← Book details Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 21

Sashe 18

Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta ce nafi sonka fiye da yanda kake sona, ya ce ban yarda ba Pretty, ta ce me zan maka ka yarda? Ya ce tashi... sallamar Zainab ce ta dakatar dasu dan tuni take kallonsu amma basu san ta shigo ba. Dady ya ce "har kun dawo?" Ta ce Umm ta wuce É—akinta.

Ruƙayya ta tashi tana mata sannu da zuwa kyar ta amsa ta shige ɗaki.

Misalin sha ɗaya Ruƙayya tana ɗakinta bacci ga zazzaɓi wanda ya zamar mata ƙa'ida duk ranar Allah zuwa yamma sai ya sauka taƙi sanar da Dady ne dan tasan zai ce suje asibiti, ita ko bata son zuwa,tasan gajiya ce bata gama sakinta ba.

Zainab ta leƙa kicin taga Sunday yana ta aiki ta koma ɗaki ta haɗa asirin da aka bata,ta cire kaya ta maka a jikinta maimakon shafawa ya ko gangaro ya shiga gurin da ba'a so nan ta tuna da gudu ta shige toilet ta shiga yin tsarki sai dai kash ya riga ya shiga,ta fito da yaƙinin bazaiyi komai ba, tunda ta wanke wayar kicin ta kira Sunday ya ɗauka ya ce Yes Madam za'a kawo wani abu ne? Ta ce kawo min Hollandia mai sanyi ya ce Ok ya ɗauko yana mamakin me yasa yau Madam zata sha Hollandia ita da bata son shi.

Ya tura ƙofa ya shiga bai ganta ba don haka ya nufi madubin ta dan ya aje mata. Ya juyo zai fito suka yi karo, tsoro ya kama shi a yanayin da ya ganta,da sauri ya juya tare da rufe idon shi bakinshi yana rawa ya ce sorry Madam.......katse shi tayi ta hanyar ɗora hannuwanta a kafaɗunshi, fargaba ya cika shi jikinshi yana ta ɓari tsam ta rungume shi tuni shirinta ya soma ratsa shi ya fara miƙa mazantakarshi ta tashi dama ya soma maida martanin abin da take mishi sun lula cikin shagala da ta ɗauke su tsawon awa biyar.

Bayan dawowa haiyacin su sai tsoro ya kama Sunday ya yin da Zainab ta soma kukan ƙarya tana faɗin daga tana mishi wasa shine zai yi mata haka? To zata sanar da Oga nan ya zube yana bata haƙuri yana kuka,ta ce saka kayan ka duk abinda na ce kayi zakayi? Ya ce zaiyi ko menene ta ciro garin magani ta ce wannan cikin Hollandia zaka saka ka tabbatar Oganka da wancan shegiyar matan sun ci, ya ce to ya saka shi a aljihu.

Ya ko saka kuma yanata gadin shi don kada wani cikin su yasha shi kaɗai sai da dare sannan suka zauna dinner Ruƙayya tasha gayu cikin super fara, yayin da Zainab aka sa farin les,ta saki fuska har su Ruƙayya suna mamaki a zukatan su.

Sunday ya yi ta jera abinci a gabansu Zainab ce da maigidan don haka ta soma zuba mishi.

Sun fara cin abinci kafin daga baya ya jawo Hollandia ya yi sanyi yanda Dady yake buƙata don haka Zainab ta zuba mishi ya soma ɗaɗɗaka ya ce Pretty ga mai sanyi fa, ta ce kasan duk yanda nake son Hollandia ƴan ƙwanakin nan ko ƙamshin ta bana son ji, ya ce kin sha da yawa ne ya hau miki kai ko? Ta ce ƙila haka ne, ya ce ni kam koda zan sha goma a rana ba zai ginsheni ba.

Cikin Zainab ya kaɗa kar dai matar nan taƙi sha ta ƙaƙaro murmushi Ruƙayya ke yau bazaki sha bane? Dubi yanda raɓa ke zuba jikin kofin da My dear yasha Ruƙayya ta duba sannan ta ce yau dai banjin sha. Tamkar Zainab ta fasa ihu don haushi, ta rasa me ke mata daɗi ji take kamar tai ma Ruƙayya ɗura,har ma Ruƙayya tasha jinin jikinta shi ko gogan yama daina cin abincin sai faman banƙarar Hollandia yake yi jinshi yake tamkar yana yawo ne a sama dan daɗi. Ruƙayya ta fara tashi tai musu saida safe kafin Zainab ma ta tashi ta nufi ɗakin ta ta kira Hajiyarta ta shaida mata Ruƙayya fa bata sha ba, faɗa Hajiya ta soma tare da zagin Zainab ɗin.

*** *** ***

Bacci mai nauyi ya ɗauki Dady bisa gadonshi ko addu'a baiyi ba daƙyar ma yayi wanka wata sabuwa Zainab tana fitowa dan zuwa ɗakin maigidan sai taga Sunday tsaye a falo,suna haɗa ido saita birkice ta kirashi ɗakinta shima abin da ya hana shi bacci kenan, suka lula cikin masha'a tsawon lokaci mai yawa sannan suka tashi cikin firgici,ya ƙwashi kayanshi ya yi waje yayin ta kama kuka menene haka daga sau ɗaya.

Kiran sallah ya farkar da Dady bayan yayi sallah ya rasa me ya hana Zainab zuwa É—akinsa? Ya san dai ko faÉ—a sukayi zata zo bare ba faÉ—a, Pretty ce gimbiya bata zuwa É—akinshi sai dai shi ya bita.

