Sashe 4
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana zube gabanta kan kafet ya yin da take zaune kan kujera, gabanta sai faÉ—uwa yake yi saboda bata san dame ya zo ba. Kallonsa tayi yana bata tausayi dan tuni Dady ya mance da ake dariya,ko yanayi su dai ya daina musu.
Sannan ya zama miskilin gaske ga zafin rai da ya koya waɗannan halayen sama taka ya same su tun bayan da ya gama jinyar rashin Ruƙayya, sai dai har Yanzun yana basu girman su tare da musu biyayya.
Ganin bashi da niyyar magana yasa ta ce "Dady menene damuwarka? Ya dubeta idanunshi sun kada sunyi ja ya ce "Momy naga Pretty, Momy Ruƙayya na gani. Shin da gaske ne tayi aure kamar yanda kuka sanar da ni?.
Gaban Momy ya yi mummunan faɗuwa cikin tsoro ta ce "Haka magabatanta suka sanar damu." Ta cigaba "Ka nutsu Dady kaida gobe kamar yanzu ka zama Ango." Dubi yanda gidan nan ya cika da ƴan biki sannan ka zo min da labarin ka ga Ruƙayya me ganinta zaya amfana maka a halin yanzu?"
Ya yi wani murmushi irin na ɓacin ran nan ya girgiza kai shi kam yana mamakin yanda kowa ya kasa gane irin son da yake ma Pretty, ya furzar da wani huci mai zafi sannan ya ce.
"Momy aini nama manta da wani labarin zan yi aure, domin dama a rashin Pretty zan auri Zainab, kuma yanzu na ganta don haka har ga Allah na manta da wani batun aure.
Gaban Momy ya faÉ—i,dan tasan zaya iya fasawa don haka sai ta soma lallashinsa.
"Haba Dady yanzu, wannan girmanmu ne,ace wancan karon mu tara mutane abu bai yiwu ba, yanzu ma mu ƙara maimaita na da? Ka tuna burinmu muga ƴaƴanka shekarun mu sun tsawaita. Haba Dady ko so kake sai mun mutu sannan zaka yi?"
Hawaye suka zubo ma Momy abin da ko cikin mafarkin shi baya son gani,wato kukan Momy.
Da sauri ya isa gabanta
"Kimin afuwa Momyna." Ya sa hannu yana share mata hawayen, "Kada ki min haka Momy, abin zaya yi min yawa,ban sama kaina son Pretty ba daga Allah ne,nima na kasa control ɗin kai na ne, Momy ki fahimce ni." Ido ta zuba mishi gami da tausaya mishi, don haka sai ta ce "Dady kai namiji ne mijin mace huɗu,kana da izinin auran Zainab da Ruƙayya har ma da wasu biyu idan kana da buƙata. Yayi shiru na wasu lokuta sannan ya ce "Shikenan ku ci gaba da bikin ku." Ta ce "To amma nafi son ka ƙwantar da hankalinka kada ciwon ka ya tashi,ka bi komai a sannu har a gama wannan ko.? To kawai ya ce mata, ya miƙe ya nufi shashin daya gina wani tsatsaran plate mai ƙyau a cikin gidan nasu.
Kai tsaye bedroom ɗin shi ya nufa ya shige toilet duk da sanyin da garin ya ɗauka sakamakon ruwan saman da ake yi tun yammacin na yau,bai hana shi sakarwa kanshi ruwan sanyi ba sai da yaji sanyin yana ratsashi sannan ya fito mai ya shafa ya saka jeans baƙi da ƴar shirt sannan ya ɗauko wata rigar sanyi jibgegiya mai laushi ya saka yasa hularta. Har lokacin sanyi yake ji, zazzaɓi ne ya sani amma sai ya share ya tsani shan magani ya ɗauki key ɗin mota ya fito.
