Sashe 12
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin sun soma nisa a hanyar ƙaramar hukumar majidaɗi shi da Zainab, waya ta soma ringing cikin kasala ya ɗauka yasa a kunne Hello Pretty?" Yanda taji Muryar shi sai da gabanta ya faɗi ba ko shakka yana tare da Zainab. Ta daure ta ce dama zamu je ibadan ne. Zainab ko tana jin ya ce Pretty ta shiga aika mishi da saƙwanni waɗanda suka sa shi ya kasa magana sai yace zan kira ki anjima, yanda taji muryar shi ma ta isa tasan cewa sunje majidaɗi ne,in ranta ya yi dubu duk sun ɓaci tayi data sanin kiranshi yafi a ƙirga. Daya sani bai ɗauka ba zai fi mata takaicin wannan abun da taji,awa ɗaya tana kuka can wayar ta soma ringing number ɗin shi ne kamar kada ta ɗauka, sai kuma tasa hannu ta ɗauka Muryar mace taji tana cewa "Hello Ruƙayya ke ce kuwa? Menene dallah na kira min miji muna cikin raya sunnah,bana son shiga rayuwar ki ba,ki bari sai kin samu ya yarda ki tare sannan sai ki dinga wannan shishshigin yanzu barni da mijina mu wala, Ruƙayya ta koma ta ƙwanta tare da sa sabon kuka.
*** *** ***
Dady ya fito daga wanka duk komai ya yi na samun natsuwa, amma duk hankalinshi yana gurin Pretty tunda bata taɓa kiranshi ba tun da ta tafi Legos, sai dai shi ya kira ta.
Ya zauna bakin gado ya dubi Zainab ya ce je kiyi wanka. Sannan ya ɗauki waya ya fara kiran Pretty tayi ta ringing tana katsewa, kamar bazata dauka ba sai kuma ta ɗauka tayi zaton ko Zainab ɗin ce ta maida mata martani, sai taji shi ya ce Prettyna takaici ne ya kamata a ranta ta ce namiji munafiki, ya ce kin kira ni ɗazun bana jin ki network kin ana matsalar shi ƙwanan nan, ta kayi haƙuri na kira lokacin da bai dace ba,ka ba matarka haƙuri ka ce banyi da nufi ba kamar yanda ta zata sai ta kashe wayar ta gaba ɗaya ma ta ƙwanta,ya zauna yana ta fassara maganar duk yanda akayi Zainab ta kirata ya shiga dialled calls yaga kam an kirata, Zainab ta fito ya dubeta me kika ce ma Pretty da kika kirata? Ta ce ni ban kirata ba ita ce ta kira kuma na shaida mata bana son haka,ban da rainin wayo sai ta kiraka muna tare?"
Haushi ya ƙara kama shi ya ce "kin san wacece Pretty? Duk ya ruɗe ya ce wallahi sai naci mutuncin ki,yarinyar da nike lallaɓawa shine dan kuturun wulaƙanci zaki ɓallo min Niger. Don yanzu ban san ta inda zan fara ba na samu na fara shawo kanta, ya ɗau wayar ya kuma kira a kashe take. Zainab dai sai da tayi data sanin bata kira Ruƙayya ba, domin ko bacci Dady bai yi ba itama faɗan da yake mata ya hana ta runtsawa asubar fari ya soma shiri.
*** *** ***
Ta dubi Salimat ta ce,don Allah in kun je kice ina gaida Sulafat,bana jin daɗi jiya da zazzaɓi na ƙwana,Salimat ta ce zan gaya mata, Nuri ya shigo ya ya dai amarya? Ance bazaki samu zuwa ba, ta ce Eh, Nuri ku gaida min ita, Salimat wata ƴar sabis ɗin su ce da tayi haɗarin mota hanyar ta ta zuwa gida ranar Lahadi, shine zasu je dubata a Ibadan, sakamakon abin da ya faru shine Ruƙayya bata samu iznin zuwa ba gashi ta ƙwana ba lafiya.
Bacci ya soma ɗaukarta ta ji magana a kanta shugaban su ne da kanshi yake sanar da ita tayi baƙo. Kan ta ce wani abu Dady ya shigo sam bata son ganin shi don sai take jin kamar a gaban ta suke jiyannan. Ta runtse ido ya shigo ya zauna kusa da ita.
