Sashe 5
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Waya ya yima family Doctor ɗin sa,nan da nan sai gashi ya duba shi. Dady mura ce da ƴar damuwa ke damun shi,muran ce ma tasa masa zazzaɓi ya yi masa allurai dan ya samu bacci sannan ya rubuta magunguna. Dad ya ce to ban da abin Son menene na shiga damuwa,kai da zaka shiga sabuwar rayuwa. Momy ta ce ban sanar da kai bane jiya fa yaga Ruƙayya domin hankalinshi tashe ya zo min. Gaban Dad ya yi mugun faɗuwa a zuciyarshi ya ce innalillahi wa'inna ilaihir raji'un.
Kasa magana ya yi har sai da Dakta ya tafi bacci mai nauyi ya ɗauki Dady, Dad ya dubi Momy ya ce "Hajiya yanzun ya ya zamuyi ne? Momy ta ce "Uhm kai dai bari, haka za'a cigaba da biki kawai,in matar ta zo in tana kula dashi ƙila ya mance da Ruƙayya." Dad ya ce "In ma za'a bashi ba sai ya aura ya haɗa su ba."
Ta ce haka ne abin nan ya isheni. Ya ce bari in angama wannan zan je Katsina filin nan da aka maida gurin sha'anin biki ana bada haya to nan ne gonar tasu mahaifin Ruƙayya zan bashi in huta nima bada zalunci nayi ba duk laifin Jega ne shi ya shirya komai, to na haƙura nima cutata ya yi tunda kinga na daɗe da sallamar shi macuci ne na ƙarshe." Momy ta ce "Hakan ya yi sai mu nema masa auran Ruƙayya."
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/2, 07:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 3
Dad ya ce "Ni dai koda ba zan nema mai auran ta ba in basu in huta."
*** *** *** ***
An É—auro aure amma hankalin amarya a tashe don haka ba'a samu yin biki a can Abuja ba aka tarkato aka taho da amarya.
Dady ya farka bacci, Zainab ya gani zaune gefen shi tayi ado sosai sai dai hankalinta a tashe yake. Ya yi ƙoƙari ya yunƙura ya tashi zaune ya ce "Zee yaushe ki ka zo?" Ta ce "Tare muka zo dasu Dad da Abokanka,tasa hannu a wuyansa, jikinka babu zafi ka ji sauƙi." Ya ce "Alhamdulillahi." ta ce "To zaka yi wanka ne?" Ya ce da ruwa mai zafi. Ya fito wankan su Momy suka shigo duba shi abokanshi ma dana can Abuja dana nan duk sun cika falon shima yana jin su sai dai jikin babu ƙarfi sannan zuciyarshi na gurin Pretty da son ganin ta.
***. *** ***
Affa ya dubi Umma ya ce "Af har zan fita na manta ban sanar dake ba jiya yaron nan Yusufa da dare ya shigo yake sanar dani É—aurin auren shi,kin ji ikon Allah duk shekarun nan baiyi auran ba."
Umma ta ce "Oh ikon Allah, to Allah ya sanya alkhairi." Affa ya ce "kuma kin ji ashe duk saƙon nan shi ne yake aiko mana ina ta neman mai kawowa ashe shi ne." Umma ta ce aini zuciyata ta raya shi ne domin naga buhun shinkafar nan mai tumatur kuma ita ce yake kawo mana da, sanda yake neman Ruƙayya." Affa ya ce "ai koda aka fasa auran yaso ya cigaba da kawowa na hana tunda suka zo nan da uwarshi nace kada ya ƙara kawo mana komai mungode." Umma ta ce "Allah ya basu zaman lafiya," Affa ya ce Amin.
Duk zancen nan da suke yi a kunnen Ruƙayya abin duniya ya ishe ta sam ita fa da tasan haka zata fuskanta a zuwannan da bata zo ba, duk da tana shirin wai cire son Dady daga ranta, sai dai abin da yake ɓata mata rai shine har yanzu zuciyarta Dady kawai take ma dariya,yaya zata yi ne domin a ganinta shi Dady bai yi mata adalci ba har manta da ita yayi ya ganta ya yi kamar bai ganta ba, ƙarshen wulaƙanci shi ne ya tako har gida ya shaidawa Affanta auran shi ƙila ma da ita yaso ya shaidawa taƙi fitowa daya kira ta.