Yana ƙoƙarin shiga motar,motar Hussain tana shigowa, dole ya tsaya ya ƙaraso kasancewar har Yanzun ana ɗan yayyafi sai ya shiga gaban motar Hussain ɗaya gefen, suka yi hannu, Hussain ya ce Ango ya za'ayi ne? Ni ɗazun na kiraka muna ƙoƙarin tafiya sai kuma ka ce min kana hanyar zuwa Kaduna. Shi ne abin ya bani mamaki tunda nasan yau aƙwai wani program shi ne ka taho? Yanzun dai nace bari na zo naji goben sai mubi jirgi da wuri ko?"
Dady ya ɗan takure jikinshi saboda sanyi sannan ya ce "kune zaku tafi da su Saddiƙ saboda ni bana jin daɗi zan zo daga bayan ku,ku tafi da su Dad tunda suma jirgi zasu bi, amma fa sha biyu zasu tashi gidana zaku sauka Sunday yana nan munyi waya dashi zaku samu komai, sannan aƙwai Abokaina nacan su Sagir matansu zasuyi ma matanku tarba sosai,ba wata matsala ku cigaba da gabatar da komai kar ku damu da cewa sai nazo.
Hussain ya ce "Daka É—aure munje kada ita Zainab É—in ta zama cikin damuwa." Ya ce ,no ba damuwa zan mata waya yanzu ma gurin Dakta zan je,kaje gida ai zamu haÉ—u gobe É—in." Hussain ya ce "To bari na kaika sai na dawo da kai." Dady ya ce "a'a nan kusa muke ka tafi gidan shi zan je.
Hussain ya tafi sannan Dady ya É—auki mota ya fita.
Kai tsaye Kabala ya nufa bakin lungun su Ruƙayya nan ya tsaya. Saboda yayyafi ba yara don haka sai ya kashe motar sannan ya shiga lungun gidan,yana nan yanda yake sai dai ya samu canje-canje,wato ƴar kwaskwarima yana tsaye daf da ƙofar gidan yana jiyo ɗan motsi baisan ko na wanene ba,ya yanke hukuncin ya yi sallama.
Ruƙayya suna zaune da Umma taji gabanta ya faɗi domin tasan Dady ne,dama ƙarfin hali tayi dan kada su Umma su gane tana cikin damuwa,dan haka sai ta daure har suke hira tana ba Umma labarin Legos. Har sai da Affa ya shigo ta gaida shi suka ɗan yi hira kafin kiran magriba. Saboda ruwa tunda ya tafi sallar magriba bai dawo ba ko sun haɗa sallar ne ko kuma ya tsaya sai isha'i ne bata sani ba.
Umma ta dubeta kamar ana sallama ko? Ta ce naji ƙila gurin Affa aka zo,ta ce A'isha tana ɗaki tana sallah je ki tura ta taji,ɗakin ta nufa gurin A'isha ƴar gidan Yaya Sadiya tace je ki waje zakiga wani mutum in ya tambayi ki Affa kice baya nan.
Yana tsaye ta fito tai mishi sannu ya amsa da yauwa ƴan mata, ta ce kana neman Affa ne? Ya ce a'a Ruƙayya tana nan? Ta ce Eh, ya ce kirata ki ce tazo, ta gaya ma Ruƙayya Aunty wai ke ake nema, ta ce kije ki ce mata nayi bacci,ta zo tace tayi bacci, ya yi murmushi sannan ya ce ita tace kice tayi bacci? A'isha ta ce Eh, ya ce "To koma ki ce mata wai Dady ne yace zai jira ta har sanda zata tashi,tana gaya ma Ruƙayya, ta ce shegiya kin ce mishi ne ni nace ina bacci? Ta ce Eh, Ruƙayya ta kai mata duka maimakon ki ce a'a, A'isha ta ce ai na manta ne Aunty.
