← Book details Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 21

Sashe 21

Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Shi kam jami'an tsaro ya kira a waya sannan ya shiga ɗakin wani abin mamaki tana jansu tana duka suna komawa suna mannewa har sanda jami'an suka zo abin da yake faruwa kenan Hajiyarta sai kuka take yi sai da mutane suka cika ɗakin tankam sannan fa sun cika lokacin su da dukan da ƴan sanda suka dinga musu, Dady ya wuce ya ɗauko jakarshi da yazo nema a gefen gado,ƴan sanda suka tasa su suna kuka, Hajiya tana ta ba Dady haƙuri, ya ce ai haƙuri yana gurinku ko kina ganin zan kuma zama da annoba? Ai Zainab annoba ce kema ki fita kafin nasa a kama ki.

Ya zauna jagwaf akan kujerar ofis ɗin shi ya kulle kanshi ya yi kuka har ya gaji, Sunday yaronshi daya ba amana, Zainab matarshi wane irin ƙwazo ne baya dashi? Amma har sai ta nemi Sunday? Lallai mutum ba abin yarda bane.

Allah sarki Pretty matar da kullum yake zargin ta da yiwa Zainab asiri ya dubi hannunshi yanda ran nan ya wawwanka ma fuskarta mari,ya miƙe ya ji ma sam tsani wannan gidan don haka gidan hutawarshi ya nufa dake area 2 ya shiga ya ƙwanta bai jima ba bacci ya yi gaba dashi ya jima a ƙwance.

Sanda ya farka sai yana jin shi wani irin tamkar an sauke mishi wasu kaya masu shegen nauyi. Yana zaune komai ya dinga dawo mishi sabo yana ta nazarin abubuwa ya É—auko wayoyinshi missed calls barkatai cikin kowacce waya,na sirikinshi sun fi yawa,yana ganin girman mahaifin Zainab shi ne ma dalilin da yasa baya kallon wasu abubuwan da Zainab É—in take mishi a zaman su.

Don haka sai ya soma neman layin shi,sun gaisa inda Dady ya bashi haƙurin rashin ɗaukar kiranshi yana bacci ne ya ce ba komai dama shima ya kira shi ne dan ya bashi haƙuri game da abubuwan da suka yi ta faruwa nan Dady ya koro mishi komai game da irin zaman nasu.

Satar da ta dinga yi mishi kai har yanda ya ɗauki watanni baya iya saduwa da ita duk saida ya zayyane mishi a ƙarshe ya ce ya sake ta saki uku. Sam minista bai damu da hakan ba don shima yau ya gaji yana zuwa gidan zai sahale wa Hajiya sai dai albarkacin ƴaƴanta ta zauna a gidan,shi kam dama yana neman wata ƙanwar abokinshi,bazawara ce kuma yana da tabbacin yarinya ce mai hankali sai ya koma sabon gidan daya jima yana ƙerawa gidan da Hajiya ta ci burin zama,sai dai yasan yanzu kash sai haƙuri.

Garin Abuja ya yi mishi zafi ya tsani gidan nashi, don haka a wannan yammacin ya kira wayar Sabi'u ya shirya musu zuwa Kaduna, Sabi'u ya ce Oga zamuyi dare a hanya. Ya ce Allah zai kare,koda ya shiga gidan É—akinshi ya wuce kai tsaye be koyi wanka ba ya canza kaya ya É—ibi kuÉ—aÉ—e ya fita.

Sun isa Kaduna ana sallar isha'i, don haka suna tsayawa sai masallaci, Ruƙayya tana kitchen riƙe da kula ta fito zataje ɗakin Momy, sai kawai sukayi kiciɓis da Dady ta yi sororo tana dubanshi ya tako zuwa gabanta, ganinshi tayi ya rame,ya kamo hannunta, Pretty ina Momy? Ta kalli sashen Dad ya ce tana saman Dad ne? Ta kaɗa a hankali ta ce Eh,ya tsurawa hannuwanta ido Pretty hannuwanki sun kunbura ne ko? Nan ma kai ta kaɗa ya ce ki zauna bari naga su Momy ya zaunar da ita tamkar mai ɗora ƙwai kan kanfa. Ya yi sama da sauri,ita kam kullum tana mamakin Dady tamkar mai aljanu.