*** *** ***
Daran ranar Dady ya raka abokanshi na Abuja masaukin baƙinsu dake nan cikin layin su. Yayin da ƴan'uwan amarya suke can sashin su Momy.
Ya dawo ya zauna a falo tunanin shi ɗaya yana son zuwa gurin Pretty,ƙwarai ya so yaje yau da dare sai dai abokai ne ba zasu barshi ya fita shi ɗaya ba.
Sannan bai san yaya zasuyi da Affa ba ita kanta Pretty bai san nufin ta akan shi ba,ga zaton shi Zainab can gurin su Momy zata ƙwana, amma sai ji ya yi an dafashi ta ce "Tunanin me kake yi My dear?" Ya dubeta "Zee me yasa ba zaki je ki ƙwanta ba?" Ta ce Momy ta ce nazo saboda baka jin daɗi don kada ka ƙwana kai ɗaya,na shigo kuma sai na same ka kana tunani." A ranshi ya ce "Kada ki yarda ki san tunanin da zuciyata take yi." Ya miƙe "To muje." Bayi ta shiga tayo wanka, ta shafa turaruka tare da wasu sirrika da Hajiyarta ta bata,dan ma abin bai zo musu yarda suke so ba. Sun so kece raini a bikin musamman ranar dinner aƙwai shiri na musamman da Hajiyar taso tai mata, sai dai Kash! Rashin lafiyar Dady hakan bai samu ba.
Yana ƙwance rigingine ta zo ta ƙwanta kusa dashi tana kiran sunanshi a hankali yayin da ƙamshin daddaɗan turare ke tashi a jikinta.
Cikin natsuwa da hikima ta dinga janshi da hira tare da nuna masa irin so da ƙaunar da take yi masa domin ya samu ƙwanciyar hankali, dangane da fahimta da ta fara yi yana cikin damuwa.
Lamo ya ƙwanta tana jikinshi tana sharar bacci. Shi kam yana tunanin Pretty gani yake kamar bai mata adalci ba, yana ƙwance da wata ba Pretty ba. Yasan yau inda Pretty ce daran nan sai Allah kawai, amma yanda Zee ta nuna zalamar ta ta bashi haushi ace mace ba kara ba kunya shi bai son haka, to amma ba yanda zaya yi tunda matarsa ce sannan shima mabuƙaci ne.
Washegari da safe an aiko musu da break fast daga cikin gida. Shi kam bai ma tashi ba tunda ya yi sallah sai kusan sha É—aya. Ta zauna tana salo a gabanshi ya rasa sam bata birgeshi amma ya ya zaya yi wani sashe na zuciyarshi ya tuna mishi da wani abu da ya faru tsakanin Hussain da Madam É—in shi, ya ce mishi first night É—in su tasha wahala don sai da Dakta ya duba ta,da ya ce mishi nauyi kasa kaji mata ciwo? Sai ya ce kasan ita mace in virgin ce dole tasha wuya." Ya dubi Zainab sai yaji ranshi ya sosu, kenan dole wani ya santa, shi sam dai baiyi sa'a ba, domin bai kasance mazinaci ba.
Shiru kawai ya yi amma bashida walwala. Misalin biyar ya shirya ya nufi Kabala, bayan ya dawo raka abokanshi kai tsaye gidan Affa ya yi da shirin ko ta ƙwana.
Daidai wannan lokacin Ruƙayya ta dawo daga gidan Yaya Suwaiba ita da A'isha,tazo tana cewa Umma ni ƴar gata ce kinga itama Yaya Suwaiba ta cika ni da kuɗi." Umma ta ce "To Allah ya yi muku albarka dukkan ku." Ruƙayya ta ce Ummanmu "Yaya Murja ta sai min waya, Yaya Fati ta sai min layi ta cika shi da kuɗi, Yaya Murja ta yi min shopping Yaya Amina kuɗi kai na gode Allah." Umma ta ce shine abin godiya. Ruƙayya ta ce bari nasa number Nura inji ko yana hanya koma ya zo, Umma ta ce tafiyar dare zakuyi kenan dai? Ruƙayya ta ce tafi ƙwanciyar hankali hanyar Legos ɗin Allah dai ya kaimu lafiya." Umma ta ce Amin.
