Sashe 6
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da suka zauna a mota sun ɗau hanyar Legas sannan ya yi ta janta da hira tare da bata labarin yarinyar da zaya aura sannan ta ɗan washe dan ya kula tana cikin damuwa baya son mata tambaya ƙila ba zata so yasan damuwar ta ba. Tana cikin wannan halin yana dai tunanin duk yanda akayi aƙwai wani abu tsakanin ta da mutumin da ya taras gurin Affanta,dan da fara'arta ta fito tana ganinshi sai kawai ta canza fuska. Kuma shima ya shiga ruɗani sakamakon ganinta.
Affa ya maido hankalinshi gurin Dady ganin shi ya yi zaune ya haɗa kai da gwiwa, ya ce "lafiya Yusufa?" Hannu yasa a kafaɗun Dady yana cewa "Taso haba Yusufa ya ya zaka zauna ƙasa." Jikinshi babu lakka ya tashi jiri yake gani don haka ya yi saurin dafa bango, Affa ya kula da haka don haka sai ya ce, zauna kan dakalin nan.
Dady ya zauna Affa ma ya zauna gefen shi Shiru kusan minti uku sannan Affa ya dubi Dady wanda zufa take keto masa, ya ce " Yusufa ka daina jin jirin?" Ya É—ago ya dubi Affa idanunshi sun kaÉ—a sunyi jajir ya ce ya lafa, sai dai naga Dakta ne saboda hawan jini na keson tashi, Affa ya yi shiru sai yana tuhumar kansa,anya ya yi ma yarannan adalci kuwa?.
In zaya iya tunawa tunda ya hana Ruƙayya Dady ko sunan shi bai kuma jin ta ambata ba, kuma yasan tana tsananin son shi, sannan bai ji daɗin yanda ta nuna mishi ba a yau shi har kunya yaji,yasan kuma har Yanzun tana sonshi hasalima a kanshine taƙi aure.
Ya dubi Dady tausayin shi yaji don zai yi matuƙar wuya bata sanadiyyar Ruƙayya ya haɗu da wannan mugun ciwon ba,haƙiƙa ya yi kuskure domin ba Dady ne ya yi mishi laifi ba Alhaji Mansur ne.
Ya dubi Dady ya ce "Yusufa meke tafe dakai kazo ne dan kai min sallama kamar yanda kayi alƙawari?" Wata wawuyar ajiyar zuciya ya saki sai da ya ɗan huta na saƙwanni sannan ya ce Affa na zo ne dama sai kuma ya tuna kodai Ruƙayya tana da aure? Don haka sai ya yi ɗan tsaki ya ce ko da yake gaisheka dama na zo yi. Affa ya ɗago ido dan ganin shin Yusufa da gaske har zuciyarshi ya zo gaida shi ne? Dan tun kan yanda ya amsa ma ya gane yana cikin wani hali,ga mamakin sa sai yaga hawaye suna zuba daga idon Yusufan nan da nan Affa ya ruɗe tare da faɗin "Subuhanallah me yake faruwa?" Dady ya sauko daga dakalin tsugunnawa ya yi gaban Affa ya rasa me zai ce ya yi shiru sai dai zubar da hawaye yake yi, shima Affa kasa magana ya yi hannu yasa akan Dady yana cewa "Menene damuwar ka Yusufa,sanar dani ko zan iya taimaka maka domin nima ubanka ne." Shiru Dady ya yi dan rasa ta inda zai zancen,kiran sallar da aka yi ne yasa Dady ajiyar zuciya sannan ya ɗaga ido ya dubi Affa. Affan ne yace suje suyi sallah in yaso sai suyi maganar cikin tsanaki.
Bayan dawowarsu daga masallaci ɗakin Affa suka yada zango. Shi Affan yasan matsalar Dady Ruƙayya ce to baya son ya soma kawo mishi zancan ta, tunda ya riga ya yi aure, shi kam Dady ya samu natsuwa kaɗan da ya yi sallah don haka ya raya ma ranshi koda Affan zai hana shi Ruƙayya sai ya sanar dashi har Yanzun yana sonta don haka sai ya gyara zama.
