Sashe 7
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saude tana ƙofar kicin kusa da ita wata ƴar matashiyar yarinya ce tana wanke-wanke ya ce "Saude ina ƙwana?" Ta ce lafiya lau uban masu gida yaya amarya? Ya ce lafiya ina uwar gidana? Ta ce tana ciki ai zata ka daina yi damu, ya yi murmushi ya ce da tsohuwar zuma ake magani Ni na isa in yar da Hajja? Ya faɗa daidai lokacin da yake ƙoƙarin shiga falon Hajja, tana zaune kan kujera tana kallon T.V ya yi murmushi sannan ya ce Hajja sarkin kallon T.V ga kuma wannan uban gilashin. Ya ce me kike kallo ne? Ta ce Oho ga dai shi nan Ni ba jin abin da suke faɗa ni keyi ba ina dai binsu da ido, ya yi murmushi ya ce ina ƙwana an tashi lafiya,? Ta ce lafiya lau, ya kishiya ba haushi? Ya dubeta ban gane wa kenan ba? Ta ba haushi nake tambaya,kan Dady ya ɗaure ya ce nifa ban san ta ba, Hajja ta na dariya tace kai dai turawa sun gama dakai komai na Hausa baka san shi ba,to ina amarsu ta ango, ya ce Oh Zainab tana gida ni naji kin kirata da wani suna.
Ta yi murmushi ta ce ba dai kazo karyawa bane? Dan mun cireka a gandu, ya ce ni da wani albishir ma nazo miki, ta ce name? Ya gyara zama na wani auran, ya yi maganar fuska ba wasa,hakan ya sa ta cire gilashin idonta ta tsura mishi ido ta ce ka fahimtar dani kaine zaka ƙara auran ko wa? Da gadara ya ce ni ne nan,kinsan wadda zan aura? Ya ce Pretty.......
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/2, 21:24] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 4
An kuma bani ita a karo na biyu kuma insha Allah ranar sati za'a É—aura mana aure.
Ta harareshi kai amma bakada kai duk yaushe kayi auren ko sati ɗaya ba'a yi ba sannan ka soma zancan wani auran? Ya ce Hajja koda mata huɗu na aura a wancan satin aka ce ga Ruƙayya sai na saki ɗaya na aureta,ke ko yanzun da ba'a ɗaura da Zainab ba ko ranar ɗaurin auren ne wallahi fasawa zanyi dan dai sanda na ganta banida tabbacin ko tana da aure ko bata dashi,kar in fasa ya zama tanada aure. Hajja ta ce yaushe ka ganta kuma wayace maka batada aure? Ya yi murmushi ya ce ƙarewar rashin aure ma an bani ita,yau su Dad zasu je gurin Affa a gama komai nan ya koro mata labarin tun daga farko har zuwa yanzun daya je gurin Affa. Hajja ta yi fatan alheri tare da roƙon shi kan ya lallashi Zainab dan kishiya aƙwai ciwo, kayi adalci, ya ce insha Allah.
Kula aka ci mai da waina dan ya kaima Zainab,a phone ya kira Dad ya sanar dashi yanda sukayi da Affa,kai tsaye sashen shi ya nufa ƙwance kan kujera ya samu Zainab Sam bata san ya shiga ba, ya tsaya kanta sai faman hawaye take zubarwa tausayinta ne ya ɗarsu a ranshi,a hankali ya ajiye kular sannan ya isa gurinta ya tsugunna ya ce Zee a cikin taushin murya, da kiranta ta juyo ta dubeshi, shima ya dubeta suka yi wa juna murmushi.
"Haba Zainab menene haka? Kina son ki ganni cikin tashin hankali ne? Ta fashe da kuka, Dady dubi fa da wayewar gari har ka tafi gurin wata kayo break,ba abin da ke ɓata min rai ace ko one week ba'ayi da auranmu ba har zakayi wani Please ka duba fa." Shiru Dady ya yi jin tatsuniyar ta a ranshi ya ce in ma kina tunanin zan fasa gara kin bari, amma a fili sai ya ce hakanan ki zauna kina kuka ƙila ma baki karya ba, hannunshi yasa ya share mata hawaye ya miƙe ina zuwa ya ce mata sannan ya nufi kitchen ya ɗauko plate waina ya zuba mata a baki yake bata tana zuba shagwaɓa ta ce ya yi mata wanka, ya ce to yanda kika ce ai haka za'ayi soyayya aka tsaya yi a bayin kafin daga bisani ya yi mata wankan sannan shima ya yi.
