Sashe 16
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dady ya dubi Zainab "ke wai bakida tunani ne kina nufin banida ikon yin yanda nike so da gidana, saboda kada ranki ya ɓaci? Ki maida hankalinki." Ya faɗa yana tafiya, ta ce Allah zai saka min, ya juyo yana dubanta ta nufi ɗakin ta, kalmar Allah zai saka mata ta zauna mishi a cikin rai ko dai gaske ne ya zalunce ta? Ya tuna ɗazunnan Ruƙayya ta dage tana mishi mita wai bai dace yaje da ita ba shi dama tafiyar nan fa ya ƙirƙireta ne don kanshi da kuma Pretty baiga amfanin tafiyar ba in har baije da ita ba. Wanka ya yi sannan yayi alwala kasancewar masallacin da tazara shiyasa sai yayi isha'i, bayan isha'in ne ya tara su dan yi musu ƙuri'a Zainab ya fara ba ta ɗauka sannan Pretty.
Hannu yana rawa Zainab ta buɗe cikin ikon Allah zaman gida ta samu nan ta soma hawaye kan cewa wannan wani munafunci ne aka haɗa don a ɓadda tunaninta, Ruƙayya ta ce Babyna na yarda ku tafi, ya ce ki min shiru ban yarda ba, ta tashi taje ta ɗauko biro da takarda tazo nan ta rubuta da taje har shaida tayi ma ɗayar sannan da tazo ta rubuta tafiya a mai shaidar ɗayar kuma ta rubuta zaman gida,ta ƙudundune ta zuba a ƙasa ya ce ta soma ɗauka,nan Allah ya nuna mata nashi ikon ta rasa mai shaidar ta ɗauki ɗaya sannan Ruƙayya ta ɗauki nata, Zainab ta katseshi da faɗin tab wallahi ban yarda ba.
A fusace Dady ya ce nima banason ki yarda ki ɗauki mataki kin ji ko? Ya miƙe yana faɗin banza mara hankalin kiyi abin da kanki son ranki a biye miki yanzu kice baki yarda ba, to kada ki yarda ɗin wawiya." Ya nufi gurin cin abinci.
Ranar dai ƙwana suka yi rigima har ta kaiga ya shashsheƙa mata mari, tare da buɗe ƙofarshi ya ce taje ɗakinta cikin daren bata bari gari ya waye ba ta kira Hajiyarta tana kuka tana gaya mata yanda abin ya kasance mata, Hajiya ta ce ƙyale shi su tafi. Insha Allah da rigima zasu dawo ko nawa zamu kashe ƴan iska zasu gane kurensu matsiyatan banza,in tana taƙamar asiri ne muma mun iya har gun tsafin da ake son kaini ina ƙi wannan karon zan je.
Zainab ta ce kije Hajiya wallahi na tsani in buɗe ido inga ƴar iskar matar nan baya gajiya da kallonta sai ka ce T.V,ko nauyi na baya ji gani gata amma bashida lokaci na. Wata ran ma in zai kirani da sunan da yake kiran ta fa zakiji ya kirani, Hajiya ta ce kada ki damu,zan gyara masa saiti,ki barsu su tafi ke dai ki tabbatar kin shaƙi kuɗi, ta ce ba wani abu.
*** *** ***
Tunda tayi sallah ta shiga shiri yanzu kam ƙal take jin ta ba wani zargin an ƙwari Zainab, yawancin kayan da suka siyo da M Bash shi ta ɗauka.
Ya shigo ya ce "bari in taya ki kema sai kije ki taya ni." Zainab kam tana ɗakinta har suka gama shiri Sunday shine ya fitar musu da kayan Dady ya kira wayar Zainab kamar ta share sai kuma ta ɗauka, ya ce ki fito zamu tafi, ta kashe kusan minti biyar ta fito, Ruƙayya ta dubeta cikin fara'a ta ce "Zainab zamu tafi." Ta dubeta ta ja tsaki "Dady gani." Ya ce zamu tafi ne, ta ce nan zakai min sallama saboda ni ba a bakin komai nike ba. To Allah ya kiyaye hanya ta wuce abin ta ta shige ɗakinta, ya ce Pretty muje kawai, Ruƙayya ta ce a'a kaje kuyi sallama ka bar mata komai, ya ce kinga check nan zan bata taƙi tsayawa,ki muje kawai ai na ajiye mata komai abinda babu ga Sunday nan sai ya amso mata dama ganin dama ne yasa zan bata kuɗin ba tsoro ba, komai da an mata ta ce an cuceta anyi meye meye?" Ruƙayya ta ce Haba don Allah kayi haƙuri kaje ka bata."
