Sashe 15
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɗakinshi ya nufa sai da ya shirya sannan ya shigo ta fesa masa turarenta sannan ta ce ba haka ake yi ba,kaje ɗakin matarka sannan ka turo ta kirani ya ce ai kema matata ce kije ki kira ta, ta ce sai ranar da ka ƙwana ɗakina,kana namiji Dady sai na koya maka yanda zaka zauna damu, ya fita sai lokacin ya tashe ta daga bacci tun bayan da ta bar ɗakinshi da asubahi. Brush kawai tayi sannan ta fito ya ce je ki kira mana Pretty muyi break.
Ta ƙwanƙwasa ƙofar, Ruƙayya ta leƙo,kizo inji My dear tana wani yanga ita a dole ta ƙwana da miji dariya ma ta ba Ruƙayya, Sai dai ita kam taji zafi da kishin wannan gayun da Ruƙayya tayi gurin cin abinci tana rawar kan haɗa mishi gara a gabanshi shi kam hankalin nan nashi yana gurin Pretty sai taka mata ƙafa yake yi. Bayan sun gama ya yi musu nasihar zaman lafiya, sannan ya fita.
Ita dai Ruƙayya tun da ta shige ɗakinta ta ɗauki waya taga Dady ya lodo mata kuɗi har dubu biyar, shi ta soma kira tai mishi godiya, sannan ta cigaba da kiran ƴan'uwa da abokan arziƙi. Can da rana Dady ya kira ta ya tambayar taci abinci ko? Ta ce shifa? Ya ce Sunday ya kawo mishi amma bai fara ci ba." Ta ce "kaci yanzu zan je naci." Ita kuma taƙi fita ne saboda tana jin Zainab da ƙawayenta ne ko ƴan'uwanta ne Oho sun cika falon.
Biyar dai dai Dady ya shigo lokacin Pretty É—in tashi ta ci gayu cikin material ja, Zainab a saye da riga da wando ita a dole Æ´ar boko, aka je aka rungumo miji,gaban Pretty ya tsaya ta ce sannu da zuwa Babyna ya ce yauwa My Pretty, Zainab ta ja shi zo muje kayi wanka My dear, ya ce Prettyna bari in fito kin ji? Ta danne sannan ta ce sai na ganka.
Ɗaki ta koma ta shiga nazari lallai zama da kishiya sai ka dage, amma zata nuna mata ita za'a ma salo? kissa Zainab ta shiga nunawa yana shiga wanka itama ta shige wai zatayi mishi,tasan yanda take hillatar maza cikin sauƙi ta shawo kansa take ta fita dan cusawa Ruƙayya haushi. Amma kash bata nan ta koma ɗaki, jallabiya Dady ya saka shima cikin saurin yaje gurin Pretty ya zauna dining table yana faɗin har ta tashi Zainab dake tsaye cikin haushin yanda yake ta zumuɗin fitowar kishiyarta, sai ta ce bari na kirata,bata jiraba ta nufi ɗakin Ruƙayya daga ita sai zani ɗaurin ƙirji da ƙaramin tawul a kanta ta ƙwanƙwasa ƙofa sau biyu Ruƙayya ta buɗe Zainab ta cire tawul ɗin kanta tana faman tsane ɗan diddigar gashinta ita dole tayu wankan tsarki, Ruƙayya kizo inji My dear,nasan kin gaji da jiran shi yana can yana neman lada tana magana tana karairaya.
Haƙiƙa saƙonta ya isa ga Ruƙayya sai dai abinka ga lauya sai ta ce to muje. Cikin murmushi ta dafa Zainab ɗin ta cigaba da faɗin kin san duk inda Babyna zai je ya samo lada zan fiso ai naga saurin shi don Allah Zainab ki rinƙa bashi haƙƙinshi yanda ya dace banda sauri." Ta yi gaba zo muje mana.
