to nidai kuɗin zaka bani, ya ce,zan turo miki, ta ce nawa? Abin ya soma bashi haushi ya ce yanda naga dama ya kashe wayar,shi fa haushin ta yake ji itace dai bata sani ba.
Yana gama shiri gurin abokanshi ya nufa can ya yi break. Hira suke suna ta shaƙiyancin su, yayin da gidan su Momy ya ɗinke da jama'a wannan karon har da Hafsi tazo da yaranta guda biyu daga Kalaba inda mijinta yake aiki. Aure kawai za'a ɗaura amma an cika fiye da wancan satin.
Dady kuwa yasaka kaya sun kai kala goma Yana cirewa sai yaga basu dace da É—aurin auren ba, duk da kasancewar kayan sababbi ne. Duk yasa aka siyo su daga Togo aka kaisu É—inki.
A ƙarshe ya haƙura cikin wata shegiyar mai masifar ƙyau, green dark hular dama tare aka kawo su,yana fitowa sai da ya birge abokanshi gurin Momy ya shiga tana cikin ƙawayenta babu wanda Dady bai birge ba, Momy kam Babu wanda ya kai ta farin ciki wannan rana, ɗan ta ya samu abin da yafi so.
Hatta motar da Dady ya hau wannan rana sabuwa ce mai shegen tsada,so kam abokanshi kayan su iri ɗaya suka sa wani farin yadi mai shegen tsada suka ɗinka gaba ɗayansu abin birgewa har da waɗanda ba baƙaƙen fata ba wasu turawa. Su Sadiƙ ne suka ɗinka duk wanda yazo indai aboki ne sai a bashi yasa. Unguwar Kabala ta ɗinke da jama'a tamkar taron idi. Tun daga farkon layin har ƙarshe dole ne sai anyi amfani da lasifiƙa wurin ɗaurin auren.
**** **** ****
Ruƙayya da yake tasowar ƙarfe huɗun Asubahi suka yi kuma motar tayi shegen gudu, huɗu saura suka sauka. Mashin ta hau zuwa Kabala suna kusanto unguwar tasu gabanta ya na ƙara faɗuwa. Sanye take da wani leshi purple ba wata ƙwalliya da tayi amma hakan birge wasu take. Sun ratsa layin nasu cike da jama'a tayi mamaki yau ba juma'a ba wannan ma an watse.
Lungunsu ta sauka ta sallami mai mashin yanda taga mutane suna kallonta sai ta ƙara tsinkewa, tana shiga gidansu taga matan maƙwafta da Yayyanta ai sai ta saki jakar hannunta tana kuma duban ɗakin Affa an ɗaga labule ga dangin babanta maza na Katsina. Yaya Murja ta ce "Oyoyo ga Ruƙayya." Sauran suka fito sun kula a firgice take, ta ce "ina Umma?" Suka ce gata nan a ɗakinta, ta faɗa ɗakin ga mamakin ta sai taga Umma zaune tasha ƙwalliya sai tayi ajiyar zuciya hankalinta ya ɗan ƙwanta ta ce "Wayyo har naji daɗi wallahi nasha ke ce babu a firgice nazo garin nan, wai meke faruwa ne? Yayyanta da suka zagaye da ita suka ce zakiji gurin Affa da ya dawo ba mutuwa bace,sai taji koma menene da sauƙi.
Bayan ta ci abinci sama-sama tayi wanka bata kai ga shafa mai ba, Yaya Murja ta ce Affa nason ganinta, hijabi ta saka kan zaninta iya ƙirji tayi ɗakin Umma yanzu duk maƙwafta sun tafi sai Yayyanta,ta zauna ta gaida Affa ya amsa cike da murna shima yasha ado, ya ce Ruƙayya nasan cewa ke kullum mai biyayya ce ina matuƙar alfahari dake. Shiyasa a yau na ɗaura miki aure ba tare da na nemi izni ko yardar ki ba. Nasan ba zaki bani kunya ba, kanta a ƙasa dama tunda taga ba mutuwa ba ce tasan dai baya wuce haka.
