Sashe 11
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Armaya'u ta ce ban ma ga abin damuwa ba tun da tasan irin son da yake miki." Ruƙy ta ce ke rabamu da mazan nan munafukai ne yazo ya ce min I love You yaje ya ce mata I miss You." M Bash ta ce koma menene yanzu dai ki dage da shan kankana da aya da dabino,da ƴan kayan marmarin nan muna rainasu, aƙwai aiki zaki gane in kin kama su, kuma akwai wasu sinadarai da Mom ta bani na Arabic ne, Armaya'u ta ce nifa? M Bash ta ce a'a sai anyi bikinki zan baki, ta ce One month fa ya rage, ta ce to zan baki sai kin zo Abuja, Armaya'u ta ce zan zo amma kafin nan zan je in fara amfani dasu kankana ɗin, Ruƙayya ta ce kai ku rabu dani ya ma samu in tare gidan shi bare ma har na tsaya shan wani abu aje a ƙwararraɓa ni, dariya suka saka mata, M Bash ta ce yanzu duk kishi ne matsalar ki,kina shiga hannunshi shiru za'a ji ki tunda kina sonshi. Ruƙayya ta ce zaku sha mamaki aini bana son cin amana, kuma zan nuna mishi mu mata dabanne. M Bash ta ce ina son fita anjima mu ɗan shiga kasuwa.
Bayan sun ci sun sha girkin da Umma tai musu can gurin la'asar suka shirya zuwa kasuwa, Ruƙayya ta ce Umma zamu kasuwa, Umma ta ce ki ma mijinki waya ki sanar dashi, takaici ya cika Ruƙayya su Sadiya suka ce ki kirashi, ta ce ya tafi da wayar ai, Armaya'u ta kirashi da tawa, ta ce ai ban ma riƙe number ɗin shi ba,ke ni ban ma san me zance mishi ba." M Bash ta ce bari na kira number Al-Mustapha ya yi min text ɗin number Dadyn.
A wayar Armaya'u suka kira M Bash ta ce Ruƙy M gashi tana ringing ta amsa tana cewa me zan ce mishi? Ya ɗauka ya ce "Hello," ta yi shiru ya ce "who is speaking?" Ta ce Ni ce, duk da ciki-ciki ta yi maganar hakan be hanashi gane muryarta ba, ya ce Pretty ya ya ne? Ta ce kasuwa zamu je, tana wani ɗaure fuska tamkar tana ganinshi, ya ce to bari na turo muku direba, ta ce daka barshi zamu hau mashin.
Da sauri ya ce kada ki yarda ki hau mashin ki jira ni, ta kashe wayar ranta ɓace ta ce kunji ko ya samu na kira shi har da cewa kar na yarda na hau mashin wai mu jira shi. Armaya'u ta ce yana da gaskiya aje a yadda mishi mata, M Bash ta ce ƙyale ta da Allah da kanta zakiga ta ƙanƙame mijinta. Ruƙayya ta ce sai kuma kuyi,wayar Armaya'u ya kuma kira ya ce su fito, baya suka shiga.
Ruƙayya na ƙoƙarin shigowa bayan suka tura ta ta zauna gurin mijinta, dole ta zauna gaba tana wani zumɓura baki, ta ɗan saci kallon shi a ranta ta ce ya ci sunanshi Son Guy ko yaushe cikin gayu yake, yanzun ma jeans ne baƙi da baƙar riga mai dogon hannu ta ɗameshi, fuskarshi fes sai ƙyakƙyawan sajen da ya kewaye bakinshi zuwa gefen fuskarshi, idanunshi masu hasken nan suna birgeta.
Ya tada mota yana cewa "Wai ke kallon fa?" Gabanta ya faɗi ashe ya gane, ta dake ta ce "Me zan kalla a nan?" Ya yi murmushi sannan ya ɗan ɗaga murya ya ce wace kasuwar zamu? M Bash ta ce Ruƙy wace zamu je? Ta ce ka kaimu Abubakar Gumi, ya ce me zaki siya? Ta ce sune zasu yi siyayya, ya ce baki da kuɗi ne,in ga jakarki,ta ce a'a ni ba'a ganar min jaka,kai ka cika tsokana kayi abin da ke gabanka..........