Ya nufi ɗakin fuska babu walwala, kuka ya sameta take yi ta kifa kanta, tausayinta yaji don haka ya isa gurinta ya kamota ya miƙar da ita ya rungume wani sabon kukan kissa ta saki yayi ta lallashi tare da bata check ɗin dubu ɗari ya ce in basu isheta ba zai sa a ƙara mata wasu cikin account ɗin ta. Ta yi ta janshi da ƴan wasanni dan dai ta nuna ma Ruƙayya itama yana yi da ita, ya ce to bari muje Zee, ta dama ka ƙosa ka tafi ne ko? Cikin shagwaɓa ya ce a'a Zee kece duk sanda muka zauna sai kin ja munyi rigima, ta shiga kissing ɗin shi a baki tana cewa in sun itama aje da ita, ya ce kar ki damu.
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/31, 19:10] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 8
Ruƙayya da taga shiru a ranta ta ce namiji sai a barshi,ta samu guri ta zauna ta ciro waya ta soma kiran Armaya'u, "Sadiya ƴan fatakol amaryar shitu," Sadiya ta ce ƴar gidan Dady ai na zaci ni baza'a kirani ai min sallama ba, jiya munyi waya da M Bash take ce min zaga duniya da bebyn naki." Ruƙayya ta ce lallai ma M Bash har ta gaya miki ina ce ma Dady beby?" Ta ce dole ne ta gaya min tunda mun kawo ki ne kina kukan bana son shi, sai kuma a jiki kin koma ce masa beby inye! Ƴar gidan bebynta." Ruƙayya ta ce ta naki ne? Zan haɗa ki da Shitu in ce yayi miki kishiya. Sadiya ta ce don ke kinada ita?.
Ruƙayya ta ce to yanzu dai sai mun dawo, ta ce ku dawo lafiya ki samo tsarabar Baby boy. Rukayya ta ce baki ce twins ba, ta kashe wayar, sannan ne suka fito tare da Zainab tana manne da jikinshi.
Ruƙayya ta miƙe tana faɗin "To Zainab sai mun dawo." Ta yatsina baki ta dubi Dady ta ce My dear sai ka dawo ka kular min da kanka, ya ce kada ki damu Zee nima ki kular min da kanki da gida,bana son yawo mara dalili ta ce dan wannan kada ka damu.
Ruƙayya dai tayi gaba kishi ko a mota sam taƙi sakin fuska sosai ya kula da haka sai abin ma ya soma bashi dariya, ita fa tace sai yaje ya ma Zee sallama, amma kuma sai ta kama shan kunu,ya raya tsokanar ta ya ɗauki wayarshi ya kira yarinyar dake nacin son shi kullum tayi ta damunshi da kira. Tasha mamakin kiran nashi dan bai taɓa kiranta ba, ringing ɗin farko ta ɗauka yace Aysha ƴanmatan gari, ta ce a'a ku ne masu gari Alhaji Yusuf,yau wace rana an kira ni? Ya ce tafiya zamuyi da amarya, shi ne nace bari in kira muyi sallama don kada ki kira waya kiji shiru kin san bana son haka.
Ruƙayya ta warce wayar ta kashe sannan ta tura a jakarta, ya dubeta "Pretty ya ya zaki min haka? Muna sallama da budurwa......." Wani kallo da ta watso mishi ne yasa ya yi shiru tamkar ya ƙwashe da dariya, amma ya dake ta ce tun kan muje airport tsaya in sauka."
Ya ce saboda me? Ta ce nidai na fasa zuwa kaje ku tafi da A'ishan ka da Zainab. Ya jawo ta haba Pretty na,ta ture shi kai na kula na mamajo ne sarkin mata, saura ta huÉ—u, ya ce haba kamar wani bazazzagi? Ta ce kaima gara ba zazzagen da kai,ni da gaske fa nike bazan je ba,ya bar dariyar da yake yi ganin da gaske take. Ya ce wasa nake miki Pretty kin san ke kaÉ—ai ce My Sweet one, My everlasting, My dear one,kin san Allah da in rasa ki a duniya,gara ace babu rayuwa ta.