Tana kira Nuraddeen ya ce saukar su kenan, yake mata tsiyar waya da cewa tazo ta matsa samari sun fito da waya." Ta ce Wayyo Nuri,wa ya gaya maka? Ba ni da saurayi, ya yi dariya Ruƙayya kenan, yanzu ya ya zan kawo kaina unguwarku? Ta ce shiga motar kasuwa ce market in kun iso sai ka hau ta Kabala kuna zuwa bus stop kai min waya sai nazo na ɗauke ka, ya ce bari na hau Kabala ina zan ce,ka ce Kabala in kun zo sai ku miƙo daga Bus stop kuyo ƙasa ka kirani zan fito na jiraka.
Haka kuwa aka yi,nan bakin lungunsu ta jirashi,yana isowa suka tari juna cikin farin ciki da murna har cikin gida suka shiga ya gaida iyayen ta cikin girmamawa. Bai taɓa zaton Ruƙayya ƴar talakawa ba ce sai dai ya jinjina ma iyayenta dattawa ne masu ƙoƙari sun birgeshi yanda suka tsaya ma ƴarsu tayi karatu. Abinci ta gabatar mishi sannan ta shiga shiri.
Suna sallama da su Umma da Affa,aka yi sallama da Affa a waje. Sun fito dan kada su ƙara dare cak numfashinta yaso ya ɗauke,da suka yi ido huɗu da Dady yana tsugunne gaban Affa. A take ta ɗaure fuska sam bata son ganin shi,tana ganin shi mugu ne bashi da adalci. Tunda ganin shi babu abin da yake ƙara mata sai tashin hankali, suka jero da Nuraddeen, shi ko numfashinsa ɗaukewa ya yi ya kasa cigaba da gaishe da Affan, ya shiga ruɗani,ya ya ma haka Ruƙayya da wani?.
Kusa da Affa suka russuna sai mun dawo Affa." Ya ce Allah ya kiyaye hanya,kasa motsi Dady ya yi har suka wuce su. Affa ya ce "Ruƙayya ga Yusufa ko baki gane shi bane?" Ba tare da ta dubeshi ba tace"Oh ban ganshi ba ina gajiya?" Ta wuce cikin ko in kula.
Ba Dady ba hatta Affa yasha mamakin ta,zama Dady ya yi tare da saka kanshi cikin gwiwoyinshi sai da suka kai ƙarshen lungunsu sannan ta juyo ta dubeshi. Tsaki tayi sannan ta kauda kai jikinta babu ƙarfi jakar hannunta ta faɗi Nuri ya dubeta ya ya ne Ruƙayya idanunta ne suka ciko da hawaye cikin rawar murya ta ce bakomai, ya ɗaukar mata jakar ya ce yi sauri gurin da zamu hau motar Legos da nisa sosai.
Kasa magana ya yi har sai da Dakta ya tafi bacci mai nauyi ya ɗauki Dady, Dad ya dubi Momy ya ce "Hajiya yanzun ya ya zamuyi ne? Momy ta ce "Uhm kai dai bari, haka za'a cigaba da biki kawai,in matar ta zo in tana kula dashi ƙila ya mance da Ruƙayya." Dad ya ce "In ma za'a bashi ba sai ya aura ya haɗa su ba."
Ta ce haka ne abin nan ya isheni. Ya ce bari in angama wannan zan je Katsina filin nan da aka maida gurin sha'anin biki ana bada haya to nan ne gonar tasu mahaifin Ruƙayya zan bashi in huta nima bada zalunci nayi ba duk laifin Jega ne shi ya shirya komai, to na haƙura nima cutata ya yi tunda kinga na daɗe da sallamar shi macuci ne na ƙarshe." Momy ta ce "Hakan ya yi sai mu nema masa auran Ruƙayya."
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/2, 07:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 3
Dad ya ce "Ni dai koda ba zan nema mai auran ta ba in basu in huta."
*** *** *** ***
An É—auro aure amma hankalin amarya a tashe don haka ba'a samu yin biki a can Abuja ba aka tarkato aka taho da amarya.
Dady ya farka bacci, Zainab ya gani zaune gefen shi tayi ado sosai sai dai hankalinta a tashe yake. Ya yi ƙoƙari ya yunƙura ya tashi zaune ya ce "Zee yaushe ki ka zo?" Ta ce "Tare muka zo dasu Dad da Abokanka,tasa hannu a wuyansa, jikinka babu zafi ka ji sauƙi." Ya ce "Alhamdulillahi." ta ce "To zaka yi wanka ne?" Ya ce da ruwa mai zafi. Ya fito wankan su Momy suka shigo duba shi abokanshi ma dana can Abuja dana nan duk sun cika falon shima yana jin su sai dai jikin babu ƙarfi sannan zuciyarshi na gurin Pretty da son ganin ta.
