Sashe 20
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin ya tafi sai da ya tada fitina domin su Momy sunce zasu gyara mata sasanta ta koma ta ce ita dai anan zata zauna ɗakin Momy, Momy ta ce shikenan ma nima zanfi son haka don inma kina can zan raba hankali na biyu ne, Dady ya ce shida so yake su tafi tare, ta ce a'a,su Momy suka ɗaure mata gindin zama, bayan fitar Momy ya zauna kusa da ita ya ce Pretty ki dubi girman Allah da girman son da nake miki ki gayan gurin da kikaje aka yo ma Zainab wannan asirin nasa a karya, zalunci ba ƙyau kefa kike min wa'azi.
Takaici ya kamata hawaye ya soma zubo mata ya ce kash kinga matsalar ki to menene abin kuka,Ni ba abinda zan miki, ta ce nifa Dady ban mata komai ba ƙarya kake son in maka? Allah ban san komai game da abin da kake tuhuma ta ba,yaja tsaki aike aƙwai ki da gaddama ne, Allah in har baki faɗa ba sai na haɗa ki da Affa,ido ta tsura mishi a ranta tana tuna kafin aurensu tamkar ya haɗiye ta, yanzun kam gashi zaune yana ƙulla mata sharri,sharrin ma gaya masa aka yi yaci ya auna amma ya hau kai ya zauna, ta ƙwanta tare da faɗin ka gaya masa mana,ta cigaba gaskiya nifa na gaji ban iya faɗa ba bazan iya zama da mafaɗaci ba ka gane? Auren nan babu dole dama sai da nace a'a aka matsa min, wani sabon haushin ne ya kamashi ya ce cikin masifar tashi dama na sani ba sona kike yi ba, to amma ai sai kibar masu sona su so ni ko? Sai kije ki mana mugunta.
Aure kuma da kike faÉ—in babu dole shine kuwa dole domin ba saki cikin shi duk wahala dole ki jure, ya fita gara ma ki faÉ—a min gurin da ki ka yo wannan mugun abun dan kin san ni ba mazinaci bane bare in bi na waje bazanje ina kallon matata kuma batada amfani a gurina ba.
Ya fita ta ƙwanta tana kuka,jin shigowar Momy sai tayi tamkar tana bacci shiru tayi tana tuna kai aure yana da daɗi da wuya, amma wuyar tafi yawa, shiyasa kowa sai ya ce Allah ya bada zaman haƙuri Allah ya saɓa halayya, gaskiya ne ta tuna yanda Affanta da Umma kai har da yayyenta suka yi ta jaddada mata kalmar nan ta haƙuri,lallai dole tayi haƙuri.
*** *** ***
Lokacin da Dady ya isa gida Zainab suna tare da Sunday ya soma zuga mata kira tsoro ya kama su amma sai ta ɓoye shi cikin wardrobe ta fito tamkar mai bacci tana mishi sannu da zuwa,ya zauna ta kawo mishi Hollandia mai sanyi ya ce ina Sunday ya shirya min table ina jin yunwa sosai,ta ɗan daburce,na na aike shi gidanmu, to bari inyi wanka in yaso ke sai kije ki min abinda zan ci tunda kin aike shi me ya hana ki aiki direba? Sunday ba ɗan aike bane,ta ce yi haƙuri,ya nufi ɗakinshi ita kuma ta nufi kitchen sai da ta tabbatar ya shiga ɗakin sannan ta fito ta buɗe Sunday,a sittin ɗin shi ya fito yanda yake gudun yaso bata dariya duk abinda aka ce babu gaskiya aƙwai matsala, Allah ka tsaremu da shiga halaka.
Momy da Dad suna ji da Ruƙayya tamkar ƙwai duk abinda take so shi za a bata har sai ya hau kanta yanzun an tashi daga tuwon Hajja an koma ɗan waken Umma kullum direba sai yaje ya karɓo, Hollandia ko abin har tsoro yake basu dashi take karyawa haka cikin dare, ta murmure sosai, wannan karon Dady satin shi uku sannan yazo.