"Pretty tashi tashi ki jini." Ta ce cikin kuka "me zan ji? Bakada sauran abin da zaka gaya min,baka dashi Dady na jima da sanin halin maza,kai kana cikin maza masu cin amana da yaudara ga karya alƙawari." Ya dubeta ta kauda kai ta ce"na tsane ka." Ya ce ban ci amanar ki ba ban yaudare ki ba,kin ƙi bani dama na nuna miki son da nake miki nasha wuya a kanki ina sonki.
Ta toshe kunne.
"Daina gaya min ƙarya,bana son ji,bana son ji." Ta faɗi tana kuka sosai,ya rasa me zai mata ya ce to yanzu tashi ki faɗi min hukuncina, laifi dai ko wane iri ne na ɗauka,ya duka saitin fuskarta yana shirin haɗa bakinta da nashi,ta tashi tana kare bakinta cikin kuka take maganar kaje ka sha bakin wata sannan kazo ka daɓa min na ce kaje na bar mata kawai ka sake ni....." Ya rufe bakinta da tafin hannu.
Ya ce "Babu wannan maganar a tsakanin mu." Kuka tayi ta mishi ya durƙusa gwiwa bibbiyu a gabanta dan Manzon rahama kiyi shiru na durƙusa ni mai laifine amma ina roƙon ki kiyi shiru. Ta daina kukan muryar ta har ta dishe ta ce ka tafi bana son ganin ka, ya ce in na tafi zaki huce? Ta yi shiru ya miƙe ya tafi.
Ta yi shiru yanda ya damu ya bata tausayi tasan gaskiyan su Armaya'u ne sai ta dage zata samu mijinta. Tasan tana son shi amma ta kasa hucewa bayan tayi wanka kusan biyu saura tana fashin sallah, don haka ta zauna yanzun ne zata karya,ta soma shan tea ta ɗauko waya ta kunna text ɗin shine suka soma shigowa duk na bada haƙuri ne tare da neman yardar ta na son shigowa anjima, tayi shiru tana tunanin yanda take da kishi da yawa. Koda yake tasan tana son shi da yawa . Ya shiga kiran wayar ta barta tana ta ringing tana katsewa ya yo text yana roƙon ta dan girman Allah ta ɗaga wayar shi,ta ɗauka ya ce don son Manzon Allah inzo kin ji don Allah." Ta ce "Um." Ya ce to gani nan nagode. Ta cigaba da kurɓar tea ɗin da ta haɗa cikin ƙaramin kofi da har yanzu bata shanye ba. Ya shigo ya zauna kusa da ita ya ya jikin? Bata tanka ba ya ce ki min magana zan ji sanyi Pretty yanzun da na sameki be kamata insha wahala ba, kuma kema kin san ko wacce ƴa mace bayan ki zata biyo ina sonki, Ina sonki kin san....." Ta ɗaga mishi hannu "bana so ban so indai kazo gani na ne ka ganni kawai." Ya kai hannu zai taɓa ta, ta ce kada ka taɓa ni,ya ce to yanzun Pretty kin ce baki son na taɓa ki yaya zanyi? Ta ce me zan ji a maganar ka Dady,ƙarya? Tayi murmushin takaici aini Dady na wuce ka tsareni ka tsarani halin maza guda dubu ƙila goma ne ban sani ba,dan haka kayi shiru zai fiye maka sai mu daɗe tare amma in kace dole sai ka tsara ni to gara ka tafi abinka, ya ce to nayi shiru can ya ce ban karya ba, da gayya ta cika mishi ƙaton kofi da tea ta tashi ta kawo mishi bread ta koma ta ƙwanta tana kallon shi ga mamakin ta sai gashi ya shanye tas kuma ya ci bread da yawa, ya ce ruwa Pretty ta tashi ta kawo mishi.