*** *** ***
Su Affa sun tarbi su Dad hannu biyu shagon gidan maƙwafcin Affa nan suka shiga tarihi ne ya maimaita kan shi wato inda aka taɓa karɓar sadakin na Ruƙayya yau ma gasu nan. Bayan gaishe-gaishe sai kuma ban haƙuri ya biyo baya inda Dad yake ƙara ba Affa haƙuri game da FIN ƘARFIN da aka mishi ya nuna cewa ba laifin shi bane laifin Alhaji Jega ne, yanzu haka sun daɗe da yin hannun riga da Jegan sakamakon cutar da ya yi mishi har ta Naira miliyan talatin da biyar ya cigaba da cewa filin nan na farko da na soma amsa gurin mahaifinku gwamnati ta bani,to sun saidashi miliyan arba'in da biyar. Sai ya kawo min miliyan goma wai haka aka saida, yanzun ma nakun ma na maida muku kayan ku,zamu sa lokaci muje in maida muku abin ku cikin bainar jama'a.
Affa ya ce dama ka barshi Alhaji." Dad ya ce "a'a aiko da, ɗin bansan cewa FIN ƘARFI ya yi maku ba, wallahi da bazan shiga abin ba.
Sannan suka koma ga batun yara inda Dad ke cewa Malam Sani Allah dai ya rubuta Ruƙayya dai My Son shine mijinta, Affa ya ce komai ai na Allah ne, abokin Dad ya ce tun ran gini ran zane inji masu hikima, abokan Affa biyu suka ce haka ne.
Dad ya ce sai muje batun sadaki ko? Affa ya ce Naira dubu goma shi ne sadakin dana yanke mata. Dad ya dubi abokinshi ya ce kaji fa Alhaji Bukar lau ƴa ce fa sukutum wai dubu goma, sukayi ƴar dariya sannan Affa ya ce ƙarancin sadaki shine mafi albarka Dad ya ce hakane sai dai har ga Allah naji babu yawa kace dai Allah ya sanya alkhairi kawai muke so,ai naji daɗi sosai ko batun aikin ta dama mu ma muna buƙatar lauya a campanyn Dady ɗin nan Kaduna da na Abuja shi kenan riba biyu, suka yi dariya, Affa ya ce haka ne gida bai ƙoshi ba ai ba'a kaima wasu ba, suka ce hakane.
Dad ya ce to batun rana fa yaushe ne ɗaurin auren? Affa ya ce wannan kuma Yusufa ne mai ajewa dama haka na sanar dashi, Dad ya ce bari na kirashi, daidai lokacin Dady yana ƙwance kan doguwar kujera Zainab tana zaune kan kafet amma ta jingina da jikin kujerar da Dady ke kai,kanta ma yana gefen ƙirjin Dady remote ne a hannunta ta kamo wata channel da ake film ɗin batsa, Dady ya ce No canza mana banason wannan channel ɗin ta ce "haba My dear daga ni sai kai fa,ka bari mu kalla." Ya ce a'a bana cikin masu kallon haramun, wannan haramun ne mutum ya kalli tsiraicin wani, don haka kamo min MBC Action ta soma searching cikin zunɓura baki, wayarshi ta soma ruri,da sauri ya ɗauka don yaji ringing ɗin daya sama Dad ɗin shi ne, ya ce Hello Dad,nan gefen kuma Dad ya ce yauwa munzo da yaushe kake son a ɗaura auran? Dady ya ce Dad wannan Saturday ɗin nake so." Dad ya ce My Son bazaka bari sai week na sama ba? Sannan an buga I.V, Dady ya ce ai Dad bar zancen I.V ko ana gobe za'a ɗaura aure muna da masu buga cart,bana son na kuma rasata ya ɗan kalli sashen da Zainab take, sai ya miƙe ya fita yana cewa Dad kaji? Ya ce shikenan.