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/16, 08:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 6
Ya ce "ai ni kece a gabana komai na Prettyna." Ta kuma shan mur.
Haka ya yi ta janta da magana tayi mai shiru har suka je kasuwa. Shagon wasu masu leshi da materials suka yada zango,ƴanmatane keta siyayya a shagon Dady yana daga ƙofar shagon yana duban Pretty ɗin shi suna taya M Bash zaɓe, duk abinda take yi baya gajiya da kallon ta, komai nata birgeshi yake yi.
Wasu ƴanmata da tun zuwansu gurin suka maida hankali kan Dady ya tafi da imaninsu,ɗayar ta ɗebi wasu lesuka guda biyu tazo gabanshi don Allah Malam muna musu ne wanne yafi ƙyau? Ya ce a'a ni ban san kayan mata ba, ga mata can ƴan uwanku. Sai cewa tayi to kai wanne yafi maka ƙyau? Nan take yasha kunu ya ce ban sani ba. Ya maida dubanshi ga Pretty ɗin shi suka haɗa ido ranta a ɓace a zatonta shi ya soma yi musu magana. Ya shiga falon kun gama? Yana magana yana kallonta ta juya mai kai.
M Bash ta ce ɗaya na ɗauka kayan su nada tsada, ya ce kema Sadiya ɗauki naki, shi kuma ya ɗauki biyu, ya haɗa ya biya suka sa musu a cikin ledoji, shagon wasu inyamurai suka shiga siyen jaka da takalmi ɗayan sai kallon Ruƙayya yake yi.
Dady yana kula dashi, Ruƙayya ta ce,a ɗauko mata ɗan mara tudu ya ce to Baby,su M Bash suka wuce wajen zaɓen jaka ya kawo mata takalmin ya ce "wannan zai dace dake kinada ƙyau fa." Ya tsugunna gabanta kamar zai kama ƙafarta yasa mata. Dady ya ce "tashi ki fito tashi." Ta dubeshi fuskarshi tamkar bai taɓa dariya ba ta miƙe ya ce Munira ku zo muje, suka ce bari in bashi kuɗin.
Ya tasa Pretty ɗin tashi a gaba suka nufi gurin mota,suma suka biyo su a mota sai masifa yake yi shi baya son irin wannan kasuwar, dubi kamar zasu taɓa mace ko baya nan be yarda ta kuma zuwa nan ba. A ranta ta ce ji irin ikon nashi, shi daya tsaya yana magana da ƴanmata amma ita daga gani yana kallonta ya ce su baro kasuwa. Wata super market ya tsaya suka shiga ya ce su ɗibi duk abinda suke so Ruƙayya dai bata yi yunƙurin ɗaukar komai ba tsayawa tayi tana kallon su, Dady ya wuce yana ɗiban abubuwa,sai da yayo leda huɗu aka haɗa aka gaya mishi kuɗin, ya biya duka da ya sauke su ya ce Pretty ga kayan nan, ta ce babu abin da zanyi dasu, ya aje ya ce ki barsu nan, ya figi mota ya yi gaba.
Munira da Armaya'u sai masifa suke yi mata, ta ce tunda ya yi muku siyayya ai dole ne ku dinga goyan bayan shi. M Bash ta ce shegen taurin kan kin nan ki rage shi yarinya da kishiya zaki zauna, tsaki ta ja sannan tayi gaba suka ce shegiya gara ma kinzo kin ƙwashe kayan ki,kishi na cinki,yara suka roƙo suka ƙwashe musu kayan.
*** *** ***
Dare ya aiko Sabi'u ya gaya mata jirgin ƙare baƙwai zata hau zuwa Legos ta shirya da wuri. Tun dare suka yi sallama da aminanta, bayan sun raba dare suna hira, daga sallar asubahi kowa ya hau shiri ya bada mota Sabi'u ya kai Armaya'u tasha ya yin da Munira direbansu zai zo ya ɗauke ta.