Haushi ya kama Zainab bata so haka ba,kai wannan ƴar bariki ce sai ta ƙara ƙaimi maimakon taje gunsu sai ta tafi ɗaki ita ko Ruƙayya firij ta nufa ta ɗauko Hollandia mai sanyi ta cika kofi ta miƙa mishi tare da faɗin sha Babyna. Itama kanta tana mamakin yanda tasa mishi suna,kai kishiya tana sa mutum ya yi abin da bai shirya ba. Gayu Zainab tayi ta zauna tana karairaya, amma duk hankalinshi yana kan Pretty ɗin shi yakan manta kowa bare wata Zainab hakan yana ɗaga hankalin Zainab matuƙa. Ya yin da Ruƙayya taga fushi bazai mata ba gara ta zage ta ƙara kanainaye Dadynta hakanne ma yasa ta dage sai da ya kaita gidan aminiyarta Munira M Bash, ta yini sun je gidan Mom inda suka samo tsarabobi masu ƙyau Munira ta cusa mata ra'ayin saka ƙananun kaya ta ce da sune ta ƙara riƙe wuyan Mustapha. Basu bar gidan sai da suka je kasuwa ta ƙwaso wanduna zuwa siket da shegun riguna na ƴan gayun zamani suna shigowa Dady na zuwa,ya ɗauki matarshi sai gida.
A ƙwanakin girkinta Dady ya shiga ruɗu tare da ƙara sonta ya nane mata koda rana sai ya baro komai ya dawo ganinta bata sani ba ya soma shirya musu yawon shaƙatawa duk da ɗinbin aikin dake gabanshi, sai ana gobe tafiya sannan ya ce ta shirya su je Kaduna. Zainab ta soma masifa ya za'ayi ranar girkinta suje Kaduna, ya ce sallama zamu je yau zamu dawo, ta tsaya sororo ina kuma zaku? Ya ce wasu kaya zanje dubawa a England ina da mata biyu ba zanje na zauna gwauro ba ta ce to ai sai kaje dani tunda nice uwargida, ya ce sai wani lokacin yanzun da Pretty zamu je wasu abubuwan suna buƙatar sai da lauya, kuma kin san ita lauya ce sannan......." Ta ce kai dai kace kawai an mallake ka da,da ita kake zuwa? Ya ce to haka ɗin ne.
Umma ta ji daɗin ganin ƴar Autarta yanda tayi ƙyau gwanin sha'awa shima Affa haka yaji daɗi ganin ta ƙwantar da hankalinta yasan suna zaman lafiya daga gani. Momy ma tayi farin ciki ganin cikin ƴan ƙwanakin nan Dady ya yi ƙyau ga ƙwanciyar hankali, lallai Ruƙayya tana kula da shi kuma rai a bashi abin da yake so, duk kan kafet suka zauna tana bakin gado sha'awa suke bata, wani son Ruƙayya take ji a ranta. Ruƙayya ta ce Momy ina wuni? Ta amsa da lafiya lau ƴata,ya ya baƙon guri da abokiyar zaman taki? Ta ce lafiya lau tama ce agaishe ku," Dady ya dubeta da yaushe ta ce a gaida Momy? Harara Ruƙayya tayi mishi, cikin murmushi ta ce ina ruwanka? Momy ta ce ato sanda zata ce kana ina? Ya yi dariya shikenan.
Dad ma ya shigo sun gaisa shi kam ya kasa barma ranshi sai da yace ƴata wane abinci ki ke ba My Son? Naga ya ƙara zama gentleman ga ƙoshin lafiya yana yawo a jikinshi." Kunya ce ta kama Ruƙayya ta durƙusa tana gaishe shi ya ce ai mun gaisa, Dady ya ce tana kula da ni Dad fiye da yanda kake zato ya shafi gefen fuskarta ashe har yanzu tana sona da,ta ce bata sona Momy ta ce bana gaya maka ba dama kaƙi yarda. Ruƙayya ta ɓoye fuskarta cikin cinyar ta. Momy ta ce to maza ku ɗau hanya kada dare ya yi muku a hanya.
Ya bi Dad samanshi dan su É—an zanta harkar kasuwanci. Ya yin da Momy take tambayar ta badai wata matsala tsakanin ta da Zainab? ta ce babu komai.
Sun ɗau hanya Sabi'u direba ke jansu suna baya suna soyewa kanta ƙwance bisa jikinshi tana ta mishi shagwaɓa ita dai yaje da Zainab domin ta ce ita ya kamata ya soma fita da ita ya ce "Haba Pretty in banda ke ban ga matar da zata samu wannan damar ba, sannan ta ce bata so." Ta tashi zaune sannan tasa hannu ta ƙara jan labulen daya shiga tsakaninsu da mai tuƙinsu wato Sabi'u, ta sanyaya murya ta ce "Ni fa nafi son komai kayi adalci saboda mu gudu tare mu tsira tare." Ya ja leɓenta ya ce da ba dake nace zanje ba da yanzun ana nan ana zunɓura min baki.
