Sashe 10
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sallamarshi ce ta katse tunani. Umma ta amsa,ta jiyo shi yana gaisawa da Umma, ya ce Affa ya fita ne? Ta ce eh,ya fita. Ai Ruƙayya tana nan cikin ɗakin ta, ya ce to, tana zaune bakin gado ya shigo message take tura ma Nuraddeen tana sanar dashi abin ya faru gareta. Ya shigo da sallama ciki-ciki ta amsa, kamar ta share shi ta dai ce ina ƙwana? Ba tare da ta dubeshi ba, ya ce ban ganshi ba,ta ɗan ɗago ido ta dube shi sanye yake cikin jeans blue da farar t.shirt,ta ɗan kama shi ya yi ƙyau sosai ya fito a Son Guy ɗin shi. Ta ce waye baka gani ba? Ya ce ƙwanan da kike tambaya, ta ɗan taɓe baki ya ce bana son taɓa bakinnan in kika ƙara zanyi maganin ki.
Umma ta zo daidai ƙofar ɗakin ta ce Ruƙayya bari in shiga nan gidan mai ɗanwake." Ta ce Umma kada ki daɗe zan fita ne." Dady ya ce "ina zaki ne." Ta ce sai kaji? Ya yi ɗan murmushi mai sauti ya ce to ai dai sai na yarda sannan za'a ko? Ta yi shiru ya taso ya dawo bakin gadon, ta matsa ya ce Pretty ni kike gudu? Kar dai ki manta ni mijinki ne, ta ɗan taɓe baki, bata ankara ba taji ya kamo leɓunanta ya manna mata kiss, tayi saurin duƙar da kanta yana ta dariya tayi banza dashi.
Wayarta ta soma ringing ta sa hannu ta ɗauka Nuraddeen ne cikin fara'a ta ce "Nuri kaga text ɗina? Ya ce eh, Mustapha yazo yana ce min yaga amarya." Na ce wallahi auren dole akai min, ban san mutumin ba ai kaga kiran da aka yi min ko? Ya ce eh, ta ce To ina isowa har an ɗaura." Ya ce Allah ya yi shine mijinki sai kiyi biyayya." Ta ce nagode, ya ce yaushe zaki shigo Legos? Ta ce nan da anjima ma zan taso, ya ce to sai kin shigo. Dady dake zaune yana jinsu ya ce "mu ga wayar?" Ta ce ina ruwanka da waya ta, ya ce ki bani ko na ƙwata. Ta tura cikin bireziya, ya ce ciro ki bani tayi banza dashi, ya haɗa hannuwanta guri ɗaya, ta ce zan maka ihu ya ce Kiyi mana ya tura hannu cikin rigar ta ya ciro wayar ya tura cikin aljihun shi. Sannan ya ce ba batun tafiya yau sai gobe,in ma mutum ya yi mini gardama in hana komawar. Jin haka sai tayi shiru.
Sallama ta ji kamar muryar M Bash, da gudu ta fito tana oyoyo M Bash ɗina." Munira ta ce kada ki taɓa ni shegiya ina Kaduna ina Abuja har sai dai naga ana nuna bikin ki a T.V ai Mom ma tace tana fushi dake. Ta ce wayyo nima fa auran nan yanda ku kaji shi haka naji shi,zo dai mu shiga. Suna shiga Munira taga abokin mijinta ta ce ashe ma angon yana ciki,ai ban san kaine angon namu ba,sai da na gani ana nuna dinner a ɗin newline, Ruƙayya ta ce zauna ƙawata kina ta zuba, ta ce Armaya'u ta iso?
Ruƙayya ta ce "a'a itama tana hanya ne?" M Bash ta ce eh tana hanya jiya muka shiryo tafiyar ta kira ni da dare ta ce nasan ana bikin ki? Na ce mata na dai gani a Talabijin shine muka ce bari muji laifin me mukayi?" Dady ya ce Gaskiya bata ƙyauta ba kuma babu inda bata kai kati ba sai ku.