Tana kallon shi ya fito da wayoyi kusan huɗu ya kunna nan aka soma kiranshi ya amsa wannan ya amsa wancan yawanci duk abokan harkar kasuwanci ne ya kira Momy ya faɗa mata yana Legos gurin Pretty ta ce ya bata su gaisa ya ce to ya miƙa mata Pretty ga Momy ta amsa ta tashi zaune har wani ɗan russunawa take yi kamar tana gaban Momy, Momy ta ce ba wata damuwa ko? Ta ce a'a ba komai, ta ce yana kula dake ko? Eh yanayi Momy nagode. Ta ce To ki kula min dashi kinji ƴata kada ki damu namiji tamkar yaro ne yanda kika saba mishi zai ɗore mishi na yaba da tarbiyyar ki, kuma nasan zan samu jikoki masu albarka. Ta ce nagode Momy, ta ce to bashi phone ɗin, ta miƙa mishi suka ci gaba da magana kan abin da ya shafe su,yana ajewa wata wayar ta soma ringing tana kallonshi yaƙi ɗaukar wayar,har aka dena kira suna zaune shiru har uku da rabi ta duba lokacin sallah ya yi nan ya zube mata komai wayoyinshi da makullin mota ya tafi a ranta ta ce ƙila yana da mota ne a nan tunda taga itama da tazo, zuwa aka yi aka ɗauke ta.
Wayoyinshi suka shiga ringing tana É—auka tana gaya musu yaje sallah,can wannan wayar ta É—azun ta É—auki ruri taga an sa my wife ta ce dama wayace ba matarka ba ce? Sai da wayar tayi sau uku tana katsewa taga yakamata ta É—auka ko itama zataji yanda ta ji.
Ta ce "Hello who is on the line." Daga can Zainab ɗin ta ce matarshi ce,ke wacece ki ka ɗauki wayar mijina? Abin ya ɗan sosa ma Ruƙayya rai, ta ce Ok mijinki ya shiga wanka in ya fito me za'a ce mishi? Zainab ta soma masifa ke wacece ina tambaya? Ruƙayya ta ce in baki da saƙo in kashe wayar dan in muna tare dashi bashi ba ɗaukar wayarki tun ɗazun kike damun mu. Sai ki bari sai naga dama ya dawo." Ta kashe wayar.
Zainab ta kira Mamanta ta ce Hajiyata aiki bai yi ba, yanzun fa yana gurinta har tana É—aga waya ta tana gaya min magana.
Hajiya ta ce "amma yana miki wulaƙanci ne?" Ta ce a'a sai dai jiya ne ta kira shi muna tare shine da ya shiga wanka na gaggaya mata magana shine fa ya ƙwana yana masifa, ta ce kinyi amfani da duk kayan da ƴar Nijar ta baki? Ta ce sosai ma bakiga yanda yake fita haiyacinshi ba idan muna tare, ta ce to ki dage kafin ta shigo ki riƙe shi gam, ta ce to ki koma wajen malamin, Hajiyar ta ce ki dai tanadi kuɗi yana baki ko? Ta ce tam ko bai bani ba ai zan ɗiba kuma ba ganewa yake ba naga kamar sun mishi yawa, suka sa dariya har da shewa tamkar ƙawaye.
*** *** ***
*** *** ***
Dady ya fito daga wanka duk komai ya yi na samun natsuwa, amma duk hankalinshi yana gurin Pretty tunda bata taɓa kiranshi ba tun da ta tafi Legos, sai dai shi ya kira ta.
Ya zauna bakin gado ya dubi Zainab ya ce je kiyi wanka. Sannan ya ɗauki waya ya fara kiran Pretty tayi ta ringing tana katsewa, kamar bazata dauka ba sai kuma ta ɗauka tayi zaton ko Zainab ɗin ce ta maida mata martani, sai taji shi ya ce Prettyna takaici ne ya kamata a ranta ta ce namiji munafiki, ya ce kin kira ni ɗazun bana jin ki network kin ana matsalar shi ƙwanan nan, ta kayi haƙuri na kira lokacin da bai dace ba,ka ba matarka haƙuri ka ce banyi da nufi ba kamar yanda ta zata sai ta kashe wayar ta gaba ɗaya ma ta ƙwanta,ya zauna yana ta fassara maganar duk yanda akayi Zainab ta kirata ya shiga dialled calls yaga kam an kirata, Zainab ta fito ya dubeta me kika ce ma Pretty da kika kirata? Ta ce ni ban kirata ba ita ce ta kira kuma na shaida mata bana son haka,ban da rainin wayo sai ta kiraka muna tare?"