Affa ka gafarce ni nasan cewa ka riga ka ƙwaɓe ni da batun Ruƙayya sai dai amma har Yanzun ita zuciyata ke so,ka taimaka min Affa nasha wahala kanta, kada kai min horo da laifin da ba nawa ba laifin wani baya shafar wani na jira Ruƙayya auran ta ya mutu har na gaji sai dai yanzu bansani ba koya mutu ne ya matsa ya kama ƙafar Affa. Don son Manzon Allah kai min agaji."
Jikin Affa babu ƙarfi ya ce "Yusufa haƙiƙa na yanke maka hukunci da ba kaine kayi laifin ba, kuma ina maka albishir da na baka Ruƙayya a karo na biyu duk san da ka shirya ko gobe ne kazo a ɗaura aure. Sannan ina mai farin cikin shaida maka Ruƙayya batayi aure ba karatu tayi yanzu haka tana bauta ma ƙasa ne a Legos.
Daskarewa Dady ya yi a gurin gani yake yi mafarki ne nan ƴan minti na zaya farka haka nan yasan tsokana ce kawai Affa ba da gaske yake ba. Affa ya kula da nufin Dady dan haka sai yace kada ka damu kaje kayi shawara da magabatanka,sam Dady bai san lokacin da ya rungume Affa yana faɗin "Affa kaima Allah ya yi maka abin da ka ke so duniya da lahira, Allah ya jiƙan magabata." Ya miƙe,na tafi Affa sai ka ganni.
*** *** ***
Kai tsaye gurin Momy ya nufa tana sallar isha'i,san da ya shiga yama manta cewa baiyi isha'in ba, koda yake akan hanya ta same shi.
Ya yi ƙwance kan gadon Momy idanunshi lumshe farin cikin shi ya yi mai yawa wai shi ne Affa ya amincemawa ya auri Pretty shin gaske ne ko kuma mafarkin daya saba ne?
Momy ta kai hannu ta dafa ƙafarshi "Yaya dai Babana? Ya ɗago da sauri kuma cikin fara'a ya ce Momy Affa ya kuma bani Ruƙayya, Momy ki tayani murna ina son ta sosai, tayi shiru tana kallon shi gani take ya soma taɓuwa ne,ganin bata ce komai ba yasa ya ce Momy kice wani abu Please cikin sigar shagwaɓa ya yi maganar Momy dariya tayi ta ce kafa girma Dady, ya ce ni dai kimin zancan Pretty,ta ce Nasan ba haka bane janka yake, ya ce "taso muje kiji a gunsa ya ce ko gobe ne na shirya nazo a ɗaura mana aure." Momy ta ce "Haba Dadyna duka fa satin nan aka ɗaura auran ka,shin ya ya za'ayi ka kuma wani? Bayan haka Ruƙayya ma batayi aure ba?" Ya ce "batayi aure ba tama gama karatu, yanzu service take yi a Legos Momy sai kinga yanda Ruƙayya ta zama Pretty ɗin ta sosai. Ya yi sujjada yana ma Allah godiya.
Shima Dad ya yi farin ciki dan kullum burin shi yaga dariyar ɗan tilon ɗana shi dan haka ya ce ba zai yi ƙasa a gwiwa ba goben nan zaya je godiya tare da kai komai, wani satin kuma a ɗaura ma Son ɗin shi aure.
Cikin farin ciki ya tura ƙofar falonshi, Zainab ta dubeshi ta miƙe ta nufo shi My dear ina ka shiga ne ? Ya rungume ta ina cikin farin ciki,itama ta soma murna,sanar dani me ya faru? Ya ƙara rungume ta,an bani Pretty ɗina wai yau nine zan auri Pretty ɗina, cikin sauri ta ture shi tana mishi wani mugun kallo,kasan abin da kake faɗa kuwa,kasan ni wacece ɗin ka kake min wannan maganar?" Ta soma kuka shekaran jiya fa aka ɗaura bikinn mu, amma kace zaka ƙara aure? Wannan wane irin wulaƙanci ne? Haba Dady."
Ya hau kujera ya zauna,ta juya zata shige bedroom, ya ce ke Zainab zo nan." Yanda ya daka mata tsawa shiyasa ta dawo ta zauna ya ce dube ni nan, ta dubeshi kinsan na taɓa ce miki bake kaɗai bace? Cikin kuka ta ce to amma da wuri haka? Ya ce saurareni Pretty ita ce rayuwa ta duk wanda yasan ni yasan halin da na shiga domin ta, ƙarshe ma a rashin tane na aure ki so Please ki bini a hankali kan Pretty komai zai iya faruwa kada ki ɓata min farin ciki na,ya riga ta shiga bedroom ɗin kai tsaye toilet ya nufa,laf ya yi cikin baho yana tunanin Pretty ina ma yana da number ta,ya kirata su sha hira,can cikin nisan da ya yi a tunaninta ya jiyo kukan Zainab.
