← Book details Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 21

Sashe 14

Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saboda yanayin zuwan da Dady ya yi mata. lokaci mai tsawo Dady yana babban birnin majidaÉ—i kafin ya rungume Pretty É—in shi tsam.

Farin ciki da wani shegen sonta ne suke ƙara ratsa shi, tsawon minti goma ya buɗe ido ya dubi fuskarta idonta yana rufe sai dai zufa da hawaye sun ma fuskar kaca-kaca ya tashi zaune ya jawo kanta ya ɗora kan cinyarshi da zanin gado yake share mata fuska yana faɗin "sannu Pretty kin ji Allah ya shi miki albarka lallai ke wata abin alfahari na ce sannu ƴar halak bari nayi wanka kema sai kiyi ko?" Ya gyara mata ƙwanciya ya shiga toilet.

Farin ciki ran Ruƙayya kar ki tona, domin ta zama cikin matan da mazajensu suke alfahari da su ta tattala budurcinta yayin ƴan matancinta, ta kawo shi inda ya dace,bata damu da ciwon da jikinta yake yi ba ga sanyi yana ratsa ta,tasa hannu ta janyo bargo ta rufa,san da ya fito jikinta ya ɗime da zazzaɓi ya ɗan ja bargon tashi kiyi wanka,ta kuma ƙudundunewa haƙoranta suka soma haɗuwa da ƴan uwansu, sanyi ta faɗa cikin ƙerma ya hau gadon shima ya shiga bargon jikinta har rawa yake yi, "innalillahi." Ya dubi agogo ƙarfe uku gashi basu da ko farasitimol wayar Momy ya kira duk ya ruɗe, tana jin ya ce Momy, ta yunƙura don Allah Dady kar ka tashe ta ka rufa mana asiri,bai jira jin zancen ta ba ya sake faɗin Momy, Momy ta ce lafiya cikin daren nan? Ya ce Pretty ba lafiya kuna da farasitimol inzo in amsa? Da safe sai muje asibiti, ta ce ka tsaya a gurin ta bari na zo, ya ce to,ya ɗauko mata rigar bacci mai ɗan kauri ya ce bari in saka miki ga Momy nan zuwa. Da sauri ta tashi zaune ta saka rigar a jikinta, ya je ya buɗe Momy ta shigo da magani Ruƙayya ta kasa kallonta, Momy ta ce kawo mata ruwa tasha maganin, tana sha ta ƙwanta. Can bacci ya ɗauke ta Momy tayi musu sai da safe ta tafi, jikinta ya shige ya ƙwanta ya ɗora kanta saman ƙirjinshi tayi ajiyar zuciya ta cigaba da bacci.

Shi kam yana jin ajiyar numfashinta sonta yana ƙara shigar shi so tsansta mai cike da yarda mai tsafta.

Bai san yayi kuskure ba sai da safe da ta kasa tashi tayi wanka, suna cikin ƴar dabarar yanda zata miƙe sai suka ji sallamar Momy ba kunya ya ce Yauwa Momy taimaka mata, kunya ta kama Ruƙayya ba shiri ta miƙe ta fara takawa cikin dauriya ta shige toilet Momy ba yarinya ba ce ta fahimci komai musamman da taje bakin gadon ta kakkaɓe musu shinfida ta ce in tasha koda tea ne sai ta ƙwanta. Alamar da ta gani kan shinfiɗar ya tabbatar mata ɗan ta ya yi sa'a don haka tace ya kawo sabon zanin gado ta matsa kusa da toilet ta ce ƴata ki shiga ruwan zafi sosai kisa dettol kin ji." A ranta ta ce shikenan mai aukuwa ta auku.