Ruƙayya ta harareshi sannan ta ce "ni fa ina Legos, Affa ya yi min waya wai inzo, hankali tashe nazo garin nan,jiya kamar yanzun muna hanya,wai ina zuwa na samu an ɗaura min aure da wanda ban ce ina so ba." Ta soma hawaye,M Bash ta ce "Ni fa nasha mamakin ace kinyi aure bamu ji ba." Dady ya ce "Munira ina angon naki wato shine bai zo min ɗaurin aure jiya ba?" Ta ce to ai yazo maka na wancan satin, ya ce to ni wannan na gayyace shi wancan ai a garin yake. Ruƙayya ta tsani ta tuna Dady yana da aure,duk sai taji ta tsane shi. Ta dubi Munira ta ce M Bash bari in kawo miki ruwa, Munira ta ce ina Umma? Umma ta shiga maƙota, ta fita dan kawo ma M Bash ɗin ruwa.
Dady ya ce "Munira nayi mamaki da Pretty ƙawarki ce." Munira ta ce "wai Ruƙayya Aminiya ta ce ta wuce ƙawa,B.U.K muka haɗu baka ganta gurin bikina ba?" Ya ce sam amma ta taɓa baki labari na? Ta ce kasan Ruƙayya da shegen zurfin ciki, koda wasa ko sunan ka bata taɓa kira ba." Ya ce labari na da ita aƙwai tsawo wata rana zata gaya miki." Ta ce shikenan ina kuma Zainab? Ya ce tana Abuja kin san halin ku na mata wai bazata tsaya ba ta tafi.
Ta ce abinne sati É—aya fa? Ya ce ke da kinsan son da nake ma Pretty a rashin ta ne fa na auri Zee wallahi."
Ruƙayya ta shigo da sallama ta ajiye goran ruwan swan water da lakaseera. Umma da Armaya'u suka shigo tara Ruƙayya ta fito da murna ta ce lah Umma a ina kika samo mini Sadiya? M Bash ga Armaya'u, Armaya'u ta ce ashe ta riga ni,ɗakin ta shiga itama ta ce ashe angon namu yana ciki? Ruƙayya ta taɓa baki, ya ce bakinki baya jin horo ko zan gyara mishi zama. Suka yi dariya ban da Ruƙayya.
Sun gaisa da Armaya'u take tambayar shi Zainab, ya ce tana Abuja Armaya'u ta ce lallai kaji daɗi mai mata biyu cikin sati ɗaya. Ruƙayya ta yi waje, ya ce ku daina fada naga kamar Pretty batason ana labarin Zee. Suka sa mishi dariya, ya miƙe daidai sanda Ruƙayya ta dawo ɗakin. Pretty zan tafi na barki da baƙin ki,bata tanka ba ta wuce ta zauna Armaya'u ta ce "Ruƙy ana miki magana." Ta ce me zan ce mishi na riƙe shi ne? M Bash ta ce ke dai Allah ya yi ƴar iska." Ya ce kuna nan ne? Suka ce gobe zamu tafi, ya ce Ok,zan shigo zuwa dare. Ruƙayya ta ce baka bani wayata ba, ya tafi yana faɗin da kin ƙwata ai.
Yana tafiya suka hauta da masifa ta ce ba fa sonshi nike yi ba don ma na barshi ya zauna ne shi ne harda ce min zai tafi, Armaya'u ta ce munafuka daga ganin yanda kike mai wannan kallon ƙasa-ƙasan kin sonshi,ai wannan gayen baya cikin mazan da za'a gani ace ba'a so. M Bash ta ce ƴar iska tana sonshi Ruƙy munafuka ce kin santa sumumi sumumi da ita. Ruƙayya ta ce "ko yana burge wasu banda ni yana da fa mata gaskiya bana son kishiya,auren dole ga kishiya? Ba zan iya ba." Har suna haɗa baki "Kada ki iya." M Bash ta ce dama yanzun ya ce mu daina maganar Zainab ba ƙya so." Ta ce mukayi dashi? Armaya'u ta ce ke kishiya ce zata baki tsoro? Gara ma ki tashi ki riƙe mijinki" M Bash ta ce ballantana Zainab,ni ranar da su Mom da ƙawatar suke labarinta da Mamanta duk saina raina mata wayo. Ruƙayya ta ce wacece Zainab ki bani labarin ta mana?" M Bash ta ce "Zainab Adam mahaifinta ministane haifaffen Sokoto, uwar ta ƴar Gombe ce ni ko bafullatana ce a Yoben Oho,bata da mutunci matanshi uku ance duk sai da ta koresu, harda matarshi ta farko wacce sukayi auren saurayi da budurwa, ƴaƴan ta biyu duk mata Zainab sai ƙanwar ta Jamila, sauran kishiyoyin data kora sune masu yara maza.