Ya sameta tayi gayu sosai cikin material mai bulun fulawoyi tayi ɓul,ɓul gwanin sha'awa dan cikin yasata haske,ta ɗaure gashin ta daya sha gyara salon taje aka gyara mata, Momy sun tafi biki ita kaɗai ce a gidan ya zuba mata ido. Ta ce mishi sannu da zuwa ya hanya? Ya ce lafiya lau Pretty gaskiya kinji sauƙi kin yi ƙyau wannan karon zamu koma Abuja ko? Nan take tasha mur,tayi kicin-kicin da rai gaskiya kada ma ka soma babu inda zanje bayan haka ma ina jiran na haihu nayi gaba rayuwa da kai Dady ba zata yiwu min ba, dole in haƙura da kai.
Ya ce haba Pretty yanzun daga zuwa na,kin tareni da wannan maganar ko ruwa baki bani ba,in kina furta rabuwa tsakaninmu,ji nake tamkar kina watsamin ruwan zafi, babu wannan a tsarin aurenmu ki tuna wahalar da nasha a kanki,nasha wahala a kanki, ta ce shi ne yasa yanzun ka ke fanshe wahalar ka a kaina? Ya ce duk mu bar maganar naji baza muje Abuja ba, amma sai mu koma sashenmu in yaso in na tafi saiki dawo nan. Ta ce a'a nifa ba zanje ko'ina ba,me kake son su Momy su ɗaukeni? Ya ce to ni shikenan sai nayi ta zama cikin ƙunci alhalin ina da mata har biyu gaskiya Pretty ki duba dai.
A ranta ta ce tunda kanada buƙata ai dole ka ƙwantar da murya, inda maza suke bata mamaki kenan ko sarki ne yakan hura hancinshi a fada daya shigo gida gaban mace koda sa'ar ƴarshi ce dole ya yi biyayya ya ƙwantar da murya,tana tunani bata san ma har yazo kusa da ita ya zauna ba, sai dai ji tayi ya jawo ta jikinshi tayi mutsu-mutsu alamar ƙwacewa ya ce haba Pretty ki ji tausayi na mana? Ta ce cikin shagwaɓa baka ce nai muku asiri ba? Da yake namiji wawane wani sa'in sai ya ce nima Zainab ce ta ce min ke ce kikayi mana,ta ce kayi bincike ka gane, ya ce ni kaina bana gane kaina ƙwanan nan ban san meke sani yin wasu abubuwan ba,in ina son inyi tunani sai na kasa kome yasa? Ta ce kana addu'a,yayi shiru can ya ce gaskiya bana addu'a akan matsalar.
Ta ce ai kaji matsalar ga addu'o'i nan cikin husnil muslim kana dashi wasu ma suna kanka amma ka kasa, ya ce haka ne zan kula yanzun ya zamuyi? Ta ce likita ya ce fa na huta, ya soma kiran layin likitan ta tsura mishi ido dariya yake bata duk ya birkice sun gaisa da likitan ko kunya yake tambayar likitan ko zai iya kusantar matarsa yanzun don yaga taji sauƙi sosai likitan ya ce me zai hana? Yanzun ne ma zakafi samun natsuwa domin mace in tanada ciki ta kanfi sanda take amarya sai dai ka biya sannu a hankali.
Ya dubeta yana murmushi ina Momy ta je ta ce taje biki nasan ta kusa dawowa ya kamo hannunta zo muje in nuna miki wani abu a sasanmu,ya jata in so ya haÉ—u da so sai soyewa, abinda ya faru kenan, Dady kam ya shiga ruÉ—u. Sanda suka dawo sasan Momy ta jima da dawowa ta ce mijinki yazo ne shiyasa na neme ki na rasa naso in kira wayarki sai kuma na ganta a kan gado.
Kunya ta kama Ruƙayya ta sosa wuyanta ta ce eh dama shi ne yazo,shi kam dariya yake mata ya ce Momy ƴar taki taji sauƙi na ce ko zamu koma tare ne? Ruƙayya ta yi saurin cewa Allah nifa bazan je ba Momy, Momy ta ce in dai zaki bishi to ku tafi,ta ce ni bazan je ba ta turo baki Momy ta ce shikenan daina fushi.
Ƙwana uku ya yi sai sun fita wai gurin likita Momy har dariya suke bata ita za'ayi wa wayo, ya tafi da ƴar nutsuwa tunda tana yawan matsa mishi yanayin addu'o'i duk sati ɗaya sai yazo Momy tasa ta share sashen su in yazo sai ta koma can in ya tafi ta dawo gurin Momy,sai dai shegen faɗan nan na nan amma ba kamar da ba, Ruƙayya anyi ƙyau kamar ta fashe cikin ya fito gwanin sha'awa.