*** *** ***

Ƙwana uku Dady da Momynshi suna tattalin Pretty ɗin tashi, tun tana kunya har ta daina. A gabanta Momy tai mishi faɗa cewa ka gwada mata ƙarfi ne Dady? Shiru ya yi yana shafa kanshi. Ta fito wanka ta zauna gaban madubi tana ƙwalliya tayi ƙyau ita kanta tasan tana amarci,gashin ta sai ƙyalli yake gashi tasa material mai fulawoyi ruwan madara,ta taje kanta gashin ya sauka har kafaɗunta ta soma fesa tararuka Dady ya shigo yana shaƙar ƙamshin turarenta,bayanta ya tsaya tana ƙoƙarin ɗaura ɗan ƙwali ya amsa ya aje.

"Nafi son ganinki haka My Pretty" ya duka ya saka fuskarshi a gefen wuyanta duk suna kallon madubi ya ce kinada ƙyau Prettyna, ta ce na kai kane? Ya ce kenan muna kama, yaushe ne zaki bani Baby shekaru na sun soma shurawa ina son yara." Kunya ta ji ta runtse ido ta ce ko yau ne Allah ya kawo zan baka, ya ce ƴan biyu nake so,ta ce to ka gayawa Allah.

*** *** ***

Wata rayuwa Dady ya nuna wa Pretty ɗin shi a wannan ƴan ƙwanakin nan mai matuƙar daɗi, itama yanzu tasan babban birnin majidaɗi, yanzun haka da take ƙwance saman kujera rungume da filon kujerar layin M Bash take kira dan neman ƙarin bayani akan wasu turaruka cikin kayan gyaran jikin da Mom ta kawo mata.

Bayan ta ɗauka Ruƙayya ta hau mata tsiya da cewa "haba M Bash kamar kun kawo gawa rami keda Armaya'u babu ko waya, Munira ta ce gara mu barku ku ci amarci babu takura." Ta ce muna ci kam lallai garin daɗi yana gidan aure amma sai ansha wuya ake shan daɗi, M Bash ta ce shegiya Ruƙy kinji maji daɗi ne ina fushin da ake yi da angon? Ta ce da kenan aiko da ɗin ma ina son kayana rashin fahimta ne yanzu kuma mun fahimci juna duk wata mata tana bayana, ko bai faɗa ba haka ne. Don haka bata gabana yanzu ma ina gaban turarukan da Mom ta bani ina son kiyi min bayanin su. Turare in zaki ƙwanta ki shafa kaɗan,garin maganin kisa zuma zaki ganta cikin ƴar leda sai kisa ruwa, kaɗan zakiyi amfani dashi zaki sha mamaki. Suna sallama Dady ya shigo ta yarda wayar saman kujera ta miƙe suka maƙale juna ya ce "ina son ki Pretty." Ta ce "I love You My Yusuf ina sonka." Tamkar ya haɗiyeta yaja hannunta suka fita gaban wata ƴar mitsilar mota fara tas ya tsayar da ita sannan yaja hannunta ya saka mata key sannan ya raɗa mata ƙyautar budurcinki nagode,rungume shi tayi.

Momy tana hangen su daga saman bene ranta ƙal farin ciki, ta ce ka nuna ma Momy ma." Ya ce ita ce ta zaɓar miki zan dinga koya miki duk Sunday,Ni kuma menene tukwicina?" Ta ɗan sake shi tayi taku biyu zuwa uku ta juyo ta ƙyafta mishi ido ɗaya tace to night, ya biyo ta yajata jikinshi me zaki bani? Ta ce zan kaika babban birnin majidaɗi zaka sha mamaki.

Ya kam sha mamakin har yaso ya zauce shiyasa ya ce ya fasa barin ta Kaduna kamar yanda da farko ta buƙata. Ya ce ai tana da ɗaki a Abuja Momy tasa baki da cewa kibi mijinki ƴata kar ki damu da kishiya,ke dai ki zama mai biyayya da ƙyautatawa shi ya ɗibi kayan ta aƙwati biyu haka kit ɗin ta da abubuwan ƙamshi na kimtsa jiki, basu samu Zainab ɗin a gida ba ɗakinta ya buɗe mata ta shiga ya taimaka mata gurin gyara ɗakin duk da cewa a gyare yake.