Ance tana ji da Zainab sai dai babu tarbiyya, tamkar karuwa haka Zainab ta rinƙa bin maza, Uban dama an gama dashi, shegen son kuɗi ne da uwar harma ƴar in gaya miki shine aka yi rufa-rufa aka bawa mijinki.
Ruƙayya ta ce "na shiga uku banason kishi da mace mai shige-shige aje a sabauta ni a banza." Armaya'u ta ce ba sai ki nemi tsari gurin Allah ba,ga addu'o'i nan na tsari. Ruƙayya ta ce nidai an haɗani da aiki ina da kishi mai tsanani musamman akan Dady wallahi da ace be aure ba bazan damu ba.
M Bash ta ce "kamar ya ya?" Nan Ruƙayya ta basu labarin farkon haɗuwarta da Dady har zuwa yanda abubuwa suka kasance ta ɗaga yatsun hannunta,kunga zobunan alƙawuran da muka yi ma juna har sau biyu. Armaya'u ku kanku shaidu ne cewa bana kula kowa, amma ba tashi ganin Dady ba sai in ganshi da budurwa, M Bash in bazaku manta ba lokacin da muka je bikin Uncle ɗin ku ban dawo Kaduna da lafiya ba." M Bash ta ce ƙwarai har Mom tasa Dakta ya duba ki." Ta ce kin tuna to lokacin ne na ganshi da wannan Zainab ɗin haka ganina na biyu,dan na uku ma tsabar wulaƙanci ban ganshi ba sune suka ganni suka rage min hanya amma ƙala bai ce min ba har na sauka, shi ne don iko aka ɗaura min aure dashi.
*** *** ***
Sun jinjina labarin data basu, sannan suka bata shawarar yanda zata zauna da mijinta. M Bash ta ce kada ki damu kin san kana naka tsarin Allah na nashi, Allah ya tsara ku biyun ne matanshi.
Umma ta zo daidai ƙofar ɗakin ta ce Ruƙayya bari in shiga nan gidan mai ɗanwake." Ta ce Umma kada ki daɗe zan fita ne." Dady ya ce "ina zaki ne." Ta ce sai kaji? Ya yi ɗan murmushi mai sauti ya ce to ai dai sai na yarda sannan za'a ko? Ta yi shiru ya taso ya dawo bakin gadon, ta matsa ya ce Pretty ni kike gudu? Kar dai ki manta ni mijinki ne, ta ɗan taɓe baki, bata ankara ba taji ya kamo leɓunanta ya manna mata kiss, tayi saurin duƙar da kanta yana ta dariya tayi banza dashi.
Wayarta ta soma ringing ta sa hannu ta ɗauka Nuraddeen ne cikin fara'a ta ce "Nuri kaga text ɗina? Ya ce eh, Mustapha yazo yana ce min yaga amarya." Na ce wallahi auren dole akai min, ban san mutumin ba ai kaga kiran da aka yi min ko? Ya ce eh, ta ce To ina isowa har an ɗaura." Ya ce Allah ya yi shine mijinki sai kiyi biyayya." Ta ce nagode, ya ce yaushe zaki shigo Legos? Ta ce nan da anjima ma zan taso, ya ce to sai kin shigo. Dady dake zaune yana jinsu ya ce "mu ga wayar?" Ta ce ina ruwanka da waya ta, ya ce ki bani ko na ƙwata. Ta tura cikin bireziya, ya ce ciro ki bani tayi banza dashi, ya haɗa hannuwanta guri ɗaya, ta ce zan maka ihu ya ce Kiyi mana ya tura hannu cikin rigar ta ya ciro wayar ya tura cikin aljihun shi. Sannan ya ce ba batun tafiya yau sai gobe,in ma mutum ya yi mini gardama in hana komawar. Jin haka sai tayi shiru.