Ta harareshi daɗin bakin namiji shi kake min,ya ce haba My Pretty kin san wuyan da nasha a kanki kuwa? Bayan ciwo da rashin ƙwanciyar hankali ga tsabar sha'awa da begen ki,bazan gaji da gaya miki sau uku ina zuwa aikin hajji inyi ɗawafi in rungume ka'aba ina kuka ina gaya ma Allah Ruƙayya, Ruƙayya. Ya ya zaya bani nayi wasa dake? Ranar da aka ɗaura min aure dake sai da nayi azumi uku dan nuna godiya ta ga maƙaginmu." Ya ɗan saurara sannan ya cigaba, "Yanzu burina na gaba inga kin cikamin gida da yara,don Allah tafiyar nan kar ki bari mu dawo baki bani Baby ba kin ji?" Ta ɗan kama kunnenshi ɗaya ta ɗan ja sannan ta ce "Allah zaka roƙa ya bamu masu albarka," ya ce kullum cikin roƙonshi nike sannan zan zage damtse a wannan tafiyar kema ki dage,inga kina ɗan aman nan na masu ciki,jaye fuska tayi tare da faɗin nidai babu ruwana.
***. **** ***
England suka fara yada zango cikin wani shahararren hotel.
Wai! Naso ace kuna nan a gurin ku ga soyayya da kanta, Tabbas Ruƙayya ta yarda beby ɗin ta ita kaɗai yake so Son ya manta da kowa da komai daga bautar Allah sai ta Pretty itace ta tuna mishi da abubuwan da ya dace ya yi kiran ƴan Nigeria zuwa ƴan kasuwancinshi,yau da suka cika sati biyu yakamata su bar ƙasar amma sai yaji baya son tafiya sai da suka ƙara ƙwana biyar.
*** *** ***
Rayuwarsu ta England ta tsaya mishi a rai ya rubuta cikin ƙundin tarihin sa, haka na Germany su kansu mutan ƙasar sunyi sha'awar su, kasancewar yana da abokan hulɗar kasuwancinshi sai dai ya ce wannan karon ba kasuwanci ya zo ba, don haka ko England bai nemi abokanshi ba, da gaske Dady shi kam ya dage sai ya samu beby, don haka ko yaushe suna garin majidaɗi gashi Pretty ɗin tashi ta shagwaɓar dashi ta ririta shi. Wani lokacin ma in ya matsa mata da maganar samun beby sai tace kaine bakada beby,nikam ina dashi ta jawo shi zo ma inyi feeding ɗin ka. Duk sunyi ƙyau har sun gaji Ruƙayya ga wasu hips sun zauna fata ta goge tayi shar, wani ƙyau kuma da shegen ƙwarjini sai ka dubi Dady.
Hannu yana rawa Zainab ta buɗe cikin ikon Allah zaman gida ta samu nan ta soma hawaye kan cewa wannan wani munafunci ne aka haɗa don a ɓadda tunaninta, Ruƙayya ta ce Babyna na yarda ku tafi, ya ce ki min shiru ban yarda ba, ta tashi taje ta ɗauko biro da takarda tazo nan ta rubuta da taje har shaida tayi ma ɗayar sannan da tazo ta rubuta tafiya a mai shaidar ɗayar kuma ta rubuta zaman gida,ta ƙudundune ta zuba a ƙasa ya ce ta soma ɗauka,nan Allah ya nuna mata nashi ikon ta rasa mai shaidar ta ɗauki ɗaya sannan Ruƙayya ta ɗauki nata, Zainab ta katseshi da faɗin tab wallahi ban yarda ba.
A fusace Dady ya ce nima banason ki yarda ki ɗauki mataki kin ji ko? Ya miƙe yana faɗin banza mara hankalin kiyi abin da kanki son ranki a biye miki yanzu kice baki yarda ba, to kada ki yarda ɗin wawiya." Ya nufi gurin cin abinci.
Ranar dai ƙwana suka yi rigima har ta kaiga ya shashsheƙa mata mari, tare da buɗe ƙofarshi ya ce taje ɗakinta cikin daren bata bari gari ya waye ba ta kira Hajiyarta tana kuka tana gaya mata yanda abin ya kasance mata, Hajiya ta ce ƙyale shi su tafi. Insha Allah da rigima zasu dawo ko nawa zamu kashe ƴan iska zasu gane kurensu matsiyatan banza,in tana taƙamar asiri ne muma mun iya har gun tsafin da ake son kaini ina ƙi wannan karon zan je.