A cikin mota ya dubeta,ko ta bashi haushi yana dubeta sai yaji ya huce, cikin sanyin murya ya ce ba gaisuwa Pretty? Ko ba'a sona na ci arziƙin aure ko?" Ta ina gajiya ya Momy? Ya yi ajiyar zuciya sannan Ya ce tace in gaida ki." Bata amsa ba ya ce ina tunanin sati mai zuwa in yazo zan sama miki gida ƙarami ki koma, ta ce ban ce ba,ka barni inda ka ganni, ya ce shikenan na barki, ta ce wayata fa? Ya ce gata,miƙo mata wata sabuwar waya mai shegen ƙyau ya yi, ta ce ni tawa nike so, ya ce tuni nayi ƙyauta da ita har layin ma zan ɗauki komai amma ban da waya da wasu ƙattai sannan ki kiyayi wani Nuri da naga yafi kowa kiranki, kuma inbox ɗin ki ba text ɗin kowa sai nashi in ya yi wasa ba zai ji da daɗi ba kin jini?"
Yanda yake maganar rai a ɓace shine ya hanata yi mishi tsiwa, sai da yaga komai ya kammala har sun soma shiga jirgi sannan ya tafi ita kam tunani take yi a ranta yau gata a jirgi. A can ma tana sauka sai ga wani yazo ya ce itace Ruƙayya? Ta ce Eh, ya ce yazo ne zai kaita gurin aikin su. Abokan service ɗin ta suna ta mata murnar aure dan da yawa sai da suka yi mata ƙorafin rashin gayyatar su, ta ce aure kawai aka ɗaura wannan dinner ma abokan mijin ne suka haɗa, Nuraddeen ne kaɗai ta zayyane ma komai.
Tana ta fama da waya, waya taƙi tayi sai dai wasu daga numbers daga nashi daga nashi daya sa mata ta Mom sai ta Yayyanta da ta Munira da Armaya'u,sai dai nasa number na kira amma ba dai na.
Haka suka ci gaba da gungurawa, kullum Dady zai kirata tana dakewa tana komai, zasu yi magana ko yayi tayi taƙi amsa mishi, amma duk ranar da be bar kira ba bata da sauran ƙwanciyar hankali har sai ya kira sannan zata samu natsuwa. Tuni ya koma Abuja bakin aikin shi ranar da ya koma ranar Zainab ta dawo, duk da irin soyayyar da yaga tana nuna mishi tare da ƙaramar hukumar maji daɗi da take gayyatar shi suna lulawa besa ya kasa gano ƙaramar ƙwasƙwarimar da aka yi mata ba kuma be sa ya manta da Pretty ɗin shi ba wani lokacin ma a gabanta ma zai ma Pretty ɗin waya.
Wata rana da dare misalin ƙarfe goma Ruƙayya ta kira shi don ta sanar dashi gobe zasu yi tafiya gaida wata abokiyar aikinsu a ibadan kuma tayi tunanin ta yi tafiyar ta kawai sai kuma ta tuna doguwar hanya zasu hau don haka sai ta kirashi.
Bayan sun ci sun sha girkin da Umma tai musu can gurin la'asar suka shirya zuwa kasuwa, Ruƙayya ta ce Umma zamu kasuwa, Umma ta ce ki ma mijinki waya ki sanar dashi, takaici ya cika Ruƙayya su Sadiya suka ce ki kirashi, ta ce ya tafi da wayar ai, Armaya'u ta kirashi da tawa, ta ce ai ban ma riƙe number ɗin shi ba,ke ni ban ma san me zance mishi ba." M Bash ta ce bari na kira number Al-Mustapha ya yi min text ɗin number Dadyn.
A wayar Armaya'u suka kira M Bash ta ce Ruƙy M gashi tana ringing ta amsa tana cewa me zan ce mishi? Ya ɗauka ya ce "Hello," ta yi shiru ya ce "who is speaking?" Ta ce Ni ce, duk da ciki-ciki ta yi maganar hakan be hanashi gane muryarta ba, ya ce Pretty ya ya ne? Ta ce kasuwa zamu je, tana wani ɗaure fuska tamkar tana ganinshi, ya ce to bari na turo muku direba, ta ce daka barshi zamu hau mashin.
