← Book details Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 21

Sashe 13

Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shi kam Dady har dare yana can sai dai ya yi sallah ya dawo, shi ya nemo musu abin da zasu ci,ita kam gimbiyar ƙin ci tayi yana gurinta har sha ɗaya tamkar kada ya tafi duk da basa hira, haka ya nufi masaukin shi.

Ta rungume tana tunanin shi har ga Allah ta ɗan huce,sai dai kishin ne yana damunta ta so ta auri Dadynta ita kaɗai ta kula dashi ta ririta shi ta maidashi abin sha'awa cikin abokanshi amma yanzun su biyu ƙila tana tufka waccen ta zama tana warwarewa.

Jirgin ƙarfe taƙwai zai bi dan haka ya yi sammako saboda suyi sallama,yau ya samu abokan ƙwananta dama su uku ne,ɗayar tayi mishi sannu da zuwa, duk suna sanye da kayan N.Y.S.C Pretty ɗin shi tana sanya takalmi ya shigo, sauran suka gaidashi suka basu guri itama ta ce an tashi lafiya? Ya ce yanda ki ka ƙwana nima haka kuma kin tashi da shirin zuwa aiki nima daga nan sai ofis." Ya ɗan ƙara bata baki duk da bata tanka ba yaji daɗin yanda tayi mishi addu'ar sauka lafiya. Bai koma gida ba kai tsaye ya wuce ofis, biyar saura ya shigo gida .

Zainab bata nan har ya yi wanka, Sunday ya gabatar mishi da abinci ga kuma Hollandia ya gama ya koma falo yana neman layin Pretty ya saba dan kullum sai ta tsinke sau biyu wata ran ma sau uku sannan ta É—auka.

Ya ce Pretty ko ki kira kiji yanda na sauka ko?" A ranta ta ce da kasan yanda na damu in san yanda ka je gida da baka ɓata bakin ka ba. Amma a wayar sai ta ce lafiya ai ita kesa aji shiru. Ya ce to ke yakike? Ta ɗan ja aji sannan ta ce lafiya lau, yanda take amsa mishi waya sai ya rasa me zai ce mata.

Suka yi shiru na É—an lokaci ya ce "ina labari?" Ta ce Æ´ar jarida ce ni zaka tambaye ni labari,ya ce to bani na kotu, ta ce ai ba can naje ba. Pretty me Momy ta ce miki jiya? Sai kaji,ka je ka tambaye ta."

Zainab ta shigo sanye da riga da siket sun ɗameta, ƙaramin gyale a kafaɗa hannunta riƙe da jaka da key ɗin mota ta zauna tana faɗin ka dawo ne ashe?" Bai tanka ta ba ya cigaba da wayarshi.

To Pretty tsakanina da ke ai akwai sirri, ta ce to ba san jin kake yi ba, ya ce to ki ɗanyi kissing ɗina I miss You,ta ce "bata nan? Tai maka mana." Zainab taja tsaki duk da bata jin me Ruƙayya ke faɗi tasan maganganun soyayya ne. Ya yi kissing ɗin wayar Ruƙayya ya kashe. Dariya ya saka ganin ya soma ciyo kanta.

Ya tamke fuska sannan ya dubi Zainab

"Ina kika je?" Ta ce a'a gida mana Hajiyata keson gani na." Ya ce shine bazaki nemi izni ba" ta ce tun jiya kaki ɗaga wayata don kana tsoron ƴar gold kada tayi fushi, ya ce shine kika fita ko? To bazan ɗauka ba, ta ce "duk inda zan je sai na gaya maka sai kace auren gargajiya?" Ya taso da faɗa kamar zai bugeta, ya ce ke jahilar ina ce? Wato har ma aƙwai auren gargajiya, to ban san shi ba,in Hajiyar ta koya miki to bazan ɗauka ba,be carefull zanyi maganin ki." Ya fita ta ce borin kunya dan yaga yaje ya ƙwana da waccan ƴar iskar,kai ma sai nayi maganin ka."