Yana wanka zuciyarshi zugi take yi tana zafi ya fito ya shirya kan dinnig babu komai sannan mata biyun babu ko ɗaya takaici ya kama shi ya ce Zainab! Ke Zainab, kai Sunday" a firgice suka fito a zatonsu asirin su ya tonu kowa yana ƙyarma ya fito, yanda jikinsu ke rawa sai suka bashi mamaki, ya ce har yanzu babu komai na break fast harna shirya zan fita,kema mara amfani bazaki matsa mishi ya shirya ba? Ya shiga faɗan rashin dalili, suka yi ajiyar zuciya ta soma cewa, My dear kayi hakuri bari inje in duba da kaina tsaki ya yi ya nufi waje.

Wasa-wasa Dady ya canza ya zama masifaffe Ruƙayya ma tsoron shi take,tun daga ranar da yayi ma Zainab duka akan wai ta fita bata sanar dashi ba, bayan yasan tana fitar bai ɗauki mataki ba sai yanzu, yau ita keda Dady ta saba shi ke zuwa ɗakinta don haka koda aka gama cin abinci sai tayi ɗaki gurin cin abincin ma a ɗari-ɗari akeyin shi sai faman harare-harare yake yana jiran ganin mistake Allah dai yasa aka gama qalau. Ruƙayya na tashi shima ya tashi ya yi ɗakinshi. Zainab tayi kitchen gurin Sunday ta ce ya fa shigo tana jiranshi ya ce to.

A ran Dady faɗi yake yau zaiyi maganin Pretty wato ita tana taƙama yana sonta shi ne haƙƙinshi ma sai ya bi ita tafi ƙarfin zuwa ɗakinshi to yau kam bazai je ba,har gurin biyu taji shiru kamar ta share sai kuma da ta ce bari taje tunda yanzun ya zama a lallaɓa. Sai dai tana fitowa Sunday ta gani zai shiga ɗakin Zainab daga shi sai gajeren wando,bai ganta ba don haka ya shige.

Kamar ta tsaya sai kuma ta wuce. A rigingine ta same shi fuskarshi tana kallon silin ta zauna gefen gadon bayan ta rufe ƙofar ya tashi yana hararar ta ya ce waton Ni Ban isa ba ko? Ta ce me ya faru ne? Ya soma ɗaga murya ƴar rainin wayo dole ki ce min me ya faru? Tunda ni kinga ina son ki sai ki ka maidani sakarai sai dai in ina buƙatar ki ni na biki ɗakinki ko? Ta ce to yi haƙuri bebyna sam faɗa baya yi maka ƙyau ta ƙarasa magana tana tura bakinta cikin nashi. Ya yi ajiyar zuciya sannan ya shiga neman lada. Irin Haka Pretty take yi tana lallaɓa shi in abin yazo kanta,ga ciwon da ko'ina na jikinta yake mata zazzaɓin rana duk ta faɗa tamkar ba ita ba.

Shi da kanshi ya tsare ta wai sai ta faɗi mishi dalilin ramarta, ta ce ko faɗan ka Dady shi kaɗai zai ramar dani tunda da ba haka kake ba, ya ce tunda ga kare ba dole ki ce min mafaɗaci ba,kina taƙama ina sonki shiyasa kowacce magana tazo bakin ki sai ki yaɓa min,ta soma hawaye tana faɗin To kayi haƙuri shikenan, ya ce ai dole kiyi kuka tunda Allah ya hore miki idon kuka da bada haƙuri,tama rasa me zata ce ya dinga shiga yana fita sannan ya yi tsaki ya wuce.

Shiru tayi tana tunanin irin wannan hali da Dady ya canza, inda ma abin ya ɗan mata sauƙi ba ita ɗaya yake mawa ba.

Wani sabon lamarin kuma duk sanda Dady ya nemi Zainab dan zuwa garin majidaɗi sai ya zama ba namiji ba,ya kasa aiwatar da komai sai dai ya haƙura bugu da ƙari kullum da dare sai taga Bokan nan cikin mafarkin ta yazo yana amfana da ita ga wani ɗoyi da yake yi ban da liƙewa juna da suke yi ita da Sunday da rana da dare in ba ita keda miji ba.

Abun ya soma damun Dady ya tsare Zainab yana tambayarta me yasa baya amfani a gurinta amma gurin Ruƙayya lafiyarshi qalau? Ta ce itama bata sani ba wai amma da Hajiya ta nemo magani wai ance Ruƙayya ce tayi mata asiri ya yi shiru yana son yayi nazari amma ya kasa natsuwa zuciyarshi tana ta faman tafarfasa tana shaida mishi gaske ne, in ba haka ba yaya za'a ce gurinta kaɗai yake namiji gurin kishiyarta shima mace ne? Wato duk son da yake nuna ma Pretty bata gani ko? Ya tashi fuu ya fita.

Tana ƙwance tayo amai ta gaji ga zazzaɓi, Dady ya shigo a fusace ta ɗago tana dubanshi, tsoro ne ya kamata ganin bata taɓa ganinshi cikin irin wannan fushin ba duk da cewa yana saurin fushi ƙwanan nan amma na yau dabanne. Tsura mata ido ya yi sannan ya girgiza kai,kin bani mamaki Ruƙayya, da sauri ta dube shi tana zaton tun ranar farko da suka haɗu ta ce mishi sunanta Ruƙayya ya maimaita faɗin sunan bai ƙara kiran Ruƙayya ba sai dai Pretty don haka sai taji wani sabon tsoro ya shige ta,ta zuba mishi ido ya ce ashe haka halinki yake? Ashe wa'azin ƙarya kike min ke munafuka ce? Cikin rawar murya ta ce me nayi Dady? Ya ce da Allah ni rufe min baki,wai duk son da nike nuna miki,be ishe ki ba sai kin shiga bokaye da malamai shi ne kika je kika yi ma Zainab asiri kada inyi sunnah da ita sai dai ke ko?
Chapter 18 · 0% Book details