Zazzaɓi sosai ya rufe Dady amma yana jingine jikin gidan Affa dan ma an samu yayyafin ya yi sauƙi a haka Affa ya shigo lungun haska tocila lokacin kuma goma ta ɗan shige shima Affan sun tsaya sasanta wani aure ne ya ga mutum tsaye gashi ba wutar lantarki. Ya yi gyaran murya sannan ya ce "wanene?" Dady ya tsugunna ƙasa "Affa sannu da zuwa." Affa ya ce yauwa ban shaida ka ba fa." Dady ya ce nine Yusuf,kan Affa ya kuma ɗaurewa ya haska shi da tocila sannan ya ce Wane Yusuf fa? Dady ya ce "Baka gane ni ba Affa?" Affa ya ce "shigo dai muji."sun zauna sannan Affa ya gane shi cikin mamaki ya ce Yusufa ai wallahi ban shaida ka ba sam ganinka nayi kayi min ƙiba.
Dady ya yi murmushi sannan ya ɗan russuna yana gaida Affa, Affa ya ce ya bayan saduwa kuma Yusufa shiru? Dady ya ce tunda muka bar nan bani da isasshen lafiya waje aka fidda ni dana dawo kuma sai harkokina suka koma Abuja, yanzun can nake,ai na zazzo bana samun ka sai dai na bada saƙo gurin mai shagon can."
Affa cike da mamaki ya ce "Dama kai ne ke aiko min da saƙon nan?" Dady ya ce "Nine Affa." Affa ya ce "Madallah to ya iyalin kuma." Dady ya ce "To ana dai niyya." Affa ya ce kana nufin har yau bakayi aure ba?" Dady ya ce "Eh, to gobe ne dai ɗaurin auren." Ya ce "Allah sarki a ina ne? Dady ya ce ba anan bane can ne Abuja." Ya ce "to Allah yasa alkhairi. Yana son ya sako zancen Ruƙayya kuma ya kasa don bai san me Affa zai ce mishi ba.
Ba ya son ya ji Affa ya ce yayi haƙuri,don haka sai yayi shiru. Sun ɗan taɓa hira sannan Affa ya ce "naga kamar kana rawar sanyi." Dady ya ce bana jin daɗi ne, Affa ya ce to kaje kasha magani ka huta zama da ciwo babu amfani, to kawai ya ce amma can ƙasan ranshi yana cewa,ga maganin nan a gidan ka. Sun yi sallama akan zaya kuma zuwa kafin ya tafi.
Da ƙyar ya kai kanshi gida. Kai tsaye sashen sa ya wuce, cikin bargo ya ƙudundune haka ya ƙwana yana rawar sanyi.
Washegari Dad yaga basu haÉ—u sallar asubahi ba, kuma bai shigo ba, gidan cike da baki ya kira layin Dady tayi ringing har ta katse ba'a É—auka ba,kusan sau biyar yana kira,wayar tana falo yana jiyo kukanta amma ba zai iya tashi ba.
Dad ya juya ya kira layin Momy wacce dama tana kan hanyar shigowa, ta ƙaraso bedroom ɗin shi riƙe da wayar ta tana ringing ta ce gani ma dama nan zan shigo, ya ce wai ina Dady ne? Bamu yi sallah dashi ba yanzu har taƙwas tayi bai shigo ba.
Gaban Momy ya faɗi ta ce "Ina jin ƙila baya jin daɗi yana can sashin sa. Ta fita shima Dad ya ɗauko sandarsa ya nufo waje yana dogarawa ne saboda ciwon ƙafa dake damunsa.
Baƙin Yola dake ɗakin Momy suka fito suna gaida Dad sanda ya fito ya nufi sashin Dady tuni Momy ta kusan shiga, baya falon dan shi kanshi key ɗin shi gaya nan akan wani ɗan kucilin firji wanda sam saboda ƙanƙantar sa baiyi kama da firji ba,ta nufi bedroom ɗin shi,ta matuƙar tsorata da taga yana maƙyarkyata akan gado da sauri ta cire masa bargo tana masa sannu, ta ce haka ka ƙwana? Kai kawai ya ɗaga mata daidai nan Dad ya shigo,ganin jikin Dady yasa tsoro ya kama shi.