Take a nan Dady ya yi sujjada yana mai godiya ga Allah gefen su Momy ya shiga dan sanar da ita, itama tayi farin ciki tare da yi mishi nasiha game da mata biyu, sannan ta ce Ruƙayyan yanzun ta sani? Ya ce a'a bata sani ba zan dai je gidan su a bani number ɗin ta da kuma adireshin gurin da take, Momy ta ce kai Babana burin ya cika, ya ce Momy ai Allah baya bacci, zuwa na hajji sau uku banda Ruƙayya babu abinda nike roƙa gurin Ubangiji sai gashi ya amsa min ya bani ita a lokacin da na soma ɗebe tsammanin samunta, wata ƴar ƙwalla ta taru mishi gefen ido, Momy tausayin ɗan nata ya kamata don haka yana fita alwala ta ɗaura don nuna godiyar ta gurin Ubangiji ta kuma roƙa mishi zaman lafiya, Allah ya kuma kare shi. Shirye-shiryen biki ya kan kama,ana jibi ɗaurin aure abokan Dady da abokan kasuwancin shi dake ƙasashe daban-daban suka soma zuwa, waɗanda basu sami zuwa wancan ba, wasu kuma sai mamaki suke yi me yasa Dady aure biyu? Ya dawo daga masaukin baƙi inda ya sauke su a Darba Hotel. Bayan ganin sun samu komai ya nufi gida yau kam sai ya ji muryar Pretty.
Sai da ya yi shirin bacci sannan ya soma neman layin ta, lokacin tana tsaka da karatun wani Nobel don ɗebe mata kewar damuwar da take ciki ta rasa kullum cikin faɗuwar gaba take a ƴan ƙwanakinnan Nuri ya kan ce mata ta yawaita addu'a sai tace ita dai tana ganin gida kamar ba lafiya. Ta kira su Murja da Fati duk sun ce mata kowa lafiya,to me yasa ranta be mata daɗi?.
Wayarta ta soma ringing takai hannu ta ɗauka,baƙuwar lamba ta gani mamaki ya kamata,dan ba kowa yasan ta da waya ba, ta ɗauka tare da faɗin.
"Salamu alaikum."
Ya Salam! Ita ce kalmar da Dady yaso furtawa ta ce wa yake magana? Ya ce Dady ne Pretty,nan da nan gabanta ya faɗi tayi shiru ta kasa magana, ya ce kinyi murna da jina? Wani irin baƙin ciki taji da ta tuna wai Dadynta. Daya ganta ya yi banza da ita? Dady da ya karya alƙawarinta? Dadyn da yazo har gidan su don gaya mata auran shi? Sai taja tsaki ta kashe, ya kuma kira taƙi ɗauka ya yi ya gaji amma bai daina ba,da ta gaji sai ta kashe wayar gaba ɗaya.
Ta yi murmushi ta ce ba dai kazo karyawa bane? Dan mun cireka a gandu, ya ce ni da wani albishir ma nazo miki, ta ce name? Ya gyara zama na wani auran, ya yi maganar fuska ba wasa,hakan ya sa ta cire gilashin idonta ta tsura mishi ido ta ce ka fahimtar dani kaine zaka ƙara auran ko wa? Da gadara ya ce ni ne nan,kinsan wadda zan aura? Ya ce Pretty.......
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/2, 21:24] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 4
An kuma bani ita a karo na biyu kuma insha Allah ranar sati za'a É—aura mana aure.
Ta harareshi kai amma bakada kai duk yaushe kayi auren ko sati ɗaya ba'a yi ba sannan ka soma zancan wani auran? Ya ce Hajja koda mata huɗu na aura a wancan satin aka ce ga Ruƙayya sai na saki ɗaya na aureta,ke ko yanzun da ba'a ɗaura da Zainab ba ko ranar ɗaurin auren ne wallahi fasawa zanyi dan dai sanda na ganta banida tabbacin ko tana da aure ko bata dashi,kar in fasa ya zama tanada aure. Hajja ta ce yaushe ka ganta kuma wayace maka batada aure? Ya yi murmushi ya ce ƙarewar rashin aure ma an bani ita,yau su Dad zasu je gurin Affa a gama komai nan ya koro mata labarin tun daga farko har zuwa yanzun daya je gurin Affa. Hajja ta yi fatan alheri tare da roƙon shi kan ya lallashi Zainab dan kishiya aƙwai ciwo, kayi adalci, ya ce insha Allah.