Haushi ya ƙara kama shi ya ce "kin san wacece Pretty? Duk ya ruɗe ya ce wallahi sai naci mutuncin ki,yarinyar da nike lallaɓawa shine dan kuturun wulaƙanci zaki ɓallo min Niger. Don yanzu ban san ta inda zan fara ba na samu na fara shawo kanta, ya ɗau wayar ya kuma kira a kashe take. Zainab dai sai da tayi data sanin bata kira Ruƙayya ba, domin ko bacci Dady bai yi ba itama faɗan da yake mata ya hana ta runtsawa asubar fari ya soma shiri.
*** *** ***
Ta dubi Salimat ta ce,don Allah in kun je kice ina gaida Sulafat,bana jin daɗi jiya da zazzaɓi na ƙwana,Salimat ta ce zan gaya mata, Nuri ya shigo ya ya dai amarya? Ance bazaki samu zuwa ba, ta ce Eh, Nuri ku gaida min ita, Salimat wata ƴar sabis ɗin su ce da tayi haɗarin mota hanyar ta ta zuwa gida ranar Lahadi, shine zasu je dubata a Ibadan, sakamakon abin da ya faru shine Ruƙayya bata samu iznin zuwa ba gashi ta ƙwana ba lafiya.
Bacci ya soma ɗaukarta ta ji magana a kanta shugaban su ne da kanshi yake sanar da ita tayi baƙo. Kan ta ce wani abu Dady ya shigo sam bata son ganin shi don sai take jin kamar a gaban ta suke jiyannan. Ta runtse ido ya shigo ya zauna kusa da ita.
"Pretty tashi tashi ki jini." Ta ce cikin kuka "me zan ji? Bakada sauran abin da zaka gaya min,baka dashi Dady na jima da sanin halin maza,kai kana cikin maza masu cin amana da yaudara ga karya alƙawari." Ya dubeta ta kauda kai ta ce"na tsane ka." Ya ce ban ci amanar ki ba ban yaudare ki ba,kin ƙi bani dama na nuna miki son da nake miki nasha wuya a kanki ina sonki.
Ta toshe kunne.
"Daina gaya min ƙarya,bana son ji,bana son ji." Ta faɗi tana kuka sosai,ya rasa me zai mata ya ce to yanzu tashi ki faɗi min hukuncina, laifi dai ko wane iri ne na ɗauka,ya duka saitin fuskarta yana shirin haɗa bakinta da nashi,ta tashi tana kare bakinta cikin kuka take maganar kaje ka sha bakin wata sannan kazo ka daɓa min na ce kaje na bar mata kawai ka sake ni....." Ya rufe bakinta da tafin hannu.
Ya ce "Babu wannan maganar a tsakanin mu." Kuka tayi ta mishi ya durƙusa gwiwa bibbiyu a gabanta dan Manzon rahama kiyi shiru na durƙusa ni mai laifine amma ina roƙon ki kiyi shiru. Ta daina kukan muryar ta har ta dishe ta ce ka tafi bana son ganin ka, ya ce in na tafi zaki huce? Ta yi shiru ya miƙe ya tafi.
Ta yi shiru yanda ya damu ya bata tausayi tasan gaskiyan su Armaya'u ne sai ta dage zata samu mijinta. Tasan tana son shi amma ta kasa hucewa bayan tayi wanka kusan biyu saura tana fashin sallah, don haka ta zauna yanzun ne zata karya,ta soma shan tea ta ɗauko waya ta kunna text ɗin shine suka soma shigowa duk na bada haƙuri ne tare da neman yardar ta na son shigowa anjima, tayi shiru tana tunanin yanda take da kishi da yawa. Koda yake tasan tana son shi da yawa . Ya shiga kiran wayar ta barta tana ta ringing tana katsewa ya yo text yana roƙon ta dan girman Allah ta ɗaga wayar shi,ta ɗauka ya ce don son Manzon Allah inzo kin ji don Allah." Ta ce "Um." Ya ce to gani nan nagode. Ta cigaba da kurɓar tea ɗin da ta haɗa cikin ƙaramin kofi da har yanzu bata shanye ba. Ya shigo ya zauna kusa da ita ya ya jikin? Bata tanka ba ya ce ki min magana zan ji sanyi Pretty yanzun da na sameki be kamata insha wahala ba, kuma kema kin san ko wacce ƴa mace bayan ki zata biyo ina sonki, Ina sonki kin san....." Ta ɗaga mishi hannu "bana so ban so indai kazo gani na ne ka ganni kawai." Ya kai hannu zai taɓa ta, ta ce kada ka taɓa ni,ya ce to yanzun Pretty kin ce baki son na taɓa ki yaya zanyi? Ta ce me zan ji a maganar ka Dady,ƙarya? Tayi murmushin takaici aini Dady na wuce ka tsareni ka tsarani halin maza guda dubu ƙila goma ne ban sani ba,dan haka kayi shiru zai fiye maka sai mu daɗe tare amma in kace dole sai ka tsara ni to gara ka tafi abinka, ya ce to nayi shiru can ya ce ban karya ba, da gayya ta cika mishi ƙaton kofi da tea ta tashi ta kawo mishi bread ta koma ta ƙwanta tana kallon shi ga mamakin ta sai gashi ya shanye tas kuma ya ci bread da yawa, ya ce ruwa Pretty ta tashi ta kawo mishi.