Gabanta yana faÉ—uwa ranta yana raya mata shikenan sun bar juna da Dady. Amma sai taji gara da hakan tunda ita ta kasa sauraron kowa.
Ta ɗago idonta yana ɗigar da hawaye ta ce Affa nagode Allah yasa hakan shine mafi alkhairi,ba zanƙi zaɓin ka ba." Affa ya ce nagode Ruƙayya amma ban ji kin tambaya wanene mijin ba? Ta ce ai Affa ba sai na tambaya ko wanene ba, tunda dai yayi maka nima yayi min." Affa ya faɗaɗa fara'arshi ya ce To albishirin ki. Ta ɗago tana dubanshi bata ce komai ba ya cigaba.
Dadynki wato Yusufa Allah ya yarda shine dai mijinki." Ido ta tsura ma Affa tana tunanin ko mafarki ne...... Shin ba wancan satin taji yana sanar da Affa auranshi ba? Shine ya ganta ya yi banza da ita shine ya karya alƙawarin ta da har yanzu ita tana tare da alƙawarinsu.
Ta dubi zoben hannunta ta girgiza. Affa ban son Dady,da ne na soshi yanzun bazan iya auran shi ba ka zaɓa min wani cikin kuka rurus take maganar.
Affa ya saki baki yana kallon ta,a zaton shi daya faɗa zata hau murna amma sai yaga akasin hakan,. Ya ce "Kina son shi Ruƙayya da,nine na hana a yanzun kada ki damu na yarda nine ma na fara amince mishi. Na ce Affa duk abinda Dad ɗin shi ya yi maka? Ni dai bana son shi, Affa ya ce Kiyi haƙuri Ruƙayya lokaci ya riga ya ƙure,an riga an ɗaura aure,kije nasan insha Allahu ba zakiyi kuka da Dady ba. Ki riƙe shi zaɓina kiyi biyayyar nan dai da kika sa ba."
Ta ce "To nagode Affa." Ta tashi kuka sosai take yi su Yayyanta sun sha mamakin wai Ruƙayya ke kukan bata son Dady. Murja ta ce me yayi miki? Ta ce cikin kuka "babu ni dai bana son shi,ko da ɗin ma dan dai bansan ciwon kaina bane." Su Yaya Sadiya da Yaya Suwaiba tashi suka yi daga gurinta suka ce kar ta soshi shegiya. Amina kuwa dama Dady tai ma waya cewar Ruƙayya tana isowa, ta kirashi ta sanar dashi a waya, haka kuwa tayi yanzu sai ga wayarshi yana sanar da ita gasu nan shi da wasu Abokanshi ya ce kice mata tayi ƙyau dan Abokaina sun matsu su ga wacece wannan ta haukatar musu da gentleman ɗin su? Amina ta yi dariya ta ce "To ƙanina."
Da farko cewa tayi ba zata ba sai da Umma tai mata tatas ta ce ta zauna ɗin,ai mu bamu isa da ita ba sannan fa su Murja suka lallaɓa ta suka gyara ta sosai wani jan leshi suka zaɓo mata cikin kayan ta dan ba'a riga an kawo lefe ba,farin takalmi da gyale suka bata ta fita tana zunɓura baki.
Sun kai su ashirin abokanshi suna sanye da cikin anko na ɗaurin aure,nan taja gyale ta rufe fuskarta. Shi kam Dady wani ƙwarjininta ya ji matuƙa sai yaji yana jin shakkar ta, Sadiƙ ya ce "baki isa ba ai ki buɗe mana fuska mu ganki." Dady kam kasa magana ya yi ya jingina da bango yana kallonta.
Ta buɗe fuska ta ce "Ina wunin ku." Suka amsa suna ta yi mata tsiya ta rikita musu aboki. Ta ƙi magana sai murmushin dole take yi saboda kada ta bada shi,ta ɗan dubeshi ta ɗan ranƙwafa ta ce ina yini? Kamar an sashi cikin aljanna ya ce lafiya lau Pretty na suna ta damun ki ko? Ta ɗan haɗe hannayenta guri guda ta ce ba komai. Abokansa suka ce to sai mun haɗu gurin dinner ta dubeshi yanzun za'ayi dinner ba zaku bari sai lokacin tarewa ba? Suka ce a'a wannan wasu ne suka shirya muku, ta ce To Allah ya kaimu anjiman. Suka tafi suna yaba tsarin yarinyar har sha'awar tarbiyyarta, wasu ko cewa suke kaga wai lafiyayyen jiki? Dole Son Guy ya ruɗe.