Zainab ta ce kije Hajiya wallahi na tsani in buɗe ido inga ƴar iskar matar nan baya gajiya da kallonta sai ka ce T.V,ko nauyi na baya ji gani gata amma bashida lokaci na. Wata ran ma in zai kirani da sunan da yake kiran ta fa zakiji ya kirani, Hajiya ta ce kada ki damu,zan gyara masa saiti,ki barsu su tafi ke dai ki tabbatar kin shaƙi kuɗi, ta ce ba wani abu.
*** *** ***
Tunda tayi sallah ta shiga shiri yanzu kam ƙal take jin ta ba wani zargin an ƙwari Zainab, yawancin kayan da suka siyo da M Bash shi ta ɗauka.
Ya shigo ya ce "bari in taya ki kema sai kije ki taya ni." Zainab kam tana ɗakinta har suka gama shiri Sunday shine ya fitar musu da kayan Dady ya kira wayar Zainab kamar ta share sai kuma ta ɗauka, ya ce ki fito zamu tafi, ta kashe kusan minti biyar ta fito, Ruƙayya ta dubeta cikin fara'a ta ce "Zainab zamu tafi." Ta dubeta ta ja tsaki "Dady gani." Ya ce zamu tafi ne, ta ce nan zakai min sallama saboda ni ba a bakin komai nike ba. To Allah ya kiyaye hanya ta wuce abin ta ta shige ɗakinta, ya ce Pretty muje kawai, Ruƙayya ta ce a'a kaje kuyi sallama ka bar mata komai, ya ce kinga check nan zan bata taƙi tsayawa,ki muje kawai ai na ajiye mata komai abinda babu ga Sunday nan sai ya amso mata dama ganin dama ne yasa zan bata kuɗin ba tsoro ba, komai da an mata ta ce an cuceta anyi meye meye?" Ruƙayya ta ce Haba don Allah kayi haƙuri kaje ka bata."
Ya nufi ɗakin fuska babu walwala, kuka ya sameta take yi ta kifa kanta, tausayinta yaji don haka ya isa gurinta ya kamota ya miƙar da ita ya rungume wani sabon kukan kissa ta saki yayi ta lallashi tare da bata check ɗin dubu ɗari ya ce in basu isheta ba zai sa a ƙara mata wasu cikin account ɗin ta. Ta yi ta janshi da ƴan wasanni dan dai ta nuna ma Ruƙayya itama yana yi da ita, ya ce to bari muje Zee, ta dama ka ƙosa ka tafi ne ko? Cikin shagwaɓa ya ce a'a Zee kece duk sanda muka zauna sai kin ja munyi rigima, ta shiga kissing ɗin shi a baki tana cewa in sun itama aje da ita, ya ce kar ki damu.
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/31, 19:10] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 8
Ruƙayya da taga shiru a ranta ta ce namiji sai a barshi,ta samu guri ta zauna ta ciro waya ta soma kiran Armaya'u, "Sadiya ƴan fatakol amaryar shitu," Sadiya ta ce ƴar gidan Dady ai na zaci ni baza'a kirani ai min sallama ba, jiya munyi waya da M Bash take ce min zaga duniya da bebyn naki." Ruƙayya ta ce lallai ma M Bash har ta gaya miki ina ce ma Dady beby?" Ta ce dole ne ta gaya min tunda mun kawo ki ne kina kukan bana son shi, sai kuma a jiki kin koma ce masa beby inye! Ƴar gidan bebynta." Ruƙayya ta ce ta naki ne? Zan haɗa ki da Shitu in ce yayi miki kishiya. Sadiya ta ce don ke kinada ita?.
Ruƙayya ta ce to yanzu dai sai mun dawo, ta ce ku dawo lafiya ki samo tsarabar Baby boy. Rukayya ta ce baki ce twins ba, ta kashe wayar, sannan ne suka fito tare da Zainab tana manne da jikinshi.
Ruƙayya ta miƙe tana faɗin "To Zainab sai mun dawo." Ta yatsina baki ta dubi Dady ta ce My dear sai ka dawo ka kular min da kanka, ya ce kada ki damu Zee nima ki kular min da kanki da gida,bana son yawo mara dalili ta ce dan wannan kada ka damu.