Da sauri ya ce kada ki yarda ki hau mashin ki jira ni, ta kashe wayar ranta ɓace ta ce kunji ko ya samu na kira shi har da cewa kar na yarda na hau mashin wai mu jira shi. Armaya'u ta ce yana da gaskiya aje a yadda mishi mata, M Bash ta ce ƙyale ta da Allah da kanta zakiga ta ƙanƙame mijinta. Ruƙayya ta ce sai kuma kuyi,wayar Armaya'u ya kuma kira ya ce su fito, baya suka shiga.
Ruƙayya na ƙoƙarin shigowa bayan suka tura ta ta zauna gurin mijinta, dole ta zauna gaba tana wani zumɓura baki, ta ɗan saci kallon shi a ranta ta ce ya ci sunanshi Son Guy ko yaushe cikin gayu yake, yanzun ma jeans ne baƙi da baƙar riga mai dogon hannu ta ɗameshi, fuskarshi fes sai ƙyakƙyawan sajen da ya kewaye bakinshi zuwa gefen fuskarshi, idanunshi masu hasken nan suna birgeta.
Ya tada mota yana cewa "Wai ke kallon fa?" Gabanta ya faɗi ashe ya gane, ta dake ta ce "Me zan kalla a nan?" Ya yi murmushi sannan ya ɗan ɗaga murya ya ce wace kasuwar zamu? M Bash ta ce Ruƙy wace zamu je? Ta ce ka kaimu Abubakar Gumi, ya ce me zaki siya? Ta ce sune zasu yi siyayya, ya ce baki da kuɗi ne,in ga jakarki,ta ce a'a ni ba'a ganar min jaka,kai ka cika tsokana kayi abin da ke gabanka..........
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/16, 08:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 6
Ya ce "ai ni kece a gabana komai na Prettyna." Ta kuma shan mur.
Haka ya yi ta janta da magana tayi mai shiru har suka je kasuwa. Shagon wasu masu leshi da materials suka yada zango,ƴanmatane keta siyayya a shagon Dady yana daga ƙofar shagon yana duban Pretty ɗin shi suna taya M Bash zaɓe, duk abinda take yi baya gajiya da kallon ta, komai nata birgeshi yake yi.
Wasu ƴanmata da tun zuwansu gurin suka maida hankali kan Dady ya tafi da imaninsu,ɗayar ta ɗebi wasu lesuka guda biyu tazo gabanshi don Allah Malam muna musu ne wanne yafi ƙyau? Ya ce a'a ni ban san kayan mata ba, ga mata can ƴan uwanku. Sai cewa tayi to kai wanne yafi maka ƙyau? Nan take yasha kunu ya ce ban sani ba. Ya maida dubanshi ga Pretty ɗin shi suka haɗa ido ranta a ɓace a zatonta shi ya soma yi musu magana. Ya shiga falon kun gama? Yana magana yana kallonta ta juya mai kai.
M Bash ta ce ɗaya na ɗauka kayan su nada tsada, ya ce kema Sadiya ɗauki naki, shi kuma ya ɗauki biyu, ya haɗa ya biya suka sa musu a cikin ledoji, shagon wasu inyamurai suka shiga siyen jaka da takalmi ɗayan sai kallon Ruƙayya yake yi.
Dady yana kula dashi, Ruƙayya ta ce,a ɗauko mata ɗan mara tudu ya ce to Baby,su M Bash suka wuce wajen zaɓen jaka ya kawo mata takalmin ya ce "wannan zai dace dake kinada ƙyau fa." Ya tsugunna gabanta kamar zai kama ƙafarta yasa mata. Dady ya ce "tashi ki fito tashi." Ta dubeshi fuskarshi tamkar bai taɓa dariya ba ta miƙe ya ce Munira ku zo muje, suka ce bari in bashi kuɗin.
Ya tasa Pretty ɗin tashi a gaba suka nufi gurin mota,suma suka biyo su a mota sai masifa yake yi shi baya son irin wannan kasuwar, dubi kamar zasu taɓa mace ko baya nan be yarda ta kuma zuwa nan ba. A ranta ta ce ji irin ikon nashi, shi daya tsaya yana magana da ƴanmata amma ita daga gani yana kallonta ya ce su baro kasuwa. Wata super market ya tsaya suka shiga ya ce su ɗibi duk abinda suke so Ruƙayya dai bata yi yunƙurin ɗaukar komai ba tsayawa tayi tana kallon su, Dady ya wuce yana ɗiban abubuwa,sai da yayo leda huɗu aka haɗa aka gaya mishi kuɗin, ya biya duka da ya sauke su ya ce Pretty ga kayan nan, ta ce babu abin da zanyi dasu, ya aje ya ce ki barsu nan, ya figi mota ya yi gaba.