To dukkan ku Matana ne da wacce naga dama da ita zanje." Ta ce Allah ko zan ji haushi daga baya zan gane kayi adalci ne, ya ce to duk naji bayan na gama mana komai shikenan sai na fasa ko mekike nufi?"
Tayi fari da idanuwanta ina nufin a cikin biyu ayi ɗaya ko dai ka tafi da ita ko kuma ayi ƙuri'a, ya ce kamar ya ya? Ta ce zaka samu paper ka rubuta zaman gida ɗayar ka rubuta tafiya ka bamu ita zata soma ɗauka kafin ni, duk wacce ta ɗauki zaman gida shikenan a tafi da ƴar'uwarta, hankalina zaifi ƙwanciya, ya ce Ni dai kin tadamin nawa" ta shiga shafa gefen fuskarshi in Allah yasa dani zaka ba makawa ka riƙe wannan.
Zainab kam da suka tafi Hajiyarta ta kirata tana faɗa mata abubuwan da suke faruwa ita kanta Hajiyar ta damu. Cikin masifa ta ce ke wato bakisan yanda zaki ƙwaci kanki ba? To kada ki sake ki yarda idan yazo ki hau masifa kice ke baki yarda ba sai dai ya barku ku duka,in kuma dole ne zuwan yaje daku ku duka,kin ji ko? Tunda yaƙi ki haɗa da masifa da kissa shi kanshi asirin ba daina shi zamuyi ba, canza wani malamin zamu yi. Ta ce to Hajiya.
*** *** ***
Jibgegiyar motar dake ɗauke dasu tayi parking a gurin daya dace cikin harabar gidan suka fito, Sabi'u ya yi gaba da motar ya kaita mazauninsu ita da taƙwarorinta,su kam ciki suka yi da sallama suka shiga falo.
Tana zaune amma bata amsa ba sanye take da atamfa super baƙa da jajayen falawoyi ƙafarta ɗaya kan ɗaya tana girgizata. Tana cika tana batsewa.
Ruƙayya ta dubeta "sannu da gida Zainab su Momy sun ce a gaisheki." Buɗar bakin ta sai tace "yauwa sannu da yawon cin amana,aini ban taɓa fita dashi ranar girkin ki ba." Ruƙayya ta ce "To kiyi haƙuri in girkina yazo kema ku tafi ko ina ne, ta wuce ɗaki cikin takaici.
Ta ƙwanƙwasa ƙofar, Ruƙayya ta leƙo,kizo inji My dear tana wani yanga ita a dole ta ƙwana da miji dariya ma ta ba Ruƙayya, Sai dai ita kam taji zafi da kishin wannan gayun da Ruƙayya tayi gurin cin abinci tana rawar kan haɗa mishi gara a gabanshi shi kam hankalin nan nashi yana gurin Pretty sai taka mata ƙafa yake yi. Bayan sun gama ya yi musu nasihar zaman lafiya, sannan ya fita.
Ita dai Ruƙayya tun da ta shige ɗakinta ta ɗauki waya taga Dady ya lodo mata kuɗi har dubu biyar, shi ta soma kira tai mishi godiya, sannan ta cigaba da kiran ƴan'uwa da abokan arziƙi. Can da rana Dady ya kira ta ya tambayar taci abinci ko? Ta ce shifa? Ya ce Sunday ya kawo mishi amma bai fara ci ba." Ta ce "kaci yanzu zan je naci." Ita kuma taƙi fita ne saboda tana jin Zainab da ƙawayenta ne ko ƴan'uwanta ne Oho sun cika falon.
Biyar dai dai Dady ya shigo lokacin Pretty É—in tashi ta ci gayu cikin material ja, Zainab a saye da riga da wando ita a dole Æ´ar boko, aka je aka rungumo miji,gaban Pretty ya tsaya ta ce sannu da zuwa Babyna ya ce yauwa My Pretty, Zainab ta ja shi zo muje kayi wanka My dear, ya ce Prettyna bari in fito kin ji? Ta danne sannan ta ce sai na ganka.