***. *** ***
Affa ya dubi Umma ya ce "Af har zan fita na manta ban sanar dake ba jiya yaron nan Yusufa da dare ya shigo yake sanar dani É—aurin auren shi,kin ji ikon Allah duk shekarun nan baiyi auran ba."
Umma ta ce "Oh ikon Allah, to Allah ya sanya alkhairi." Affa ya ce "kuma kin ji ashe duk saƙon nan shi ne yake aiko mana ina ta neman mai kawowa ashe shi ne." Umma ta ce aini zuciyata ta raya shi ne domin naga buhun shinkafar nan mai tumatur kuma ita ce yake kawo mana da, sanda yake neman Ruƙayya." Affa ya ce "ai koda aka fasa auran yaso ya cigaba da kawowa na hana tunda suka zo nan da uwarshi nace kada ya ƙara kawo mana komai mungode." Umma ta ce "Allah ya basu zaman lafiya," Affa ya ce Amin.
Duk zancen nan da suke yi a kunnen Ruƙayya abin duniya ya ishe ta sam ita fa da tasan haka zata fuskanta a zuwannan da bata zo ba, duk da tana shirin wai cire son Dady daga ranta, sai dai abin da yake ɓata mata rai shine har yanzu zuciyarta Dady kawai take ma dariya,yaya zata yi ne domin a ganinta shi Dady bai yi mata adalci ba har manta da ita yayi ya ganta ya yi kamar bai ganta ba, ƙarshen wulaƙanci shi ne ya tako har gida ya shaidawa Affanta auran shi ƙila ma da ita yaso ya shaidawa taƙi fitowa daya kira ta.
*** *** ***
Daran ranar Dady ya raka abokanshi na Abuja masaukin baƙinsu dake nan cikin layin su. Yayin da ƴan'uwan amarya suke can sashin su Momy.
Ya dawo ya zauna a falo tunanin shi ɗaya yana son zuwa gurin Pretty,ƙwarai ya so yaje yau da dare sai dai abokai ne ba zasu barshi ya fita shi ɗaya ba.
Sannan bai san yaya zasuyi da Affa ba ita kanta Pretty bai san nufin ta akan shi ba,ga zaton shi Zainab can gurin su Momy zata ƙwana, amma sai ji ya yi an dafashi ta ce "Tunanin me kake yi My dear?" Ya dubeta "Zee me yasa ba zaki je ki ƙwanta ba?" Ta ce Momy ta ce nazo saboda baka jin daɗi don kada ka ƙwana kai ɗaya,na shigo kuma sai na same ka kana tunani." A ranshi ya ce "Kada ki yarda ki san tunanin da zuciyata take yi." Ya miƙe "To muje." Bayi ta shiga tayo wanka, ta shafa turaruka tare da wasu sirrika da Hajiyarta ta bata,dan ma abin bai zo musu yarda suke so ba. Sun so kece raini a bikin musamman ranar dinner aƙwai shiri na musamman da Hajiyar taso tai mata, sai dai Kash! Rashin lafiyar Dady hakan bai samu ba.
Yana ƙwance rigingine ta zo ta ƙwanta kusa dashi tana kiran sunanshi a hankali yayin da ƙamshin daddaɗan turare ke tashi a jikinta.
Cikin natsuwa da hikima ta dinga janshi da hira tare da nuna masa irin so da ƙaunar da take yi masa domin ya samu ƙwanciyar hankali, dangane da fahimta da ta fara yi yana cikin damuwa.
Lamo ya ƙwanta tana jikinshi tana sharar bacci. Shi kam yana tunanin Pretty gani yake kamar bai mata adalci ba, yana ƙwance da wata ba Pretty ba. Yasan yau inda Pretty ce daran nan sai Allah kawai, amma yanda Zee ta nuna zalamar ta ta bashi haushi ace mace ba kara ba kunya shi bai son haka, to amma ba yanda zaya yi tunda matarsa ce sannan shima mabuƙaci ne.