Sallama ta ji kamar muryar M Bash, da gudu ta fito tana oyoyo M Bash ɗina." Munira ta ce kada ki taɓa ni shegiya ina Kaduna ina Abuja har sai dai naga ana nuna bikin ki a T.V ai Mom ma tace tana fushi dake. Ta ce wayyo nima fa auran nan yanda ku kaji shi haka naji shi,zo dai mu shiga. Suna shiga Munira taga abokin mijinta ta ce ashe ma angon yana ciki,ai ban san kaine angon namu ba,sai da na gani ana nuna dinner a ɗin newline, Ruƙayya ta ce zauna ƙawata kina ta zuba, ta ce Armaya'u ta iso?
Ruƙayya ta ce "a'a itama tana hanya ne?" M Bash ta ce eh tana hanya jiya muka shiryo tafiyar ta kira ni da dare ta ce nasan ana bikin ki? Na ce mata na dai gani a Talabijin shine muka ce bari muji laifin me mukayi?" Dady ya ce Gaskiya bata ƙyauta ba kuma babu inda bata kai kati ba sai ku.
Ruƙayya ta harareshi sannan ta ce "ni fa ina Legos, Affa ya yi min waya wai inzo, hankali tashe nazo garin nan,jiya kamar yanzun muna hanya,wai ina zuwa na samu an ɗaura min aure da wanda ban ce ina so ba." Ta soma hawaye,M Bash ta ce "Ni fa nasha mamakin ace kinyi aure bamu ji ba." Dady ya ce "Munira ina angon naki wato shine bai zo min ɗaurin aure jiya ba?" Ta ce to ai yazo maka na wancan satin, ya ce to ni wannan na gayyace shi wancan ai a garin yake. Ruƙayya ta tsani ta tuna Dady yana da aure,duk sai taji ta tsane shi. Ta dubi Munira ta ce M Bash bari in kawo miki ruwa, Munira ta ce ina Umma? Umma ta shiga maƙota, ta fita dan kawo ma M Bash ɗin ruwa.
Dady ya ce "Munira nayi mamaki da Pretty ƙawarki ce." Munira ta ce "wai Ruƙayya Aminiya ta ce ta wuce ƙawa,B.U.K muka haɗu baka ganta gurin bikina ba?" Ya ce sam amma ta taɓa baki labari na? Ta ce kasan Ruƙayya da shegen zurfin ciki, koda wasa ko sunan ka bata taɓa kira ba." Ya ce labari na da ita aƙwai tsawo wata rana zata gaya miki." Ta ce shikenan ina kuma Zainab? Ya ce tana Abuja kin san halin ku na mata wai bazata tsaya ba ta tafi.
Ta ce abinne sati É—aya fa? Ya ce ke da kinsan son da nake ma Pretty a rashin ta ne fa na auri Zee wallahi."
Ruƙayya ta shigo da sallama ta ajiye goran ruwan swan water da lakaseera. Umma da Armaya'u suka shigo tara Ruƙayya ta fito da murna ta ce lah Umma a ina kika samo mini Sadiya? M Bash ga Armaya'u, Armaya'u ta ce ashe ta riga ni,ɗakin ta shiga itama ta ce ashe angon namu yana ciki? Ruƙayya ta taɓa baki, ya ce bakinki baya jin horo ko zan gyara mishi zama. Suka yi dariya ban da Ruƙayya.