Ɗaki ta koma ta shiga nazari lallai zama da kishiya sai ka dage, amma zata nuna mata ita za'a ma salo? kissa Zainab ta shiga nunawa yana shiga wanka itama ta shige wai zatayi mishi,tasan yanda take hillatar maza cikin sauƙi ta shawo kansa take ta fita dan cusawa Ruƙayya haushi. Amma kash bata nan ta koma ɗaki, jallabiya Dady ya saka shima cikin saurin yaje gurin Pretty ya zauna dining table yana faɗin har ta tashi Zainab dake tsaye cikin haushin yanda yake ta zumuɗin fitowar kishiyarta, sai ta ce bari na kirata,bata jiraba ta nufi ɗakin Ruƙayya daga ita sai zani ɗaurin ƙirji da ƙaramin tawul a kanta ta ƙwanƙwasa ƙofa sau biyu Ruƙayya ta buɗe Zainab ta cire tawul ɗin kanta tana faman tsane ɗan diddigar gashinta ita dole tayu wankan tsarki, Ruƙayya kizo inji My dear,nasan kin gaji da jiran shi yana can yana neman lada tana magana tana karairaya.
Haƙiƙa saƙonta ya isa ga Ruƙayya sai dai abinka ga lauya sai ta ce to muje. Cikin murmushi ta dafa Zainab ɗin ta cigaba da faɗin kin san duk inda Babyna zai je ya samo lada zan fiso ai naga saurin shi don Allah Zainab ki rinƙa bashi haƙƙinshi yanda ya dace banda sauri." Ta yi gaba zo muje mana.
Haushi ya kama Zainab bata so haka ba,kai wannan ƴar bariki ce sai ta ƙara ƙaimi maimakon taje gunsu sai ta tafi ɗaki ita ko Ruƙayya firij ta nufa ta ɗauko Hollandia mai sanyi ta cika kofi ta miƙa mishi tare da faɗin sha Babyna. Itama kanta tana mamakin yanda tasa mishi suna,kai kishiya tana sa mutum ya yi abin da bai shirya ba. Gayu Zainab tayi ta zauna tana karairaya, amma duk hankalinshi yana kan Pretty ɗin shi yakan manta kowa bare wata Zainab hakan yana ɗaga hankalin Zainab matuƙa. Ya yin da Ruƙayya taga fushi bazai mata ba gara ta zage ta ƙara kanainaye Dadynta hakanne ma yasa ta dage sai da ya kaita gidan aminiyarta Munira M Bash, ta yini sun je gidan Mom inda suka samo tsarabobi masu ƙyau Munira ta cusa mata ra'ayin saka ƙananun kaya ta ce da sune ta ƙara riƙe wuyan Mustapha. Basu bar gidan sai da suka je kasuwa ta ƙwaso wanduna zuwa siket da shegun riguna na ƴan gayun zamani suna shigowa Dady na zuwa,ya ɗauki matarshi sai gida.
A ƙwanakin girkinta Dady ya shiga ruɗu tare da ƙara sonta ya nane mata koda rana sai ya baro komai ya dawo ganinta bata sani ba ya soma shirya musu yawon shaƙatawa duk da ɗinbin aikin dake gabanshi, sai ana gobe tafiya sannan ya ce ta shirya su je Kaduna. Zainab ta soma masifa ya za'ayi ranar girkinta suje Kaduna, ya ce sallama zamu je yau zamu dawo, ta tsaya sororo ina kuma zaku? Ya ce wasu kaya zanje dubawa a England ina da mata biyu ba zanje na zauna gwauro ba ta ce to ai sai kaje dani tunda nice uwargida, ya ce sai wani lokacin yanzun da Pretty zamu je wasu abubuwan suna buƙatar sai da lauya, kuma kin san ita lauya ce sannan......." Ta ce kai dai kace kawai an mallake ka da,da ita kake zuwa? Ya ce to haka ɗin ne.
Umma ta ji daɗin ganin ƴar Autarta yanda tayi ƙyau gwanin sha'awa shima Affa haka yaji daɗi ganin ta ƙwantar da hankalinta yasan suna zaman lafiya daga gani. Momy ma tayi farin ciki ganin cikin ƴan ƙwanakin nan Dady ya yi ƙyau ga ƙwanciyar hankali, lallai Ruƙayya tana kula da shi kuma rai a bashi abin da yake so, duk kan kafet suka zauna tana bakin gado sha'awa suke bata, wani son Ruƙayya take ji a ranta. Ruƙayya ta ce Momy ina wuni? Ta amsa da lafiya lau ƴata,ya ya baƙon guri da abokiyar zaman taki? Ta ce lafiya lau tama ce agaishe ku," Dady ya dubeta da yaushe ta ce a gaida Momy? Harara Ruƙayya tayi mishi, cikin murmushi ta ce ina ruwanka? Momy ta ce ato sanda zata ce kana ina? Ya yi dariya shikenan.