Munira da Armaya'u sai masifa suke yi mata, ta ce tunda ya yi muku siyayya ai dole ne ku dinga goyan bayan shi. M Bash ta ce shegen taurin kan kin nan ki rage shi yarinya da kishiya zaki zauna, tsaki ta ja sannan tayi gaba suka ce shegiya gara ma kinzo kin ƙwashe kayan ki,kishi na cinki,yara suka roƙo suka ƙwashe musu kayan.
*** *** ***
Dare ya aiko Sabi'u ya gaya mata jirgin ƙare baƙwai zata hau zuwa Legos ta shirya da wuri. Tun dare suka yi sallama da aminanta, bayan sun raba dare suna hira, daga sallar asubahi kowa ya hau shiri ya bada mota Sabi'u ya kai Armaya'u tasha ya yin da Munira direbansu zai zo ya ɗauke ta.
A cikin mota ya dubeta,ko ta bashi haushi yana dubeta sai yaji ya huce, cikin sanyin murya ya ce ba gaisuwa Pretty? Ko ba'a sona na ci arziƙin aure ko?" Ta ina gajiya ya Momy? Ya yi ajiyar zuciya sannan Ya ce tace in gaida ki." Bata amsa ba ya ce ina tunanin sati mai zuwa in yazo zan sama miki gida ƙarami ki koma, ta ce ban ce ba,ka barni inda ka ganni, ya ce shikenan na barki, ta ce wayata fa? Ya ce gata,miƙo mata wata sabuwar waya mai shegen ƙyau ya yi, ta ce ni tawa nike so, ya ce tuni nayi ƙyauta da ita har layin ma zan ɗauki komai amma ban da waya da wasu ƙattai sannan ki kiyayi wani Nuri da naga yafi kowa kiranki, kuma inbox ɗin ki ba text ɗin kowa sai nashi in ya yi wasa ba zai ji da daɗi ba kin jini?"
Yanda yake maganar rai a ɓace shine ya hanata yi mishi tsiwa, sai da yaga komai ya kammala har sun soma shiga jirgi sannan ya tafi ita kam tunani take yi a ranta yau gata a jirgi. A can ma tana sauka sai ga wani yazo ya ce itace Ruƙayya? Ta ce Eh, ya ce yazo ne zai kaita gurin aikin su. Abokan service ɗin ta suna ta mata murnar aure dan da yawa sai da suka yi mata ƙorafin rashin gayyatar su, ta ce aure kawai aka ɗaura wannan dinner ma abokan mijin ne suka haɗa, Nuraddeen ne kaɗai ta zayyane ma komai.
Tana ta fama da waya, waya taƙi tayi sai dai wasu daga numbers daga nashi daga nashi daya sa mata ta Mom sai ta Yayyanta da ta Munira da Armaya'u,sai dai nasa number na kira amma ba dai na.
Haka suka ci gaba da gungurawa, kullum Dady zai kirata tana dakewa tana komai, zasu yi magana ko yayi tayi taƙi amsa mishi, amma duk ranar da be bar kira ba bata da sauran ƙwanciyar hankali har sai ya kira sannan zata samu natsuwa. Tuni ya koma Abuja bakin aikin shi ranar da ya koma ranar Zainab ta dawo, duk da irin soyayyar da yaga tana nuna mishi tare da ƙaramar hukumar maji daɗi da take gayyatar shi suna lulawa besa ya kasa gano ƙaramar ƙwasƙwarimar da aka yi mata ba kuma be sa ya manta da Pretty ɗin shi ba wani lokacin ma a gabanta ma zai ma Pretty ɗin waya.
Wata rana da dare misalin ƙarfe goma Ruƙayya ta kira shi don ta sanar dashi gobe zasu yi tafiya gaida wata abokiyar aikinsu a ibadan kuma tayi tunanin ta yi tafiyar ta kawai sai kuma ta tuna doguwar hanya zasu hau don haka sai ta kirashi.