Washegari da safe an aiko musu da break fast daga cikin gida. Shi kam bai ma tashi ba tunda ya yi sallah sai kusan sha É—aya. Ta zauna tana salo a gabanshi ya rasa sam bata birgeshi amma ya ya zaya yi wani sashe na zuciyarshi ya tuna mishi da wani abu da ya faru tsakanin Hussain da Madam É—in shi, ya ce mishi first night É—in su tasha wahala don sai da Dakta ya duba ta,da ya ce mishi nauyi kasa kaji mata ciwo? Sai ya ce kasan ita mace in virgin ce dole tasha wuya." Ya dubi Zainab sai yaji ranshi ya sosu, kenan dole wani ya santa, shi sam dai baiyi sa'a ba, domin bai kasance mazinaci ba.
Shiru kawai ya yi amma bashida walwala. Misalin biyar ya shirya ya nufi Kabala, bayan ya dawo raka abokanshi kai tsaye gidan Affa ya yi da shirin ko ta ƙwana.
Daidai wannan lokacin Ruƙayya ta dawo daga gidan Yaya Suwaiba ita da A'isha,tazo tana cewa Umma ni ƴar gata ce kinga itama Yaya Suwaiba ta cika ni da kuɗi." Umma ta ce "To Allah ya yi muku albarka dukkan ku." Ruƙayya ta ce Ummanmu "Yaya Murja ta sai min waya, Yaya Fati ta sai min layi ta cika shi da kuɗi, Yaya Murja ta yi min shopping Yaya Amina kuɗi kai na gode Allah." Umma ta ce shine abin godiya. Ruƙayya ta ce bari nasa number Nura inji ko yana hanya koma ya zo, Umma ta ce tafiyar dare zakuyi kenan dai? Ruƙayya ta ce tafi ƙwanciyar hankali hanyar Legos ɗin Allah dai ya kaimu lafiya." Umma ta ce Amin.
Tana kira Nuraddeen ya ce saukar su kenan, yake mata tsiyar waya da cewa tazo ta matsa samari sun fito da waya." Ta ce Wayyo Nuri,wa ya gaya maka? Ba ni da saurayi, ya yi dariya Ruƙayya kenan, yanzu ya ya zan kawo kaina unguwarku? Ta ce shiga motar kasuwa ce market in kun iso sai ka hau ta Kabala kuna zuwa bus stop kai min waya sai nazo na ɗauke ka, ya ce bari na hau Kabala ina zan ce,ka ce Kabala in kun zo sai ku miƙo daga Bus stop kuyo ƙasa ka kirani zan fito na jiraka.
Haka kuwa aka yi,nan bakin lungunsu ta jirashi,yana isowa suka tari juna cikin farin ciki da murna har cikin gida suka shiga ya gaida iyayen ta cikin girmamawa. Bai taɓa zaton Ruƙayya ƴar talakawa ba ce sai dai ya jinjina ma iyayenta dattawa ne masu ƙoƙari sun birgeshi yanda suka tsaya ma ƴarsu tayi karatu. Abinci ta gabatar mishi sannan ta shiga shiri.
Suna sallama da su Umma da Affa,aka yi sallama da Affa a waje. Sun fito dan kada su ƙara dare cak numfashinta yaso ya ɗauke,da suka yi ido huɗu da Dady yana tsugunne gaban Affa. A take ta ɗaure fuska sam bata son ganin shi,tana ganin shi mugu ne bashi da adalci. Tunda ganin shi babu abin da yake ƙara mata sai tashin hankali, suka jero da Nuraddeen, shi ko numfashinsa ɗaukewa ya yi ya kasa cigaba da gaishe da Affan, ya shiga ruɗani,ya ya ma haka Ruƙayya da wani?.
Kusa da Affa suka russuna sai mun dawo Affa." Ya ce Allah ya kiyaye hanya,kasa motsi Dady ya yi har suka wuce su. Affa ya ce "Ruƙayya ga Yusufa ko baki gane shi bane?" Ba tare da ta dubeshi ba tace"Oh ban ganshi ba ina gajiya?" Ta wuce cikin ko in kula.
Ba Dady ba hatta Affa yasha mamakin ta,zama Dady ya yi tare da saka kanshi cikin gwiwoyinshi sai da suka kai ƙarshen lungunsu sannan ta juyo ta dubeshi. Tsaki tayi sannan ta kauda kai jikinta babu ƙarfi jakar hannunta ta faɗi Nuri ya dubeta ya ya ne Ruƙayya idanunta ne suka ciko da hawaye cikin rawar murya ta ce bakomai, ya ɗaukar mata jakar ya ce yi sauri gurin da zamu hau motar Legos da nisa sosai.