Dad ma ya shigo sun gaisa shi kam ya kasa barma ranshi sai da yace ƴata wane abinci ki ke ba My Son? Naga ya ƙara zama gentleman ga ƙoshin lafiya yana yawo a jikinshi." Kunya ce ta kama Ruƙayya ta durƙusa tana gaishe shi ya ce ai mun gaisa, Dady ya ce tana kula da ni Dad fiye da yanda kake zato ya shafi gefen fuskarta ashe har yanzu tana sona da,ta ce bata sona Momy ta ce bana gaya maka ba dama kaƙi yarda. Ruƙayya ta ɓoye fuskarta cikin cinyar ta. Momy ta ce to maza ku ɗau hanya kada dare ya yi muku a hanya.
Ya bi Dad samanshi dan su É—an zanta harkar kasuwanci. Ya yin da Momy take tambayar ta badai wata matsala tsakanin ta da Zainab? ta ce babu komai.
Sun ɗau hanya Sabi'u direba ke jansu suna baya suna soyewa kanta ƙwance bisa jikinshi tana ta mishi shagwaɓa ita dai yaje da Zainab domin ta ce ita ya kamata ya soma fita da ita ya ce "Haba Pretty in banda ke ban ga matar da zata samu wannan damar ba, sannan ta ce bata so." Ta tashi zaune sannan tasa hannu ta ƙara jan labulen daya shiga tsakaninsu da mai tuƙinsu wato Sabi'u, ta sanyaya murya ta ce "Ni fa nafi son komai kayi adalci saboda mu gudu tare mu tsira tare." Ya ja leɓenta ya ce da ba dake nace zanje ba da yanzun ana nan ana zunɓura min baki.
To dukkan ku Matana ne da wacce naga dama da ita zanje." Ta ce Allah ko zan ji haushi daga baya zan gane kayi adalci ne, ya ce to duk naji bayan na gama mana komai shikenan sai na fasa ko mekike nufi?"
Tayi fari da idanuwanta ina nufin a cikin biyu ayi ɗaya ko dai ka tafi da ita ko kuma ayi ƙuri'a, ya ce kamar ya ya? Ta ce zaka samu paper ka rubuta zaman gida ɗayar ka rubuta tafiya ka bamu ita zata soma ɗauka kafin ni, duk wacce ta ɗauki zaman gida shikenan a tafi da ƴar'uwarta, hankalina zaifi ƙwanciya, ya ce Ni dai kin tadamin nawa" ta shiga shafa gefen fuskarshi in Allah yasa dani zaka ba makawa ka riƙe wannan.
Zainab kam da suka tafi Hajiyarta ta kirata tana faɗa mata abubuwan da suke faruwa ita kanta Hajiyar ta damu. Cikin masifa ta ce ke wato bakisan yanda zaki ƙwaci kanki ba? To kada ki sake ki yarda idan yazo ki hau masifa kice ke baki yarda ba sai dai ya barku ku duka,in kuma dole ne zuwan yaje daku ku duka,kin ji ko? Tunda yaƙi ki haɗa da masifa da kissa shi kanshi asirin ba daina shi zamuyi ba, canza wani malamin zamu yi. Ta ce to Hajiya.
*** *** ***
Jibgegiyar motar dake ɗauke dasu tayi parking a gurin daya dace cikin harabar gidan suka fito, Sabi'u ya yi gaba da motar ya kaita mazauninsu ita da taƙwarorinta,su kam ciki suka yi da sallama suka shiga falo.
Tana zaune amma bata amsa ba sanye take da atamfa super baƙa da jajayen falawoyi ƙafarta ɗaya kan ɗaya tana girgizata. Tana cika tana batsewa.
Ruƙayya ta dubeta "sannu da gida Zainab su Momy sun ce a gaisheki." Buɗar bakin ta sai tace "yauwa sannu da yawon cin amana,aini ban taɓa fita dashi ranar girkin ki ba." Ruƙayya ta ce "To kiyi haƙuri in girkina yazo kema ku tafi ko ina ne, ta wuce ɗaki cikin takaici.