Sashe 3
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A fili ta ce "Nasan kana son ta Yusufa, ta dalilin ta ka samu hawan jini,baka dangana da yarinyar nan ba sai da aka haɗa da roƙon Allah sannan ka lafa kayi haƙuri,matar mutum kabarin sa, ya ce "Hajja sam ban so ni aka haɗa da roƙon Allah ba wai don na dangana da son Pretty naso a ce son ta ya kashe ni,." Hajja ta ce "Ashsha! Ashsha kul na kuma ji koda bai kashe ka ba ai ya saka rayuwarka cikin wahala tunda in ciwon nan ya tashi duk hankalinmu tashi yake. Ya ce ai Dad shine ya ja min dan da basu cuci Affa sun zalunce shi ba wallahi na san ba zai hana min Pretty ba,kuma banga laifin Affa ba domin an yi mishi FIN ƘARFI, kafin Hajja ta ce wani abu wayar Dady ta shiga ƙara ya duba Hussain ne ya tuna suna can suna jiranshi game da programs ɗin bikin shi. Ya ce "Hello, Hussain sorry kuna jirana ko, ina zuwa. Ya kashe wayar sannan ya kira layin direban shi ya ce ka sameni gidan Hajja a Kabala ka hawo achaɓa kazo ka jani.
Sabi'u ya ce "To ƴallaɓai." Komawa ya yi ya jingina da kujera. Hajja ta dube shi ta ce "Ina ce kace tafiya zaka yi." Ya maida numfashi bazan iya jan motar bane shine na kira direba ya jani. Gaban Hajja ya faɗi ta ce,ba dai jikin ba ne? Ya ƙaƙaro murmushi ya ce "a'a ba jikin bane Hajja,kin san jiki da jini gashi muna yawan zirga-zirga aikin ba hutu,ta ce To bari in baka wani magani na gajiya ne shima na hawan jinin ne, ta miƙe ta shiga bedroom ɗin ta ta ɗauko garin magani ta miƙa mishi.
Gashi kuma kai ba gwanin shan koko ba sai kasha da Yoghurt ko Hollandia naka,ya yi,sai sannan direban ya yi mishi waya ya iso, ya ce to,gami da faɗin Hajja ni zan tafi." Ya ciro kuɗi,ba dai ki buƙatar komai ko? Ta ce a'a ba komai, ya miƙa mata kuɗin da shima bai san iyakar su ba............
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[7/31, 16:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 2
Baisan yawan su ba, ya ce "gashi na cin goro, wannan kuma ki ba ma Saude." Ta ce mungode Allah shi albarka ya biya buƙatu. Ya ce amin Hajja nagode, ta ce a'a nice da godiya Yusufa aini sai hamdala da Ubangiji ya barni da raina, da ubanka ne me min komai gashi har mun kai matsayin da ya haifeka gashi kaima kana kula dani, ya ce duk albarkarki muke nema Hajja.
Har waje ta rakashi inda ya shiga mota direba yaja shi suka tafi.
*** *** *** ***
Yau kam a gajiye Ruƙayya ta taso daga kotun da aka tura ta game da wata shari'a. Bakin gate suka yi kiciɓis da Nuraddeen Kano. Ya ce a'a Ruƙy yana ganin ki haka hula a hannu jaka hannu gari yai sanyi? Ta ce kai dai bari kawai Nuri,yau ɗin nan na gaji sosai fa ta nufi ɗakin su ta shiga sai da ta huta tayi wanka taci abinci sannan ta yi sallah.
Washegari tana ɗauraye after dress ɗin ta da T shirt ɗin ta,Nura ya sameta Ruƙy ina tunanin duk ma yanda za'ayi gobe Friday koda yamma ne zan je Kano, ta ce ka dawo yaushe? Ya ce Sunday ko Monday." Ta ce Kash, nima da ina da issasun kuɗi da mun je sai nima na sauka Kaduna,in yaso in kana dawowa sai na baka adireshin gidan mu sai mu dawo.
Ya ce "Oh muje in kuÉ—in naki sun kasa sai na cika miki dan nima sai a hankali,allwasce É—ina ne na wancan watan ta ce aini nawa tuni sun sha aiki.