Zainab dai batasan Ruƙayya tana da ciki ba,sai wannan dawowar da Dady ya yi inda yake ce mata Pretty ta shiga watan haihuwar ta zai koma Kaduna kullum ya dinga zuwa Abuja ofis, ta ce ai wai kana nufin Ruƙayya ciki ne da ita? Ya ce au baki sani ba? Ai ta kusa haihuwa, kinga ke kaɗai na manta ban gaya miki ba.
Nan ta miƙe cikin tashin hankali lallai Dady ka kasa nema min magani balle in samu lafiya, amma ita kai mata ciki,koda yake ƙila nice bakason na haihu shiyasa, ya ce ke kada fa ki dameni, kinga nasan kin gama zubar da ƙwayoyin ki a titi zaki min surutun banza kodan kinga ban gaya miki sakamakon da likitan ya gaya min ba to tunda kinso ji yanzu zakiji ya ce bazaki haihu ba sakamakon shan ƙwayoyin hana haihuwa, magani kije can ki nema da kanki nidai tunda nasan lafiya ta qalau shikenan ya sa kai ya wuce.
Mantuwar da Dady ya yi itace ta dawo dashi gida,sai da ya bincike ɗakinshi kaf baiga jakar ba, kuɗi ne Naira miliyan uku da dubu ɗari baƙwai ba canji duk daloline na America zai biya cikon kuɗin wani inji daya siya da wani banki suka yi gwanjo amma ya nemi jakar ya rasa,ɗakin Zainab ya nufa yasan tana nan tana shegen baccinta da ta iya.
Gabanshi ne Ya yi mummunan faɗuwa mai zai gani Sunday da Zainab,sam basu san yana tsaye ba ma da ƙarfi ya furta innalillahi ya nufi gurinsu wani abin da yafi ɗaure mishi kai da sun ganshi amma sun kasa barin abin da suke, ya ɗauki waya ya kira Hajiyar Zainab ya ce tazo yanzun nan ya fito ya ja musu ƙofa don takaici hawaye yana zubo mishi, to dama asirin in sun fara masha'arsu sai sun kai awa biyar sannan zasu dawo hankalinsu kuma shigar su kenan ya dawo don haka har Hajiya ta zo ya ce ta shiga ɗaki gashi nan zuwa, ta zata faɗa sukayi tana shiga ta samu saɓanin haka.
Takaici ya kamata hawaye ya soma zubo mata ya ce kash kinga matsalar ki to menene abin kuka,Ni ba abinda zan miki, ta ce nifa Dady ban mata komai ba ƙarya kake son in maka? Allah ban san komai game da abin da kake tuhuma ta ba,yaja tsaki aike aƙwai ki da gaddama ne, Allah in har baki faɗa ba sai na haɗa ki da Affa,ido ta tsura mishi a ranta tana tuna kafin aurensu tamkar ya haɗiye ta, yanzun kam gashi zaune yana ƙulla mata sharri,sharrin ma gaya masa aka yi yaci ya auna amma ya hau kai ya zauna, ta ƙwanta tare da faɗin ka gaya masa mana,ta cigaba gaskiya nifa na gaji ban iya faɗa ba bazan iya zama da mafaɗaci ba ka gane? Auren nan babu dole dama sai da nace a'a aka matsa min, wani sabon haushin ne ya kamashi ya ce cikin masifar tashi dama na sani ba sona kike yi ba, to amma ai sai kibar masu sona su so ni ko? Sai kije ki mana mugunta.
Aure kuma da kike faÉ—in babu dole shine kuwa dole domin ba saki cikin shi duk wahala dole ki jure, ya fita gara ma ki faÉ—a min gurin da ki ka yo wannan mugun abun dan kin san ni ba mazinaci bane bare in bi na waje bazanje ina kallon matata kuma batada amfani a gurina ba.
Ya fita ta ƙwanta tana kuka,jin shigowar Momy sai tayi tamkar tana bacci shiru tayi tana tuna kai aure yana da daɗi da wuya, amma wuyar tafi yawa, shiyasa kowa sai ya ce Allah ya bada zaman haƙuri Allah ya saɓa halayya, gaskiya ne ta tuna yanda Affanta da Umma kai har da yayyenta suka yi ta jaddada mata kalmar nan ta haƙuri,lallai dole tayi haƙuri.