Kula aka ci mai da waina dan ya kaima Zainab,a phone ya kira Dad ya sanar dashi yanda sukayi da Affa,kai tsaye sashen shi ya nufa ƙwance kan kujera ya samu Zainab Sam bata san ya shiga ba, ya tsaya kanta sai faman hawaye take zubarwa tausayinta ne ya ɗarsu a ranshi,a hankali ya ajiye kular sannan ya isa gurinta ya tsugunna ya ce Zee a cikin taushin murya, da kiranta ta juyo ta dubeshi, shima ya dubeta suka yi wa juna murmushi.
"Haba Zainab menene haka? Kina son ki ganni cikin tashin hankali ne? Ta fashe da kuka, Dady dubi fa da wayewar gari har ka tafi gurin wata kayo break,ba abin da ke ɓata min rai ace ko one week ba'ayi da auranmu ba har zakayi wani Please ka duba fa." Shiru Dady ya yi jin tatsuniyar ta a ranshi ya ce in ma kina tunanin zan fasa gara kin bari, amma a fili sai ya ce hakanan ki zauna kina kuka ƙila ma baki karya ba, hannunshi yasa ya share mata hawaye ya miƙe ina zuwa ya ce mata sannan ya nufi kitchen ya ɗauko plate waina ya zuba mata a baki yake bata tana zuba shagwaɓa ta ce ya yi mata wanka, ya ce to yanda kika ce ai haka za'ayi soyayya aka tsaya yi a bayin kafin daga bisani ya yi mata wankan sannan shima ya yi.
*** *** ***
Su Affa sun tarbi su Dad hannu biyu shagon gidan maƙwafcin Affa nan suka shiga tarihi ne ya maimaita kan shi wato inda aka taɓa karɓar sadakin na Ruƙayya yau ma gasu nan. Bayan gaishe-gaishe sai kuma ban haƙuri ya biyo baya inda Dad yake ƙara ba Affa haƙuri game da FIN ƘARFIN da aka mishi ya nuna cewa ba laifin shi bane laifin Alhaji Jega ne, yanzu haka sun daɗe da yin hannun riga da Jegan sakamakon cutar da ya yi mishi har ta Naira miliyan talatin da biyar ya cigaba da cewa filin nan na farko da na soma amsa gurin mahaifinku gwamnati ta bani,to sun saidashi miliyan arba'in da biyar. Sai ya kawo min miliyan goma wai haka aka saida, yanzun ma nakun ma na maida muku kayan ku,zamu sa lokaci muje in maida muku abin ku cikin bainar jama'a.
Affa ya ce dama ka barshi Alhaji." Dad ya ce "a'a aiko da, ɗin bansan cewa FIN ƘARFI ya yi maku ba, wallahi da bazan shiga abin ba.
Sannan suka koma ga batun yara inda Dad ke cewa Malam Sani Allah dai ya rubuta Ruƙayya dai My Son shine mijinta, Affa ya ce komai ai na Allah ne, abokin Dad ya ce tun ran gini ran zane inji masu hikima, abokan Affa biyu suka ce haka ne.
Dad ya ce sai muje batun sadaki ko? Affa ya ce Naira dubu goma shi ne sadakin dana yanke mata. Dad ya dubi abokinshi ya ce kaji fa Alhaji Bukar lau ƴa ce fa sukutum wai dubu goma, sukayi ƴar dariya sannan Affa ya ce ƙarancin sadaki shine mafi albarka Dad ya ce hakane sai dai har ga Allah naji babu yawa kace dai Allah ya sanya alkhairi kawai muke so,ai naji daɗi sosai ko batun aikin ta dama mu ma muna buƙatar lauya a campanyn Dady ɗin nan Kaduna da na Abuja shi kenan riba biyu, suka yi dariya, Affa ya ce haka ne gida bai ƙoshi ba ai ba'a kaima wasu ba, suka ce hakane.