Ranar juma'a tunda safe suka soma shiri,tasowar asuba suka yi,dan haka huɗu tai musu a Kaduna. Sun tsaya a garejin Mando nan Ruƙayya ta sauka,Nura ya rako ta inda yake cewa gashi ba waya a hannunki bare in na shigo unguwarku na kira ki. Ya kamata ace kina da waya fa ba girmanki ba ne. Ta yi dariya sannan ta ce Nuri kenan,Ni nan daka ganni ban so na riƙe waya ba ne, Amma ko ada,na riƙe waya a lokacin da sai wanda ya isa ne yake riƙewa, kuma ma yanzun ban ga dama bane, amma ka bari insha Allahu sai dai kaji calling ɗina. Alƙawari zan kiraka da layina, ya ce shikenan.
Mashin ta samu ɗari uku tun daga Mando gareji zuwa Kabala su kenan kuɗin ta dan haka ta ce muje ai gida nazo kuma bana son shiga mota ga hadari yana ta harhaɗowa gara na isa gida akan kari,bana son ruwa ya taɓa lafiya ta. Sun iso daf da shiga Kabala suna kan titin independence aka soma tsula ruwa nan kuma mashin tayi faci. Ruƙayya ta ce "Oh ni Ruƙy ya zanyi kenan? Ta sauka ta bashi ɗari ukun ya ce "Yaya zaki bani duka gashi bamu kai ba? Ta ce ba komai kaje kawai bari na taka, ya ce ga ruwa? Ta ce kar ka damu,tana tafiya duk ta jiƙe.
Tun daga nesa Sabi'u ya dubi ubangidansa "Ƴallaɓai ga wata can tana buƙatar taimako." Dady ya amsa ba tare da ya ɗago ba, ya ce "A taimaka mata." Ya rufe baki tare da faɗuwar gaba irin wacce bai taɓa ji ba, ya kai hange ga yarinyar da Sabi'u ya ce su taimaka mata,da tazara tsakanin su kuma shekaru baƙwai masu ƙyau bai ganta ba, amma sai da ya gane ta. Ko shakka ba zaya yi ba waccan Pretty ɗin shi ce, domin duk da basa tare kuma idanunshi sun daina ganin ta wannan ba zai hana zuciyarshi kullum karanta surar ta ba, haka yake tsarata kullum.
Sanye take da jallabiya doguwa baƙa haɗe da gyalenta,jaka da takalmin ta ma duk baƙaƙe ne,sai dai ta jiƙe sharkaf har ɗiga take yi.
Jijiyoyin jikin Dady suka tsaya cak, komai ya daina kai saƙo a jikinshi lokacin da ya tsinkayi muryar Ruƙayya suna magana da direba yana cewa baiwar Allah shigo mu taimaka miki ta ce "a'a, nagode Malam na kusa gida gashi kuma duk na jiƙe,ka na jiƙa muku kujera." Ya ce, bakomai shigo taimako ne ai."
Sam Ruƙayya bata ga Dady ba kasancewar motar na waje baya ganin na ciki, amma shi Dady yana ganin ta, tana shaga gaban motar gabanta ya faɗi sai dai har ga Allah bata zata da wani cikin motar ba, don haka sai tayi addu'a a ranta dan kar ta faɗa mugun hannu.
Ta ɓalle maɓallan gaban abayar ta cire sai ga riga T.Shirt mai ɗauka da rubutun N.Y.S.C ta bayyana da wandon ta, ta zage jakar hannunta ta ciro rigar sanyin N.Y.S.C tasa ta ɗaura gyale kamar ɗan ƙwali sannan ta ciro hijabi ƙarami tasa ta maida abaya cikin jaka. Ƙamshin da take shaƙa da faɗuwar gabanta da yaa tsananta sune suka tuna mata da wani abu, tabbas duk inda turaren nan ya fito daga gurin Dady ne, domin tun da suka rabu da Dady bata kuma jin ƙamshin nan ba sai yau.
Ya Allah! Ta faɗa cikin wata muguwar faɗuwar gaba, lokacin da ta dubi madubi ta ga Dady zaune a bayanta. Daga nan bata kuma motsi ba sai ƙwatancen da ta dinga ma direba har lungunsu. Ta ce da direba nagode fa, ya ce bakomai." Ta buɗe mota ta fita.sannan ta saci kallon Dady ta rufe ta tafi, zuciyarta cike da mamakin Dady. Lallai duniya wai kamar Dady ya ganta ya share ta, hawaye ya zubo mata tayi nadamar zuwan ta Kaduna a yau.