Sun gaisa da Armaya'u take tambayar shi Zainab, ya ce tana Abuja Armaya'u ta ce lallai kaji daɗi mai mata biyu cikin sati ɗaya. Ruƙayya ta yi waje, ya ce ku daina fada naga kamar Pretty batason ana labarin Zee. Suka sa mishi dariya, ya miƙe daidai sanda Ruƙayya ta dawo ɗakin. Pretty zan tafi na barki da baƙin ki,bata tanka ba ta wuce ta zauna Armaya'u ta ce "Ruƙy ana miki magana." Ta ce me zan ce mishi na riƙe shi ne? M Bash ta ce ke dai Allah ya yi ƴar iska." Ya ce kuna nan ne? Suka ce gobe zamu tafi, ya ce Ok,zan shigo zuwa dare. Ruƙayya ta ce baka bani wayata ba, ya tafi yana faɗin da kin ƙwata ai.
Yana tafiya suka hauta da masifa ta ce ba fa sonshi nike yi ba don ma na barshi ya zauna ne shi ne harda ce min zai tafi, Armaya'u ta ce munafuka daga ganin yanda kike mai wannan kallon ƙasa-ƙasan kin sonshi,ai wannan gayen baya cikin mazan da za'a gani ace ba'a so. M Bash ta ce ƴar iska tana sonshi Ruƙy munafuka ce kin santa sumumi sumumi da ita. Ruƙayya ta ce "ko yana burge wasu banda ni yana da fa mata gaskiya bana son kishiya,auren dole ga kishiya? Ba zan iya ba." Har suna haɗa baki "Kada ki iya." M Bash ta ce dama yanzun ya ce mu daina maganar Zainab ba ƙya so." Ta ce mukayi dashi? Armaya'u ta ce ke kishiya ce zata baki tsoro? Gara ma ki tashi ki riƙe mijinki" M Bash ta ce ballantana Zainab,ni ranar da su Mom da ƙawatar suke labarinta da Mamanta duk saina raina mata wayo. Ruƙayya ta ce wacece Zainab ki bani labarin ta mana?" M Bash ta ce "Zainab Adam mahaifinta ministane haifaffen Sokoto, uwar ta ƴar Gombe ce ni ko bafullatana ce a Yoben Oho,bata da mutunci matanshi uku ance duk sai da ta koresu, harda matarshi ta farko wacce sukayi auren saurayi da budurwa, ƴaƴan ta biyu duk mata Zainab sai ƙanwar ta Jamila, sauran kishiyoyin data kora sune masu yara maza.
Ance tana ji da Zainab sai dai babu tarbiyya, tamkar karuwa haka Zainab ta rinƙa bin maza, Uban dama an gama dashi, shegen son kuɗi ne da uwar harma ƴar in gaya miki shine aka yi rufa-rufa aka bawa mijinki.
Ruƙayya ta ce "na shiga uku banason kishi da mace mai shige-shige aje a sabauta ni a banza." Armaya'u ta ce ba sai ki nemi tsari gurin Allah ba,ga addu'o'i nan na tsari. Ruƙayya ta ce nidai an haɗani da aiki ina da kishi mai tsanani musamman akan Dady wallahi da ace be aure ba bazan damu ba.
M Bash ta ce "kamar ya ya?" Nan Ruƙayya ta basu labarin farkon haɗuwarta da Dady har zuwa yanda abubuwa suka kasance ta ɗaga yatsun hannunta,kunga zobunan alƙawuran da muka yi ma juna har sau biyu. Armaya'u ku kanku shaidu ne cewa bana kula kowa, amma ba tashi ganin Dady ba sai in ganshi da budurwa, M Bash in bazaku manta ba lokacin da muka je bikin Uncle ɗin ku ban dawo Kaduna da lafiya ba." M Bash ta ce ƙwarai har Mom tasa Dakta ya duba ki." Ta ce kin tuna to lokacin ne na ganshi da wannan Zainab ɗin haka ganina na biyu,dan na uku ma tsabar wulaƙanci ban ganshi ba sune suka ganni suka rage min hanya amma ƙala bai ce min ba har na sauka, shi ne don iko aka ɗaura min aure dashi.
*** *** ***
Sun jinjina labarin data basu, sannan suka bata shawarar yanda zata zauna da mijinta. M Bash ta ce kada ki damu kin san kana naka tsarin Allah na nashi, Allah ya tsara ku biyun ne matanshi.