Bayan sun tafi ya rage shi da ita ya miƙe yana duban fuskarta. Ta ci magani tamkar ba ita ba, Ya ce Pretty na gashi dai Allah ya......" Ta ɗago idanun nan nata waɗanda suke matuƙar birgeshi, ta ɓalla mishi harara,nan take ya yi shiru ta ce "Dady manyan ƙasa,nifa yanzun ba Ruƙayyan da bace da ka sani, yanzun wannan babu Dady a ranta kamar yanda ya manta da ita, kada kaga cewa Affa ya cusa maka ni,ka ɗauka ina son ka har yanzu? Ya yi murmushi ya ce Pretty kenan,ai ni burina in aure ki,ko ki soni ko ki ƙini Pretty ni mijinki ne nasan kuma ina sonki. Ko? Ta dube shi kamar gaske ya ce da wasa ne?"
Sam bata cikin haiyacin ta gani take an ɓoye mata ne babu wanda bata kira ba cikin Yayyanta amma duk sun ce ba komai kuma basu san kiran da Affa yake mata ba,kona menene?.
Nuraddeen ta kira take sanar dashi abin da yake faruwa, yazo gurinta suna tattauna maganar ya ce ta ƙwantar da hankalinta insha Allahu babu komai, kuma ta bar tafiyar sai gobe, tun da yau lokaci ya ƙure,
*** **** ****
Tun Asubahi tana cikin motar mocopolo duk ta ƙosa ta ganta gida dan jin meke faruwa?.
Wayewar garin wato ranar ɗaurin aure ai kada kuso kuga ango wanda dama ƙwana ya yi bai runtsa ba,nafilfili yake yi yana roƙon Allah kar ya kawo sanadin fasa auran. Da safen ne yana fitowa wanka.
Zainab ta kirashi inda take mishi ƙorafin rashin kiranta tunda ta dawo, har ga Allah shi yama manta da wata Zainab baya tuna komai sai Pretty ɗin shi. Ya ce "Kiyi haƙuri abubuwa sun min yawa yasu Hajiya?" Ta ce lafiya,dama ina son kuɗi ne. Ya ce me zakiyi dasu ne? Bana baki dubu hamsin da zaki tafi ba? Ta ce To ai anayin kayan faɗar kishiya kuma ba kai min ba, ya ce aiko ita ma Pretty ɗin ba riga na mata kayan ba tukunna, ta ce to nidai kuɗin zaka bani, ya ce,zan turo miki, ta ce nawa? Abin ya soma bashi haushi ya ce yanda naga dama ya kashe wayar,shi fa haushin ta yake ji itace dai bata sani ba.
Yana gama shiri gurin abokanshi ya nufa can ya yi break. Hira suke suna ta shaƙiyancin su, yayin da gidan su Momy ya ɗinke da jama'a wannan karon har da Hafsi tazo da yaranta guda biyu daga Kalaba inda mijinta yake aiki. Aure kawai za'a ɗaura amma an cika fiye da wancan satin.
Dady kuwa yasaka kaya sun kai kala goma Yana cirewa sai yaga basu dace da É—aurin auren ba, duk da kasancewar kayan sababbi ne. Duk yasa aka siyo su daga Togo aka kaisu É—inki.
A ƙarshe ya haƙura cikin wata shegiyar mai masifar ƙyau, green dark hular dama tare aka kawo su,yana fitowa sai da ya birge abokanshi gurin Momy ya shiga tana cikin ƙawayenta babu wanda Dady bai birge ba, Momy kam Babu wanda ya kai ta farin ciki wannan rana, ɗan ta ya samu abin da yafi so.