*** *** ***

Ƙwanci tashi su Ruƙayya sun gama sabis farin ciki ba wanda ya kai Dady tun ranar da ta dawo baya ma ƙasar yana Italy. Amma ya soma maganar biki,yana dirowa ya yi wanka sai Kabala.

Affa ya samu dan yasan in takan ƴar rigimar tashi ya bi sai ta dinga kawo mai uzuri,sun yanke sati biyu sannan ya sameta da maganar, ta ce ita wata biyu sai ta huta in kuma ya matsa mata sai ta fasa tarewar gaba ɗaya,ai dama dole akai mata, ya bata haƙuri tare da cewa ya yarda sai nan da wata biyun.

Ashe anyi rashin sa'a Umma ta ji,yana fitowa tsakar gida ta fito daga ɗaki tace kaje ka cigaba da shiri Yusuf sati biyun da kuka tsaida ba ƙari.

Bayan tafiyarshi ta yi ma Ruƙayya ta tas tare da cewa sai ta haɗa ta da Affanta nan ta shiga bata haƙuri tare da cewa ta yarda.

*** *** ***

Shiri ba kama hannun yaro duk ɓangare biyun, Ruƙayya ta taka har Katsina, Zaria ta gayyato ƙawayenta na secondary su Amira,su Munira da Armaya'u ba zama ita sati biyu ne tsakanin ta da Ruƙayya za'ayi nata su Yaya Murja da Fati ana ta shirin yanda bikin zai kasance ya yin da su Yaya Sadiya manyan yayye ana ta shirya Auta. Kowa faɗi yake tana da kishiya Mom ɗin su M Bash tazo ta ɗauki amarya dan kimtsi na musamman.

Ƙwananta biyu tai ƙyau ta gyaru har ita kanta tana jin sha'awar mijinta,tana ba su M Bash labari suka yi ta mata dariya ta ce ni tsoro nake kar yaje ya rakwaɓani a banza gara shi yana da wata.

Gefen Dady daga Kaduna har Abuja ya hana jama'a sukuni, gidajenshi ma sun san Pretty zata shigo an gyara ko ina sashenta ya zuba komai.

Zainab ma ya canza mata amma tana ta mita wai amaryar daya gama da ita tun a waje shine yake rawar jiki, ya ce mata ai Pretty ba irin ki bace ke dai dana taya tun a wajen da kin bani, sannan koda ban taya ba ai kin bama wasu. Ranar tayi kuka kuma tayi data sanin yi mishi wannan maganar.

An kawo aƙwatuna har goma sha biyar Affa ya kirashi yana faɗa ya ce kamar hauka? Gashi shine ya yi musu Anko. Bayan su launching, dinner, walima da sauransu.

*** *** ***

Amarya ta tare ɗakinta dake nan Kaduna gidan da Dady ya ƙera cikin gidan su. Bayan an kaita wajen su Momy aka basu amanar ta, aka maida ta ɗakinta kowa ya watse sai ƙawaye,Angwaye sun shigo har da Nuraddeen wanda shima ya rikiɗe ya koma abokin ango maimakon na amarya.

Anyi ɗan wasa da dariya anguna sun bada kuɗin da su Armaya'u suka buƙata na siyen baki, Al-Mustapha yaja Munirar shi suka nufi masaukinshi,ya yin da Ruƙayya ta riƙe Armaya'u wai sai ta ƙwana.

Da ƙyar ta ɓanɓareta ta gudu, Dady yazo yana lallashin ta dama tun da aka soma bikin kuka take yi musamman ranar da iyaye sukai mata huɗubar zaman aure idonta sai da ya kumbura saboda kuka.

Zahiri Ruƙayya tana da tsoro don haka koda Dady ya ce Pretty yo alwala mu gabatar da sallar ma'aurata sai ta ce mishi tana fashin sallah sannan ta ƙi yarda su ƙwanta tare, dole ya bar mata ɗakin,ba dan yaso ba,sai don kada ya ɓallo rikicinta.