Dad ya ce to batun rana fa yaushe ne ɗaurin auren? Affa ya ce wannan kuma Yusufa ne mai ajewa dama haka na sanar dashi, Dad ya ce bari na kirashi, daidai lokacin Dady yana ƙwance kan doguwar kujera Zainab tana zaune kan kafet amma ta jingina da jikin kujerar da Dady ke kai,kanta ma yana gefen ƙirjin Dady remote ne a hannunta ta kamo wata channel da ake film ɗin batsa, Dady ya ce No canza mana banason wannan channel ɗin ta ce "haba My dear daga ni sai kai fa,ka bari mu kalla." Ya ce a'a bana cikin masu kallon haramun, wannan haramun ne mutum ya kalli tsiraicin wani, don haka kamo min MBC Action ta soma searching cikin zunɓura baki, wayarshi ta soma ruri,da sauri ya ɗauka don yaji ringing ɗin daya sama Dad ɗin shi ne, ya ce Hello Dad,nan gefen kuma Dad ya ce yauwa munzo da yaushe kake son a ɗaura auran? Dady ya ce Dad wannan Saturday ɗin nake so." Dad ya ce My Son bazaka bari sai week na sama ba? Sannan an buga I.V, Dady ya ce ai Dad bar zancen I.V ko ana gobe za'a ɗaura aure muna da masu buga cart,bana son na kuma rasata ya ɗan kalli sashen da Zainab take, sai ya miƙe ya fita yana cewa Dad kaji? Ya ce shikenan.
Take a nan Dady ya yi sujjada yana mai godiya ga Allah gefen su Momy ya shiga dan sanar da ita, itama tayi farin ciki tare da yi mishi nasiha game da mata biyu, sannan ta ce Ruƙayyan yanzun ta sani? Ya ce a'a bata sani ba zan dai je gidan su a bani number ɗin ta da kuma adireshin gurin da take, Momy ta ce kai Babana burin ya cika, ya ce Momy ai Allah baya bacci, zuwa na hajji sau uku banda Ruƙayya babu abinda nike roƙa gurin Ubangiji sai gashi ya amsa min ya bani ita a lokacin da na soma ɗebe tsammanin samunta, wata ƴar ƙwalla ta taru mishi gefen ido, Momy tausayin ɗan nata ya kamata don haka yana fita alwala ta ɗaura don nuna godiyar ta gurin Ubangiji ta kuma roƙa mishi zaman lafiya, Allah ya kuma kare shi. Shirye-shiryen biki ya kan kama,ana jibi ɗaurin aure abokan Dady da abokan kasuwancin shi dake ƙasashe daban-daban suka soma zuwa, waɗanda basu sami zuwa wancan ba, wasu kuma sai mamaki suke yi me yasa Dady aure biyu? Ya dawo daga masaukin baƙi inda ya sauke su a Darba Hotel. Bayan ganin sun samu komai ya nufi gida yau kam sai ya ji muryar Pretty.
Sai da ya yi shirin bacci sannan ya soma neman layin ta, lokacin tana tsaka da karatun wani Nobel don ɗebe mata kewar damuwar da take ciki ta rasa kullum cikin faɗuwar gaba take a ƴan ƙwanakinnan Nuri ya kan ce mata ta yawaita addu'a sai tace ita dai tana ganin gida kamar ba lafiya. Ta kira su Murja da Fati duk sun ce mata kowa lafiya,to me yasa ranta be mata daɗi?.
Wayarta ta soma ringing takai hannu ta ɗauka,baƙuwar lamba ta gani mamaki ya kamata,dan ba kowa yasan ta da waya ba, ta ɗauka tare da faɗin.
"Salamu alaikum."
Ya Salam! Ita ce kalmar da Dady yaso furtawa ta ce wa yake magana? Ya ce Dady ne Pretty,nan da nan gabanta ya faɗi tayi shiru ta kasa magana, ya ce kinyi murna da jina? Wani irin baƙin ciki taji da ta tuna wai Dadynta. Daya ganta ya yi banza da ita? Dady da ya karya alƙawarinta? Dadyn da yazo har gidan su don gaya mata auran shi? Sai taja tsaki ta kashe, ya kuma kira taƙi ɗauka ya yi ya gaji amma bai daina ba,da ta gaji sai ta kashe wayar gaba ɗaya.