*** *** ***
Lokacin da Dady ya isa gida Zainab suna tare da Sunday ya soma zuga mata kira tsoro ya kama su amma sai ta ɓoye shi cikin wardrobe ta fito tamkar mai bacci tana mishi sannu da zuwa,ya zauna ta kawo mishi Hollandia mai sanyi ya ce ina Sunday ya shirya min table ina jin yunwa sosai,ta ɗan daburce,na na aike shi gidanmu, to bari inyi wanka in yaso ke sai kije ki min abinda zan ci tunda kin aike shi me ya hana ki aiki direba? Sunday ba ɗan aike bane,ta ce yi haƙuri,ya nufi ɗakinshi ita kuma ta nufi kitchen sai da ta tabbatar ya shiga ɗakin sannan ta fito ta buɗe Sunday,a sittin ɗin shi ya fito yanda yake gudun yaso bata dariya duk abinda aka ce babu gaskiya aƙwai matsala, Allah ka tsaremu da shiga halaka.
Momy da Dad suna ji da Ruƙayya tamkar ƙwai duk abinda take so shi za a bata har sai ya hau kanta yanzun an tashi daga tuwon Hajja an koma ɗan waken Umma kullum direba sai yaje ya karɓo, Hollandia ko abin har tsoro yake basu dashi take karyawa haka cikin dare, ta murmure sosai, wannan karon Dady satin shi uku sannan yazo.
Ya sameta tayi gayu sosai cikin material mai bulun fulawoyi tayi ɓul,ɓul gwanin sha'awa dan cikin yasata haske,ta ɗaure gashin ta daya sha gyara salon taje aka gyara mata, Momy sun tafi biki ita kaɗai ce a gidan ya zuba mata ido. Ta ce mishi sannu da zuwa ya hanya? Ya ce lafiya lau Pretty gaskiya kinji sauƙi kin yi ƙyau wannan karon zamu koma Abuja ko? Nan take tasha mur,tayi kicin-kicin da rai gaskiya kada ma ka soma babu inda zanje bayan haka ma ina jiran na haihu nayi gaba rayuwa da kai Dady ba zata yiwu min ba, dole in haƙura da kai.
Ya ce haba Pretty yanzun daga zuwa na,kin tareni da wannan maganar ko ruwa baki bani ba,in kina furta rabuwa tsakaninmu,ji nake tamkar kina watsamin ruwan zafi, babu wannan a tsarin aurenmu ki tuna wahalar da nasha a kanki,nasha wahala a kanki, ta ce shi ne yasa yanzun ka ke fanshe wahalar ka a kaina? Ya ce duk mu bar maganar naji baza muje Abuja ba, amma sai mu koma sashenmu in yaso in na tafi saiki dawo nan. Ta ce a'a nifa ba zanje ko'ina ba,me kake son su Momy su ɗaukeni? Ya ce to ni shikenan sai nayi ta zama cikin ƙunci alhalin ina da mata har biyu gaskiya Pretty ki duba dai.
A ranta ta ce tunda kanada buƙata ai dole ka ƙwantar da murya, inda maza suke bata mamaki kenan ko sarki ne yakan hura hancinshi a fada daya shigo gida gaban mace koda sa'ar ƴarshi ce dole ya yi biyayya ya ƙwantar da murya,tana tunani bata san ma har yazo kusa da ita ya zauna ba, sai dai ji tayi ya jawo ta jikinshi tayi mutsu-mutsu alamar ƙwacewa ya ce haba Pretty ki ji tausayi na mana? Ta ce cikin shagwaɓa baka ce nai muku asiri ba? Da yake namiji wawane wani sa'in sai ya ce nima Zainab ce ta ce min ke ce kikayi mana,ta ce kayi bincike ka gane, ya ce ni kaina bana gane kaina ƙwanan nan ban san meke sani yin wasu abubuwan ba,in ina son inyi tunani sai na kasa kome yasa? Ta ce kana addu'a,yayi shiru can ya ce gaskiya bana addu'a akan matsalar.