Suka shirya kayanta cikin dirowa, Sunday ya gabatar musu da abinci a dining table sun sha Hollandia kafin suka shige toilet,ƙiri-ƙiri Ruƙayya ta hana Dady ya sanar da kowa cewa yana cikin Abuja duk da ɗinbin jama'ar dake son ganinshi ba cewa tayi kada ya kira su ba a'a idan tana gabanshi ya kan mance kowa da komai sai Pretty.

Zainab sai bayan isha'i ta dawo suna ƙwance kan doguwar kujera duka su biyu, suna kallo tare da ƴan wasanni da suka saba ma juna turus ta tsaya tana dubansu. Kishi da fargaban rashin samunta da Dady baiyi a gida ba ta ɗaure ta ce "Sannunku." Dady ya dubeta rai a ɓace amma sai ya share don kada ya yi mata cin fuska gaban kishiya ya ce "yauwa Zee,ina kika je?" Ta ce naje na dubo Hajiya ta bataji daɗi ba, ya ce Allah ya sauwaƙe ya dubi Pretty ɗin shi da kishi ya hanata ko motsi ya ce Pretty ga Zee ta dawo ta daure ta yunƙura ta tashi zaune suka dubi juna cikin ido,gaban Zainab ya yi mummunan faɗuwa ganin Ruƙayya ta ce, Ruky dama kece kishiyata? Ruƙayya ta ce oh baki sani ba ko? Wallahi ni ce ya ƙwana biyu? Zainab ta haɗiye miyau da ƙyer ta ce lafiya lau ta nufi ɗakin ta lallai sai ta dage kafin ta ƙwace Dady,nan taji tsanar Ruƙayya ta shige ta.

Ruƙayya ta fito daga wanka ta gama shirin ƙwanciya. Yau kam tasan sai dai ta rungumi filonta,tana shirin kulle ƙofa Dady ya shigo ta ce na zata ka ƙwanta? Ya ce a ina? Ta ce ɗakin matarka mana, ya ce a'a,ta tsaya ban gane a'a ba ai can zaka ƙwana ko ka manta ne? Ya yi shiru tazo ta shige jikinshi ka je can haƙƙinta ne ƙwananta ne gobe sai ka raba mana ƙwana in ɗai ɗai ko biyu bazan taɓa so ka zama mara adalci ba don ina son ka zama Yusuf ɗina har cikin aljanna." Ya zuba mata ido in sumbace ki? Ta ce kaɗan kar ka zarme.

Sai da ta ƙwace kanta ta tura shi ta rufe ƙofa kan gado ta faɗa ta rungume filo wasu ƙananan ƙwalla suka zubo mata Dadynta yana tare da kishiyarta.

Da safe ta fito wanka ta zauna gaban madubi in kinga yanda take tsara ƙwalliya sai kiyi tsammanin shi ta karanta a makaranta. Ta gama aka taje gashi wata shegiyar shadda tasa,tasha ado ta zuba ɗauri tamkar zata je liyafa dama gashi har Yanzun lallen amarcinta na nan wata shahararriyar mai dayis tayi mata,wato Sadiya layin ƴan kifi Allah ya yi mata baiwar zana shi tamkar daga India ta koyo,in tayi maka ya yi wata bai goge ba, amarya sak kalolin turaruka ta fesa sai ƙamshi yake tashi.

Dady ya turo ƙofa a hankali ya shigo kayan bacci ne a jikinshi wani abu taji ya tukare ta a ƙirji amma sai ta danne ta rage tsawo, ina ƙwana? Ya shafi fuskarta lafiya Prettyna kin tashi lafiya? Ta ce lafiya, ya ce zo muje dining room,ta ce baka zuwa ofis ne yau? Ya ce zanje, ta ce bakayi wanka ba, ya ce zanyi muje kiyi break ta ce a'a sai kayi wanka yaso ya shiga toilet ɗin ta tace a'a sai dai yaje can inda ya ƙwana.
Chapter 14 · 0% Book details