Sannan ya zama miskilin gaske ga zafin rai da ya koya waɗannan halayen sama taka ya same su tun bayan da ya gama jinyar rashin Ruƙayya, sai dai har Yanzun yana basu girman su tare da musu biyayya.
Ganin bashi da niyyar magana yasa ta ce "Dady menene damuwarka? Ya dubeta idanunshi sun kada sunyi ja ya ce "Momy naga Pretty, Momy Ruƙayya na gani. Shin da gaske ne tayi aure kamar yanda kuka sanar da ni?.
Gaban Momy ya yi mummunan faɗuwa cikin tsoro ta ce "Haka magabatanta suka sanar damu." Ta cigaba "Ka nutsu Dady kaida gobe kamar yanzu ka zama Ango." Dubi yanda gidan nan ya cika da ƴan biki sannan ka zo min da labarin ka ga Ruƙayya me ganinta zaya amfana maka a halin yanzu?"
Ya yi wani murmushi irin na ɓacin ran nan ya girgiza kai shi kam yana mamakin yanda kowa ya kasa gane irin son da yake ma Pretty, ya furzar da wani huci mai zafi sannan ya ce.
"Momy aini nama manta da wani labarin zan yi aure, domin dama a rashin Pretty zan auri Zainab, kuma yanzu na ganta don haka har ga Allah na manta da wani batun aure.
Gaban Momy ya faÉ—i,dan tasan zaya iya fasawa don haka sai ta soma lallashinsa.
"Haba Dady yanzu, wannan girmanmu ne,ace wancan karon mu tara mutane abu bai yiwu ba, yanzu ma mu ƙara maimaita na da? Ka tuna burinmu muga ƴaƴanka shekarun mu sun tsawaita. Haba Dady ko so kake sai mun mutu sannan zaka yi?"
Hawaye suka zubo ma Momy abin da ko cikin mafarkin shi baya son gani,wato kukan Momy.
Da sauri ya isa gabanta
"Kimin afuwa Momyna." Ya sa hannu yana share mata hawayen, "Kada ki min haka Momy, abin zaya yi min yawa,ban sama kaina son Pretty ba daga Allah ne,nima na kasa control ɗin kai na ne, Momy ki fahimce ni." Ido ta zuba mishi gami da tausaya mishi, don haka sai ta ce "Dady kai namiji ne mijin mace huɗu,kana da izinin auran Zainab da Ruƙayya har ma da wasu biyu idan kana da buƙata. Yayi shiru na wasu lokuta sannan ya ce "Shikenan ku ci gaba da bikin ku." Ta ce "To amma nafi son ka ƙwantar da hankalinka kada ciwon ka ya tashi,ka bi komai a sannu har a gama wannan ko.? To kawai ya ce mata, ya miƙe ya nufi shashin daya gina wani tsatsaran plate mai ƙyau a cikin gidan nasu.
Kai tsaye bedroom ɗin shi ya nufa ya shige toilet duk da sanyin da garin ya ɗauka sakamakon ruwan saman da ake yi tun yammacin na yau,bai hana shi sakarwa kanshi ruwan sanyi ba sai da yaji sanyin yana ratsashi sannan ya fito mai ya shafa ya saka jeans baƙi da ƴar shirt sannan ya ɗauko wata rigar sanyi jibgegiya mai laushi ya saka yasa hularta. Har lokacin sanyi yake ji, zazzaɓi ne ya sani amma sai ya share ya tsani shan magani ya ɗauki key ɗin mota ya fito.