Hatta motar da Dady ya hau wannan rana sabuwa ce mai shegen tsada,so kam abokanshi kayan su iri ɗaya suka sa wani farin yadi mai shegen tsada suka ɗinka gaba ɗayansu abin birgewa har da waɗanda ba baƙaƙen fata ba wasu turawa. Su Sadiƙ ne suka ɗinka duk wanda yazo indai aboki ne sai a bashi yasa. Unguwar Kabala ta ɗinke da jama'a tamkar taron idi. Tun daga farkon layin har ƙarshe dole ne sai anyi amfani da lasifiƙa wurin ɗaurin auren.
**** **** ****
Ruƙayya da yake tasowar ƙarfe huɗun Asubahi suka yi kuma motar tayi shegen gudu, huɗu saura suka sauka. Mashin ta hau zuwa Kabala suna kusanto unguwar tasu gabanta ya na ƙara faɗuwa. Sanye take da wani leshi purple ba wata ƙwalliya da tayi amma hakan birge wasu take. Sun ratsa layin nasu cike da jama'a tayi mamaki yau ba juma'a ba wannan ma an watse.
Lungunsu ta sauka ta sallami mai mashin yanda taga mutane suna kallonta sai ta ƙara tsinkewa, tana shiga gidansu taga matan maƙwafta da Yayyanta ai sai ta saki jakar hannunta tana kuma duban ɗakin Affa an ɗaga labule ga dangin babanta maza na Katsina. Yaya Murja ta ce "Oyoyo ga Ruƙayya." Sauran suka fito sun kula a firgice take, ta ce "ina Umma?" Suka ce gata nan a ɗakinta, ta faɗa ɗakin ga mamakin ta sai taga Umma zaune tasha ƙwalliya sai tayi ajiyar zuciya hankalinta ya ɗan ƙwanta ta ce "Wayyo har naji daɗi wallahi nasha ke ce babu a firgice nazo garin nan, wai meke faruwa ne? Yayyanta da suka zagaye da ita suka ce zakiji gurin Affa da ya dawo ba mutuwa bace,sai taji koma menene da sauƙi.
Bayan ta ci abinci sama-sama tayi wanka bata kai ga shafa mai ba, Yaya Murja ta ce Affa nason ganinta, hijabi ta saka kan zaninta iya ƙirji tayi ɗakin Umma yanzu duk maƙwafta sun tafi sai Yayyanta,ta zauna ta gaida Affa ya amsa cike da murna shima yasha ado, ya ce Ruƙayya nasan cewa ke kullum mai biyayya ce ina matuƙar alfahari dake. Shiyasa a yau na ɗaura miki aure ba tare da na nemi izni ko yardar ki ba. Nasan ba zaki bani kunya ba, kanta a ƙasa dama tunda taga ba mutuwa ba ce tasan dai baya wuce haka.
Gabanta yana faÉ—uwa ranta yana raya mata shikenan sun bar juna da Dady. Amma sai taji gara da hakan tunda ita ta kasa sauraron kowa.
Ta ɗago idonta yana ɗigar da hawaye ta ce Affa nagode Allah yasa hakan shine mafi alkhairi,ba zanƙi zaɓin ka ba." Affa ya ce nagode Ruƙayya amma ban ji kin tambaya wanene mijin ba? Ta ce ai Affa ba sai na tambaya ko wanene ba, tunda dai yayi maka nima yayi min." Affa ya faɗaɗa fara'arshi ya ce To albishirin ki. Ta ɗago tana dubanshi bata ce komai ba ya cigaba.
Dadynki wato Yusufa Allah ya yarda shine dai mijinki." Ido ta tsura ma Affa tana tunanin ko mafarki ne...... Shin ba wancan satin taji yana sanar da Affa auranshi ba? Shine ya ganta ya yi banza da ita shine ya karya alƙawarin ta da har yanzu ita tana tare da alƙawarinsu.
Ta dubi zoben hannunta ta girgiza. Affa ban son Dady,da ne na soshi yanzun bazan iya auran shi ba ka zaɓa min wani cikin kuka rurus take maganar.