Ruƙayya dai tayi gaba kishi ko a mota sam taƙi sakin fuska sosai ya kula da haka sai abin ma ya soma bashi dariya, ita fa tace sai yaje ya ma Zee sallama, amma kuma sai ta kama shan kunu,ya raya tsokanar ta ya ɗauki wayarshi ya kira yarinyar dake nacin son shi kullum tayi ta damunshi da kira. Tasha mamakin kiran nashi dan bai taɓa kiranta ba, ringing ɗin farko ta ɗauka yace Aysha ƴanmatan gari, ta ce a'a ku ne masu gari Alhaji Yusuf,yau wace rana an kira ni? Ya ce tafiya zamuyi da amarya, shi ne nace bari in kira muyi sallama don kada ki kira waya kiji shiru kin san bana son haka.
Ruƙayya ta warce wayar ta kashe sannan ta tura a jakarta, ya dubeta "Pretty ya ya zaki min haka? Muna sallama da budurwa......." Wani kallo da ta watso mishi ne yasa ya yi shiru tamkar ya ƙwashe da dariya, amma ya dake ta ce tun kan muje airport tsaya in sauka."
Ya ce saboda me? Ta ce nidai na fasa zuwa kaje ku tafi da A'ishan ka da Zainab. Ya jawo ta haba Pretty na,ta ture shi kai na kula na mamajo ne sarkin mata, saura ta huÉ—u, ya ce haba kamar wani bazazzagi? Ta ce kaima gara ba zazzagen da kai,ni da gaske fa nike bazan je ba,ya bar dariyar da yake yi ganin da gaske take. Ya ce wasa nake miki Pretty kin san ke kaÉ—ai ce My Sweet one, My everlasting, My dear one,kin san Allah da in rasa ki a duniya,gara ace babu rayuwa ta.
Ta harareshi daɗin bakin namiji shi kake min,ya ce haba My Pretty kin san wuyan da nasha a kanki kuwa? Bayan ciwo da rashin ƙwanciyar hankali ga tsabar sha'awa da begen ki,bazan gaji da gaya miki sau uku ina zuwa aikin hajji inyi ɗawafi in rungume ka'aba ina kuka ina gaya ma Allah Ruƙayya, Ruƙayya. Ya ya zaya bani nayi wasa dake? Ranar da aka ɗaura min aure dake sai da nayi azumi uku dan nuna godiya ta ga maƙaginmu." Ya ɗan saurara sannan ya cigaba, "Yanzu burina na gaba inga kin cikamin gida da yara,don Allah tafiyar nan kar ki bari mu dawo baki bani Baby ba kin ji?" Ta ɗan kama kunnenshi ɗaya ta ɗan ja sannan ta ce "Allah zaka roƙa ya bamu masu albarka," ya ce kullum cikin roƙonshi nike sannan zan zage damtse a wannan tafiyar kema ki dage,inga kina ɗan aman nan na masu ciki,jaye fuska tayi tare da faɗin nidai babu ruwana.
***. **** ***
England suka fara yada zango cikin wani shahararren hotel.
Wai! Naso ace kuna nan a gurin ku ga soyayya da kanta, Tabbas Ruƙayya ta yarda beby ɗin ta ita kaɗai yake so Son ya manta da kowa da komai daga bautar Allah sai ta Pretty itace ta tuna mishi da abubuwan da ya dace ya yi kiran ƴan Nigeria zuwa ƴan kasuwancinshi,yau da suka cika sati biyu yakamata su bar ƙasar amma sai yaji baya son tafiya sai da suka ƙara ƙwana biyar.
*** *** ***
Rayuwarsu ta England ta tsaya mishi a rai ya rubuta cikin ƙundin tarihin sa, haka na Germany su kansu mutan ƙasar sunyi sha'awar su, kasancewar yana da abokan hulɗar kasuwancinshi sai dai ya ce wannan karon ba kasuwanci ya zo ba, don haka ko England bai nemi abokanshi ba, da gaske Dady shi kam ya dage sai ya samu beby, don haka ko yaushe suna garin majidaɗi gashi Pretty ɗin tashi ta shagwaɓar dashi ta ririta shi. Wani lokacin ma in ya matsa mata da maganar samun beby sai tace kaine bakada beby,nikam ina dashi ta jawo shi zo ma inyi feeding ɗin ka. Duk sunyi ƙyau har sun gaji Ruƙayya ga wasu hips sun zauna fata ta goge tayi shar, wani ƙyau kuma da shegen ƙwarjini sai ka dubi Dady.