Yana ƙoƙarin shiga motar,motar Hussain tana shigowa, dole ya tsaya ya ƙaraso kasancewar har Yanzun ana ɗan yayyafi sai ya shiga gaban motar Hussain ɗaya gefen, suka yi hannu, Hussain ya ce Ango ya za'ayi ne? Ni ɗazun na kiraka muna ƙoƙarin tafiya sai kuma ka ce min kana hanyar zuwa Kaduna. Shi ne abin ya bani mamaki tunda nasan yau aƙwai wani program shi ne ka taho? Yanzun dai nace bari na zo naji goben sai mubi jirgi da wuri ko?"
Dady ya ɗan takure jikinshi saboda sanyi sannan ya ce "kune zaku tafi da su Saddiƙ saboda ni bana jin daɗi zan zo daga bayan ku,ku tafi da su Dad tunda suma jirgi zasu bi, amma fa sha biyu zasu tashi gidana zaku sauka Sunday yana nan munyi waya dashi zaku samu komai, sannan aƙwai Abokaina nacan su Sagir matansu zasuyi ma matanku tarba sosai,ba wata matsala ku cigaba da gabatar da komai kar ku damu da cewa sai nazo.
Hussain ya ce "Daka É—aure munje kada ita Zainab É—in ta zama cikin damuwa." Ya ce ,no ba damuwa zan mata waya yanzu ma gurin Dakta zan je,kaje gida ai zamu haÉ—u gobe É—in." Hussain ya ce "To bari na kaika sai na dawo da kai." Dady ya ce "a'a nan kusa muke ka tafi gidan shi zan je.
Hussain ya tafi sannan Dady ya É—auki mota ya fita.
Kai tsaye Kabala ya nufa bakin lungun su Ruƙayya nan ya tsaya. Saboda yayyafi ba yara don haka sai ya kashe motar sannan ya shiga lungun gidan,yana nan yanda yake sai dai ya samu canje-canje,wato ƴar kwaskwarima yana tsaye daf da ƙofar gidan yana jiyo ɗan motsi baisan ko na wanene ba,ya yanke hukuncin ya yi sallama.
Ruƙayya suna zaune da Umma taji gabanta ya faɗi domin tasan Dady ne,dama ƙarfin hali tayi dan kada su Umma su gane tana cikin damuwa,dan haka sai ta daure har suke hira tana ba Umma labarin Legos. Har sai da Affa ya shigo ta gaida shi suka ɗan yi hira kafin kiran magriba. Saboda ruwa tunda ya tafi sallar magriba bai dawo ba ko sun haɗa sallar ne ko kuma ya tsaya sai isha'i ne bata sani ba.
Umma ta dubeta kamar ana sallama ko? Ta ce naji ƙila gurin Affa aka zo,ta ce A'isha tana ɗaki tana sallah je ki tura ta taji,ɗakin ta nufa gurin A'isha ƴar gidan Yaya Sadiya tace je ki waje zakiga wani mutum in ya tambayi ki Affa kice baya nan.
Yana tsaye ta fito tai mishi sannu ya amsa da yauwa ƴan mata, ta ce kana neman Affa ne? Ya ce a'a Ruƙayya tana nan? Ta ce Eh, ya ce kirata ki ce tazo, ta gaya ma Ruƙayya Aunty wai ke ake nema, ta ce kije ki ce mata nayi bacci,ta zo tace tayi bacci, ya yi murmushi sannan ya ce ita tace kice tayi bacci? A'isha ta ce Eh, ya ce "To koma ki ce mata wai Dady ne yace zai jira ta har sanda zata tashi,tana gaya ma Ruƙayya, ta ce shegiya kin ce mishi ne ni nace ina bacci? Ta ce Eh, Ruƙayya ta kai mata duka maimakon ki ce a'a, A'isha ta ce ai na manta ne Aunty.