Tana kallon shi ya fito da wayoyi kusan huɗu ya kunna nan aka soma kiranshi ya amsa wannan ya amsa wancan yawanci duk abokan harkar kasuwanci ne ya kira Momy ya faɗa mata yana Legos gurin Pretty ta ce ya bata su gaisa ya ce to ya miƙa mata Pretty ga Momy ta amsa ta tashi zaune har wani ɗan russunawa take yi kamar tana gaban Momy, Momy ta ce ba wata damuwa ko? Ta ce a'a ba komai, ta ce yana kula dake ko? Eh yanayi Momy nagode. Ta ce To ki kula min dashi kinji ƴata kada ki damu namiji tamkar yaro ne yanda kika saba mishi zai ɗore mishi na yaba da tarbiyyar ki, kuma nasan zan samu jikoki masu albarka. Ta ce nagode Momy, ta ce to bashi phone ɗin, ta miƙa mishi suka ci gaba da magana kan abin da ya shafe su,yana ajewa wata wayar ta soma ringing tana kallonshi yaƙi ɗaukar wayar,har aka dena kira suna zaune shiru har uku da rabi ta duba lokacin sallah ya yi nan ya zube mata komai wayoyinshi da makullin mota ya tafi a ranta ta ce ƙila yana da mota ne a nan tunda taga itama da tazo, zuwa aka yi aka ɗauke ta.
Wayoyinshi suka shiga ringing tana É—auka tana gaya musu yaje sallah,can wannan wayar ta É—azun ta É—auki ruri taga an sa my wife ta ce dama wayace ba matarka ba ce? Sai da wayar tayi sau uku tana katsewa taga yakamata ta É—auka ko itama zataji yanda ta ji.
Ta ce "Hello who is on the line." Daga can Zainab ɗin ta ce matarshi ce,ke wacece ki ka ɗauki wayar mijina? Abin ya ɗan sosa ma Ruƙayya rai, ta ce Ok mijinki ya shiga wanka in ya fito me za'a ce mishi? Zainab ta soma masifa ke wacece ina tambaya? Ruƙayya ta ce in baki da saƙo in kashe wayar dan in muna tare dashi bashi ba ɗaukar wayarki tun ɗazun kike damun mu. Sai ki bari sai naga dama ya dawo." Ta kashe wayar.
Zainab ta kira Mamanta ta ce Hajiyata aiki bai yi ba, yanzun fa yana gurinta har tana É—aga waya ta tana gaya min magana.
Hajiya ta ce "amma yana miki wulaƙanci ne?" Ta ce a'a sai dai jiya ne ta kira shi muna tare shine da ya shiga wanka na gaggaya mata magana shine fa ya ƙwana yana masifa, ta ce kinyi amfani da duk kayan da ƴar Nijar ta baki? Ta ce sosai ma bakiga yanda yake fita haiyacinshi ba idan muna tare, ta ce to ki dage kafin ta shigo ki riƙe shi gam, ta ce to ki koma wajen malamin, Hajiyar ta ce ki dai tanadi kuɗi yana baki ko? Ta ce tam ko bai bani ba ai zan ɗiba kuma ba ganewa yake ba naga kamar sun mishi yawa, suka sa dariya har da shewa tamkar ƙawaye.
*** *** ***