Cikin hanzari ya fito tana ƙwance kan gado tana kuka. A hankali ya isa gurinta kallonta ya yi tana bashi tausayi ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dafata tare da cewa "Zee.. Zee taso kiji." Ya ɗagota ta ƙwanta a kafaɗarshi tana shashshekar kuka ya ce "Zee son da kike min na gaskiya ne kuwa? Ta dube shi cikin shashsheka ta ce me yasa kake shakka? Tayi ajiyar zuciya sannan ta ci gaba "Ka daina shakka akan son da nake ma." Ya ce to in har kina sona dole kiso Pretty,kar ki zaton cin fuska nake miki, tsakanina da Allah nake sanar dake,ko iyayena sanin mahimmancin a gare shi ne dalilin daya sa zasu goya min baya. Zee inda kinsan halin da na shiga kan Pretty bama zakiyi magana ba shawarar da zan baki itace in baki son ta ki koyi yanda zaki sota dan auran ta ba fashi kuma gaskiya ni bazan iya zama inuwa ɗaya da maƙiyina ba,na sani kema ina son ki tunda ni ne na ajiye ki haka auran Pretty ba shi ne zai sa na wulaƙanta ki ko na daina sonki ba,ke dai ki bani goyan baya. Tasan duk abinda ya faɗa hakan yake nufi,garama ta haƙuri dan haka sai ta zame ta ƙwanta akan gadon shima bai ce komai ba ya koma toilet ya ɗauro alwala yazo ya shiga jero nafiloli dan nuna godiyar shi ga Ubangiji.
Washegari tun da sassafe Dady ya taka gidan Affa dan sanar dashi zuwan Dad É—inshi tare da tambayar yaushe ya kamata zuwan nasu ya kama? Da yamma ko da daddare? Affa ya ce da dare bayan isha'i ai zai fi ko?" Dady ya ce to shikenan Affa,yana son bashi kuÉ—i yana ganin kada Affa ya yi faÉ—a, daga nan gidan Hajja ya zarce.
*** *** ***
Affa ya maido hankalinshi gurin Dady ganin shi ya yi zaune ya haɗa kai da gwiwa, ya ce "lafiya Yusufa?" Hannu yasa a kafaɗun Dady yana cewa "Taso haba Yusufa ya ya zaka zauna ƙasa." Jikinshi babu lakka ya tashi jiri yake gani don haka ya yi saurin dafa bango, Affa ya kula da haka don haka sai ya ce, zauna kan dakalin nan.
Dady ya zauna Affa ma ya zauna gefen shi Shiru kusan minti uku sannan Affa ya dubi Dady wanda zufa take keto masa, ya ce " Yusufa ka daina jin jirin?" Ya É—ago ya dubi Affa idanunshi sun kaÉ—a sunyi jajir ya ce ya lafa, sai dai naga Dakta ne saboda hawan jini na keson tashi, Affa ya yi shiru sai yana tuhumar kansa,anya ya yi ma yarannan adalci kuwa?.
In zaya iya tunawa tunda ya hana Ruƙayya Dady ko sunan shi bai kuma jin ta ambata ba, kuma yasan tana tsananin son shi, sannan bai ji daɗin yanda ta nuna mishi ba a yau shi har kunya yaji,yasan kuma har Yanzun tana sonshi hasalima a kanshine taƙi aure.
Ya dubi Dady tausayin shi yaji don zai yi matuƙar wuya bata sanadiyyar Ruƙayya ya haɗu da wannan mugun ciwon ba,haƙiƙa ya yi kuskure domin ba Dady ne ya yi mishi laifi ba Alhaji Mansur ne.