Da safe bayan ta sheƙa ƙwalliya da super mai jajayen fulawa ta wuce Dady a falo ta nufi gefen su Momy, shima ya biyo ta yana cewa shine kika wuce ni? Sai ta nuna bata ganshi ba a zahiri kuma ta ganshi waya taji yanayi da Zainab, Momy ta ji daɗin ganinsu haka Dad a can suka yi break sannan suka dawo.

Kusan sati ɗaya kullum Pretty ta ce tana al'ada daya fita sai tayi sallanta, ranar da suka cika ƙwana goma tana ƙwance a falo hannunta riƙe da littafi tana dubawa, Yaya Fati ta bata shi ta ce zai taimaka mata zaman aure.

Dady ya fito sanye da jeans baƙi haka riga, ta kalleshi tana matuƙar son shi sai dai kishi, ya yi mata ƙyau.

Ya zauna kusa da ita ya ce "Pretty har yanzu baki fara sallah ba?" Ta ce lafiya ta qalau haka nake kayana. Ta cigaba da karatun ta, ya ce ko dan baki sona ne shine kike guduna?" Ta ce "zan ƙi yin sallah dan kai ne?" Ya ce ai Allah yana kallon ki fa,bata tanka ba.

Da dare ta fito wanka ta kulle ƙofa sannan ta tada sallah tana tahiyar ƙarshe taji shigowar shi ya yi amfani da wani key ya shigo, gabanta ya yi muguwar faɗuwa ya wuce ya gadonta ƙwanta ya ɗauki littafin da take karantawa mai suna 'TAWA TA SAME NI' yana dubawa tayi sallama kana ta sake tada kabbara. Yana kallon tayi ta sallah tun yana ƙirgawa a ranshi har ya daina. Ya tashi ya shiga toilet shima ya ɗauro alwala daidai tayi sallama ya ce Pretty biyoni jam'i gara in taya ki ko zakiyi saurin gamawa.

Raka'a biyu suka yi har tayi mamakin yanda Dady ya dinga jero musu addu'a ya ce Pretty ta so,taƙi tashi ya kamata ya cire hijabin daga ita sai ɗaurin ƙirji ta ce meye haka Dady bana so fa, ya ce haba Pretty kiji tausayi na ki tuna baya ki tuna dadynki nasha wuya kanki, ta ce "Ni nace ban son ji baka wani sona."

Ya dubeta"ina sonki ina ƙaunarki, nafi son ki da kaina,ki tuna baya." Ta ce kai dai kana son jikinane kawai, ya ce kinyi kuskure,na fara sonki tun baki girma ba,na so ki lokacin da baki mallaki komai na ƴa mace ba, baki da komai na soki badan ƙyaunki ba badan dukiya ba,badan cikar halitta ba, ya ƙara sassauta murya "Nasan da kin soni yanzun ban san me nayi miki ba." Ya ɗaga yatsun shi guda biyu "kalli zoben alƙawarinki yana cin jikina ban cire ba,ban ci amanar ki ba,ki bari mu fahimci juna. Tana shirin magana bakinshi yasa cikin nata ya shiga nuna mata wasu kalolin soyayya masu zafi da gaggawa tana son shi don haka bin shi tayi suka lula. Sai da tafiya ta soma nisa sai ta kasa tsoro ya shige ta ta soma faɗin "yi haƙuri Dady, don Allah ka barni,ba zai iya ba tunda ya jima yana jiran wannan rana, da zafi zafi yake nuna mata soyayyarshi don haka tayi mata nauyi gashi tasha gyara, wannan dalilin yasa tasha wahala ga Ruƙayya da son jiki ko allura bata so amma ganin babu sarki sai Allah nan da nan ta haƙura Dady ya kusan fanshe wuyarshi a kanta. Ta wahalu ƙwarai saboda...........

🖊️🖊️🖊️
[8/21, 06:53] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*

*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

Page 7
Chapter 13 · 0% Book details