Ta miƙe gara ma taje ta gyara musu gefen su don wancan Zuwan da ya yi irin masifar da ya dinga mata,wai shi baya son ƙazanta,tasan zai zo amma bata sa an gyara ba,da tace mishi wazan sa? Sai ya ce mata Oho miki, to Momy ƴan aikin ta bana ƙwana ba ne suna gamawa suke tafiya, girki tafi son tayi da kanta ita ba yara ba bare ta ce matsalar yara ko zasu ɓata gidan da dai sauransu.

Haka ta zage tana ta faman gyara, da É—akinshi ta soma duk da babu wani datti dama, sannan ta koma É—akinta zuwa falo.

Shi kam wannan lokacin yana can yana zayyane ma su Momy abubuwan da suka faru. Sun sha mamaki Momy ta ce ai dama rashin bincike a aure matsala ne, Dad ya ce aini na nemi sani da mahaifinta naji an yabe shi, Momy ta ce mahaifinta zama yake a gida? Dady ya ce shima yau ɗin nan ya ce zaije ya rabu da uwar shima ya gaji, Momy ta ce Allah sarki Ruƙayya nifa nasan zuwan nan ba lafiya ba, Dady ya ce Ni kaina Momy inna tuna marin da nayi mata duk sai naji kunya. Yanzun sai ka bata haƙuri cewar Dad, ya ce dole ma, duk tare suka sauko sun zauna falo suka ce ya kira ta,ya duba bata ɗakin Momy bata toilet bata kitchen yazo yana huci ya ce ban ganta ba, Momy ta ce duba sasanku,nan ya sameta tana ta goge goge ta gama shara da alama duk ta gaji.

Da gudu ya isa gurinta ya rungumo ta "haba Pretty, haba Pretty ya ya zaki zo kina aiki haka bayan kinsan cewa baki da ishasshiyar lafiya, daga yau bana son kina komai kin ji ko? Kallonshi kawai take.

Su Momy sukai mata bayanin komai tare da bata haƙuri akan duk abubuwan da Dady ya yi mata, shima Dady ya ƙara neman afuwa,ta ce ita dama bata riƙe shi a ranta ba,koda suka ci abinci suka nufi sashensu ta kasa sakin jiki dashi, ya ce haba Pretty na ni ne fa dadynki mai son nan naki kin tuna? Ki share komai ki tuno da farkon aurenmu, yanzun na zama naki ke ke ɗaya ko? Ya ɗaga mata gira.

Ta dubeshi da murmushi shikenan Dady komai ya wuce na yafe maka.

"Yauwa My Pretty, nagode."

Ya ƙara matsowa daf da ita yana yi mata wani irin kallo mai tattare da tsananin so da ƙauna. Itama kallon nashi take yi cike da wani irin yanayi mai cike da tsantsar so.

"Come to me My Pretty,I want as some thing please come." Murya ƙasa-ƙasa yake faɗar maganar,a hankali tabi umarninsa kafin wani lokaci suka shiga farantawa junansu rai, sai gashi sun dawo kamar yau ne daren farkon su na amarci.

*** *** ***

Haka suka cigaba da zaman su shi da Pretty cikin ƙwanciyar hankali da farantawa juna, Allah ya basu ƴaƴa biyu mace da namiji ƙyawawa dasu.

Hankalin kowa ya ƙwanta, kowa sai farin ciki yake, yanzu Dady bashi da wata sauran damuwa. Ruƙayya ta zage damtse kullum faranta ran Dady take. Wannan shi ne abin da yasa iyayensu suka cigaba da yi musu addu'a tare da fatan alkhairi cikin alfahari da jin daɗin zaman aurensu.

Alhamdulillahi

Ƙarshen littafin FIN ƘARFI

Taku Halima Abdullahi K Mashi.
Chapter 21 · 0% Book details