Ya dubi Dady ya ce "Yusufa meke tafe dakai kazo ne dan kai min sallama kamar yanda kayi alƙawari?" Wata wawuyar ajiyar zuciya ya saki sai da ya ɗan huta na saƙwanni sannan ya ce Affa na zo ne dama sai kuma ya tuna kodai Ruƙayya tana da aure? Don haka sai ya yi ɗan tsaki ya ce ko da yake gaisheka dama na zo yi. Affa ya ɗago ido dan ganin shin Yusufa da gaske har zuciyarshi ya zo gaida shi ne? Dan tun kan yanda ya amsa ma ya gane yana cikin wani hali,ga mamakin sa sai yaga hawaye suna zuba daga idon Yusufan nan da nan Affa ya ruɗe tare da faɗin "Subuhanallah me yake faruwa?" Dady ya sauko daga dakalin tsugunnawa ya yi gaban Affa ya rasa me zai ce ya yi shiru sai dai zubar da hawaye yake yi, shima Affa kasa magana ya yi hannu yasa akan Dady yana cewa "Menene damuwar ka Yusufa,sanar dani ko zan iya taimaka maka domin nima ubanka ne." Shiru Dady ya yi dan rasa ta inda zai zancen,kiran sallar da aka yi ne yasa Dady ajiyar zuciya sannan ya ɗaga ido ya dubi Affa. Affan ne yace suje suyi sallah in yaso sai suyi maganar cikin tsanaki.
Bayan dawowarsu daga masallaci ɗakin Affa suka yada zango. Shi Affan yasan matsalar Dady Ruƙayya ce to baya son ya soma kawo mishi zancan ta, tunda ya riga ya yi aure, shi kam Dady ya samu natsuwa kaɗan da ya yi sallah don haka ya raya ma ranshi koda Affan zai hana shi Ruƙayya sai ya sanar dashi har Yanzun yana sonta don haka sai ya gyara zama.
Affa ka gafarce ni nasan cewa ka riga ka ƙwaɓe ni da batun Ruƙayya sai dai amma har Yanzun ita zuciyata ke so,ka taimaka min Affa nasha wahala kanta, kada kai min horo da laifin da ba nawa ba laifin wani baya shafar wani na jira Ruƙayya auran ta ya mutu har na gaji sai dai yanzu bansani ba koya mutu ne ya matsa ya kama ƙafar Affa. Don son Manzon Allah kai min agaji."
Jikin Affa babu ƙarfi ya ce "Yusufa haƙiƙa na yanke maka hukunci da ba kaine kayi laifin ba, kuma ina maka albishir da na baka Ruƙayya a karo na biyu duk san da ka shirya ko gobe ne kazo a ɗaura aure. Sannan ina mai farin cikin shaida maka Ruƙayya batayi aure ba karatu tayi yanzu haka tana bauta ma ƙasa ne a Legos.
Daskarewa Dady ya yi a gurin gani yake yi mafarki ne nan ƴan minti na zaya farka haka nan yasan tsokana ce kawai Affa ba da gaske yake ba. Affa ya kula da nufin Dady dan haka sai yace kada ka damu kaje kayi shawara da magabatanka,sam Dady bai san lokacin da ya rungume Affa yana faɗin "Affa kaima Allah ya yi maka abin da ka ke so duniya da lahira, Allah ya jiƙan magabata." Ya miƙe,na tafi Affa sai ka ganni.
*** *** ***
Kai tsaye gurin Momy ya nufa tana sallar isha'i,san da ya shiga yama manta cewa baiyi isha'in ba, koda yake akan hanya ta same shi.
Ya yi ƙwance kan gadon Momy idanunshi lumshe farin cikin shi ya yi mai yawa wai shi ne Affa ya amincemawa ya auri Pretty shin gaske ne ko kuma mafarkin daya saba ne?
Momy ta kai hannu ta dafa ƙafarshi "Yaya dai Babana? Ya ɗago da sauri kuma cikin fara'a ya ce Momy Affa ya kuma bani Ruƙayya, Momy ki tayani murna ina son ta sosai, tayi shiru tana kallon shi gani take ya soma taɓuwa ne,ganin bata ce komai ba yasa ya ce Momy kice wani abu Please cikin sigar shagwaɓa ya yi maganar Momy dariya tayi ta ce kafa girma Dady, ya ce ni dai kimin zancan Pretty,ta ce Nasan ba haka bane janka yake, ya ce "taso muje kiji a gunsa ya ce ko gobe ne na shirya nazo a ɗaura mana aure." Momy ta ce "Haba Dadyna duka fa satin nan aka ɗaura auran ka,shin ya ya za'ayi ka kuma wani? Bayan haka Ruƙayya ma batayi aure ba?" Ya ce "batayi aure ba tama gama karatu, yanzu service take yi a Legos Momy sai kinga yanda Ruƙayya ta zama Pretty ɗin ta sosai. Ya yi sujjada yana ma Allah godiya.