Zazzaɓi sosai ya rufe Dady amma yana jingine jikin gidan Affa dan ma an samu yayyafin ya yi sauƙi a haka Affa ya shigo lungun haska tocila lokacin kuma goma ta ɗan shige shima Affan sun tsaya sasanta wani aure ne ya ga mutum tsaye gashi ba wutar lantarki. Ya yi gyaran murya sannan ya ce "wanene?" Dady ya tsugunna ƙasa "Affa sannu da zuwa." Affa ya ce yauwa ban shaida ka ba fa." Dady ya ce nine Yusuf,kan Affa ya kuma ɗaurewa ya haska shi da tocila sannan ya ce Wane Yusuf fa? Dady ya ce "Baka gane ni ba Affa?" Affa ya ce "shigo dai muji."sun zauna sannan Affa ya gane shi cikin mamaki ya ce Yusufa ai wallahi ban shaida ka ba sam ganinka nayi kayi min ƙiba.
Dady ya yi murmushi sannan ya ɗan russuna yana gaida Affa, Affa ya ce ya bayan saduwa kuma Yusufa shiru? Dady ya ce tunda muka bar nan bani da isasshen lafiya waje aka fidda ni dana dawo kuma sai harkokina suka koma Abuja, yanzun can nake,ai na zazzo bana samun ka sai dai na bada saƙo gurin mai shagon can."
Affa cike da mamaki ya ce "Dama kai ne ke aiko min da saƙon nan?" Dady ya ce "Nine Affa." Affa ya ce "Madallah to ya iyalin kuma." Dady ya ce "To ana dai niyya." Affa ya ce kana nufin har yau bakayi aure ba?" Dady ya ce "Eh, to gobe ne dai ɗaurin auren." Ya ce "Allah sarki a ina ne? Dady ya ce ba anan bane can ne Abuja." Ya ce "to Allah yasa alkhairi. Yana son ya sako zancen Ruƙayya kuma ya kasa don bai san me Affa zai ce mishi ba.
Ba ya son ya ji Affa ya ce yayi haƙuri,don haka sai yayi shiru. Sun ɗan taɓa hira sannan Affa ya ce "naga kamar kana rawar sanyi." Dady ya ce bana jin daɗi ne, Affa ya ce to kaje kasha magani ka huta zama da ciwo babu amfani, to kawai ya ce amma can ƙasan ranshi yana cewa,ga maganin nan a gidan ka. Sun yi sallama akan zaya kuma zuwa kafin ya tafi.
Da ƙyar ya kai kanshi gida. Kai tsaye sashen sa ya wuce, cikin bargo ya ƙudundune haka ya ƙwana yana rawar sanyi.
Washegari Dad yaga basu haÉ—u sallar asubahi ba, kuma bai shigo ba, gidan cike da baki ya kira layin Dady tayi ringing har ta katse ba'a É—auka ba,kusan sau biyar yana kira,wayar tana falo yana jiyo kukanta amma ba zai iya tashi ba.
Dad ya juya ya kira layin Momy wacce dama tana kan hanyar shigowa, ta ƙaraso bedroom ɗin shi riƙe da wayar ta tana ringing ta ce gani ma dama nan zan shigo, ya ce wai ina Dady ne? Bamu yi sallah dashi ba yanzu har taƙwas tayi bai shigo ba.
Gaban Momy ya faɗi ta ce "Ina jin ƙila baya jin daɗi yana can sashin sa. Ta fita shima Dad ya ɗauko sandarsa ya nufo waje yana dogarawa ne saboda ciwon ƙafa dake damunsa.
Baƙin Yola dake ɗakin Momy suka fito suna gaida Dad sanda ya fito ya nufi sashin Dady tuni Momy ta kusan shiga, baya falon dan shi kanshi key ɗin shi gaya nan akan wani ɗan kucilin firji wanda sam saboda ƙanƙantar sa baiyi kama da firji ba,ta nufi bedroom ɗin shi,ta matuƙar tsorata da taga yana maƙyarkyata akan gado da sauri ta cire masa bargo tana masa sannu, ta ce haka ka ƙwana? Kai kawai ya ɗaga mata daidai nan Dad ya shigo,ganin jikin Dady yasa tsoro ya kama shi.