Affa ya saki baki yana kallon ta,a zaton shi daya faɗa zata hau murna amma sai yaga akasin hakan,. Ya ce "Kina son shi Ruƙayya da,nine na hana a yanzun kada ki damu na yarda nine ma na fara amince mishi. Na ce Affa duk abinda Dad ɗin shi ya yi maka? Ni dai bana son shi, Affa ya ce Kiyi haƙuri Ruƙayya lokaci ya riga ya ƙure,an riga an ɗaura aure,kije nasan insha Allahu ba zakiyi kuka da Dady ba. Ki riƙe shi zaɓina kiyi biyayyar nan dai da kika sa ba."
Ta ce "To nagode Affa." Ta tashi kuka sosai take yi su Yayyanta sun sha mamakin wai Ruƙayya ke kukan bata son Dady. Murja ta ce me yayi miki? Ta ce cikin kuka "babu ni dai bana son shi,ko da ɗin ma dan dai bansan ciwon kaina bane." Su Yaya Sadiya da Yaya Suwaiba tashi suka yi daga gurinta suka ce kar ta soshi shegiya. Amina kuwa dama Dady tai ma waya cewar Ruƙayya tana isowa, ta kirashi ta sanar dashi a waya, haka kuwa tayi yanzu sai ga wayarshi yana sanar da ita gasu nan shi da wasu Abokanshi ya ce kice mata tayi ƙyau dan Abokaina sun matsu su ga wacece wannan ta haukatar musu da gentleman ɗin su? Amina ta yi dariya ta ce "To ƙanina."
Da farko cewa tayi ba zata ba sai da Umma tai mata tatas ta ce ta zauna ɗin,ai mu bamu isa da ita ba sannan fa su Murja suka lallaɓa ta suka gyara ta sosai wani jan leshi suka zaɓo mata cikin kayan ta dan ba'a riga an kawo lefe ba,farin takalmi da gyale suka bata ta fita tana zunɓura baki.
Sun kai su ashirin abokanshi suna sanye da cikin anko na ɗaurin aure,nan taja gyale ta rufe fuskarta. Shi kam Dady wani ƙwarjininta ya ji matuƙa sai yaji yana jin shakkar ta, Sadiƙ ya ce "baki isa ba ai ki buɗe mana fuska mu ganki." Dady kam kasa magana ya yi ya jingina da bango yana kallonta.
Ta buɗe fuska ta ce "Ina wunin ku." Suka amsa suna ta yi mata tsiya ta rikita musu aboki. Ta ƙi magana sai murmushin dole take yi saboda kada ta bada shi,ta ɗan dubeshi ta ɗan ranƙwafa ta ce ina yini? Kamar an sashi cikin aljanna ya ce lafiya lau Pretty na suna ta damun ki ko? Ta ɗan haɗe hannayenta guri guda ta ce ba komai. Abokansa suka ce to sai mun haɗu gurin dinner ta dubeshi yanzun za'ayi dinner ba zaku bari sai lokacin tarewa ba? Suka ce a'a wannan wasu ne suka shirya muku, ta ce To Allah ya kaimu anjiman. Suka tafi suna yaba tsarin yarinyar har sha'awar tarbiyyarta, wasu ko cewa suke kaga wai lafiyayyen jiki? Dole Son Guy ya ruɗe.
Bayan sun tafi ya rage shi da ita ya miƙe yana duban fuskarta. Ta ci magani tamkar ba ita ba, Ya ce Pretty na gashi dai Allah ya......" Ta ɗago idanun nan nata waɗanda suke matuƙar birgeshi, ta ɓalla mishi harara,nan take ya yi shiru ta ce "Dady manyan ƙasa,nifa yanzun ba Ruƙayyan da bace da ka sani, yanzun wannan babu Dady a ranta kamar yanda ya manta da ita, kada kaga cewa Affa ya cusa maka ni,ka ɗauka ina son ka har yanzu? Ya yi murmushi ya ce Pretty kenan,ai ni burina in aure ki,ko ki soni ko ki ƙini Pretty ni mijinki ne nasan kuma ina sonki. Ko? Ta dube shi kamar gaske ya ce da wasa ne?"