Shima Dad ya yi farin ciki dan kullum burin shi yaga dariyar ɗan tilon ɗana shi dan haka ya ce ba zai yi ƙasa a gwiwa ba goben nan zaya je godiya tare da kai komai, wani satin kuma a ɗaura ma Son ɗin shi aure.
Cikin farin ciki ya tura ƙofar falonshi, Zainab ta dubeshi ta miƙe ta nufo shi My dear ina ka shiga ne ? Ya rungume ta ina cikin farin ciki,itama ta soma murna,sanar dani me ya faru? Ya ƙara rungume ta,an bani Pretty ɗina wai yau nine zan auri Pretty ɗina, cikin sauri ta ture shi tana mishi wani mugun kallo,kasan abin da kake faɗa kuwa,kasan ni wacece ɗin ka kake min wannan maganar?" Ta soma kuka shekaran jiya fa aka ɗaura bikinn mu, amma kace zaka ƙara aure? Wannan wane irin wulaƙanci ne? Haba Dady."
Ya hau kujera ya zauna,ta juya zata shige bedroom, ya ce ke Zainab zo nan." Yanda ya daka mata tsawa shiyasa ta dawo ta zauna ya ce dube ni nan, ta dubeshi kinsan na taɓa ce miki bake kaɗai bace? Cikin kuka ta ce to amma da wuri haka? Ya ce saurareni Pretty ita ce rayuwa ta duk wanda yasan ni yasan halin da na shiga domin ta, ƙarshe ma a rashin tane na aure ki so Please ki bini a hankali kan Pretty komai zai iya faruwa kada ki ɓata min farin ciki na,ya riga ta shiga bedroom ɗin kai tsaye toilet ya nufa,laf ya yi cikin baho yana tunanin Pretty ina ma yana da number ta,ya kirata su sha hira,can cikin nisan da ya yi a tunaninta ya jiyo kukan Zainab.
Cikin hanzari ya fito tana ƙwance kan gado tana kuka. A hankali ya isa gurinta kallonta ya yi tana bashi tausayi ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dafata tare da cewa "Zee.. Zee taso kiji." Ya ɗagota ta ƙwanta a kafaɗarshi tana shashshekar kuka ya ce "Zee son da kike min na gaskiya ne kuwa? Ta dube shi cikin shashsheka ta ce me yasa kake shakka? Tayi ajiyar zuciya sannan ta ci gaba "Ka daina shakka akan son da nake ma." Ya ce to in har kina sona dole kiso Pretty,kar ki zaton cin fuska nake miki, tsakanina da Allah nake sanar dake,ko iyayena sanin mahimmancin a gare shi ne dalilin daya sa zasu goya min baya. Zee inda kinsan halin da na shiga kan Pretty bama zakiyi magana ba shawarar da zan baki itace in baki son ta ki koyi yanda zaki sota dan auran ta ba fashi kuma gaskiya ni bazan iya zama inuwa ɗaya da maƙiyina ba,na sani kema ina son ki tunda ni ne na ajiye ki haka auran Pretty ba shi ne zai sa na wulaƙanta ki ko na daina sonki ba,ke dai ki bani goyan baya. Tasan duk abinda ya faɗa hakan yake nufi,garama ta haƙuri dan haka sai ta zame ta ƙwanta akan gadon shima bai ce komai ba ya koma toilet ya ɗauro alwala yazo ya shiga jero nafiloli dan nuna godiyar shi ga Ubangiji.
Washegari tun da sassafe Dady ya taka gidan Affa dan sanar dashi zuwan Dad É—inshi tare da tambayar yaushe ya kamata zuwan nasu ya kama? Da yamma ko da daddare? Affa ya ce da dare bayan isha'i ai zai fi ko?" Dady ya ce to shikenan Affa,yana son bashi kuÉ—i yana ganin kada Affa ya yi faÉ—a, daga nan gidan Hajja ya zarce.
*** *** ***