Ta ce ai kaji matsalar ga addu'o'i nan cikin husnil muslim kana dashi wasu ma suna kanka amma ka kasa, ya ce haka ne zan kula yanzun ya zamuyi? Ta ce likita ya ce fa na huta, ya soma kiran layin likitan ta tsura mishi ido dariya yake bata duk ya birkice sun gaisa da likitan ko kunya yake tambayar likitan ko zai iya kusantar matarsa yanzun don yaga taji sauƙi sosai likitan ya ce me zai hana? Yanzun ne ma zakafi samun natsuwa domin mace in tanada ciki ta kanfi sanda take amarya sai dai ka biya sannu a hankali.
Ya dubeta yana murmushi ina Momy ta je ta ce taje biki nasan ta kusa dawowa ya kamo hannunta zo muje in nuna miki wani abu a sasanmu,ya jata in so ya haÉ—u da so sai soyewa, abinda ya faru kenan, Dady kam ya shiga ruÉ—u. Sanda suka dawo sasan Momy ta jima da dawowa ta ce mijinki yazo ne shiyasa na neme ki na rasa naso in kira wayarki sai kuma na ganta a kan gado.
Kunya ta kama Ruƙayya ta sosa wuyanta ta ce eh dama shi ne yazo,shi kam dariya yake mata ya ce Momy ƴar taki taji sauƙi na ce ko zamu koma tare ne? Ruƙayya ta yi saurin cewa Allah nifa bazan je ba Momy, Momy ta ce in dai zaki bishi to ku tafi,ta ce ni bazan je ba ta turo baki Momy ta ce shikenan daina fushi.
Ƙwana uku ya yi sai sun fita wai gurin likita Momy har dariya suke bata ita za'ayi wa wayo, ya tafi da ƴar nutsuwa tunda tana yawan matsa mishi yanayin addu'o'i duk sati ɗaya sai yazo Momy tasa ta share sashen su in yazo sai ta koma can in ya tafi ta dawo gurin Momy,sai dai shegen faɗan nan na nan amma ba kamar da ba, Ruƙayya anyi ƙyau kamar ta fashe cikin ya fito gwanin sha'awa.
Zainab dai batasan Ruƙayya tana da ciki ba,sai wannan dawowar da Dady ya yi inda yake ce mata Pretty ta shiga watan haihuwar ta zai koma Kaduna kullum ya dinga zuwa Abuja ofis, ta ce ai wai kana nufin Ruƙayya ciki ne da ita? Ya ce au baki sani ba? Ai ta kusa haihuwa, kinga ke kaɗai na manta ban gaya miki ba.
Nan ta miƙe cikin tashin hankali lallai Dady ka kasa nema min magani balle in samu lafiya, amma ita kai mata ciki,koda yake ƙila nice bakason na haihu shiyasa, ya ce ke kada fa ki dameni, kinga nasan kin gama zubar da ƙwayoyin ki a titi zaki min surutun banza kodan kinga ban gaya miki sakamakon da likitan ya gaya min ba to tunda kinso ji yanzu zakiji ya ce bazaki haihu ba sakamakon shan ƙwayoyin hana haihuwa, magani kije can ki nema da kanki nidai tunda nasan lafiya ta qalau shikenan ya sa kai ya wuce.
Mantuwar da Dady ya yi itace ta dawo dashi gida,sai da ya bincike ɗakinshi kaf baiga jakar ba, kuɗi ne Naira miliyan uku da dubu ɗari baƙwai ba canji duk daloline na America zai biya cikon kuɗin wani inji daya siya da wani banki suka yi gwanjo amma ya nemi jakar ya rasa,ɗakin Zainab ya nufa yasan tana nan tana shegen baccinta da ta iya.
Gabanshi ne Ya yi mummunan faɗuwa mai zai gani Sunday da Zainab,sam basu san yana tsaye ba ma da ƙarfi ya furta innalillahi ya nufi gurinsu wani abin da yafi ɗaure mishi kai da sun ganshi amma sun kasa barin abin da suke, ya ɗauki waya ya kira Hajiyar Zainab ya ce tazo yanzun nan ya fito ya ja musu ƙofa don takaici hawaye yana zubo mishi, to dama asirin in sun fara masha'arsu sai sun kai awa biyar sannan zasu dawo hankalinsu kuma shigar su kenan ya dawo don haka har Hajiya ta zo ya ce ta shiga ɗaki gashi nan zuwa, ta zata faɗa sukayi tana shiga ta samu saɓanin haka.