Shi kam Dady be ma san anzo har Ruƙayya ta fita ba,haƙiƙa jikinshi ya mutu, zuciyarshi ba ta tare dashi,yana tunanin dama Pretty bata yi aure ba,ko ko tayi ta cigaba da karatun a gidan mijinta? Auren ya mutu ne? Ko ko mijinne ya mutu? Ko ko da auren ta? Wanene zai bashi wannan amsar. Ganin Ruƙayya ya tsorata Dady gami da firgita shi, ta taɗo mishi da wata sabuwar muhimmiyar soyayyar ta.
A fili ya ce "Wannan karon ko Pretty tana da aure ko batada shi, koma wanene mijinta sai ya bai mishi Pretty É—in shi,kai koma ta halin yaya ne shi bazaya barta ba,bai san sun iso gidan Hajja ba sai dai ya ji Sabi'u na cewa.
"Ƴallaɓai mun iso." Ga zaton shi gidan su Ruƙayyan, sai yaga gidan Hajja nan ya soma tunanin kodai mafarki ne? Kai ba mafarki bane. Ya dubi Sabi'u ya ce "ina Pretty ɗin fa? Kan Sabi'u ya ɗaure ya ce,wace Pretty kuma ko wacce muka ɗauko? Dady ya ce "Eh," Sabi'u ya ce ai mun sauke gida Ƴallaɓai baka kula bane." Nan Dady ya wayance ya ce "Ok." Ya shiga gidan Hajja ya bar Sabi'u da mamakin halin da Ƴallaɓai ya shiga kan yarinyar nan,a ranshi ya ce koda yake fa yarinyar ta haɗu dole Oga ya ruɗe har magana yake shi kaɗai ina jin shi.
*** *** *** ***
Yaraf ya zube a kujerar falon Hajja,Saude da ke jira abinci akan centre table tana faɗin "Uban masu gida kasha hanya,in fatan dai baka sha dukan ruwa ba?" Da ƙyar ya ce sannu Saude ina Hajja? Ta ce gata nan zuwa tana ɗauro alwala ne, sama-sama suka gaisa da Hajja don haka ta tasa shi da tambayoyi jikinne Yusufa ko ko gajiya ce?.
Numfashinsa yana sama-sama ya ce "Duk aƙwai." Ta ce "To ai gara ka je asibiti ko? Ya ce "wannan bana asibiti bane ku barni na huta bana son magana." Duk shiru suka yi,yana ƙwance har aka kira magriba, ya yunƙura da ƙyar ya tafi sallah. Hollandia kawai ya ɗaɗɗaka baici komai ba ya kira direba a waya ya zo ya ɗauke shi. Hajja ta yi tayi ya ci abinci kasancewar ya yi azumi ya ce "Kiyi haƙuri Hajja ba zan iya cin komai ba, ina cikin damuwa ki min addu'a." Ido ta bishi da shi har ya shiga cikin mota sam baya tare da tunanin shi, tunanin shi kawai ta ina zaya fara da wannan lamarin.?
A hankali ya ce "Sabi'u kaini gida gurin Momy."
Sabi'u ya ce "To ƴallaɓai." Komawa ya yi ya jingina da kujera. Hajja ta dube shi ta ce "Ina ce kace tafiya zaka yi." Ya maida numfashi bazan iya jan motar bane shine na kira direba ya jani. Gaban Hajja ya faɗi ta ce,ba dai jikin ba ne? Ya ƙaƙaro murmushi ya ce "a'a ba jikin bane Hajja,kin san jiki da jini gashi muna yawan zirga-zirga aikin ba hutu,ta ce To bari in baka wani magani na gajiya ne shima na hawan jinin ne, ta miƙe ta shiga bedroom ɗin ta ta ɗauko garin magani ta miƙa mishi.
Gashi kuma kai ba gwanin shan koko ba sai kasha da Yoghurt ko Hollandia naka,ya yi,sai sannan direban ya yi mishi waya ya iso, ya ce to,gami da faɗin Hajja ni zan tafi." Ya ciro kuɗi,ba dai ki buƙatar komai ko? Ta ce a'a ba komai, ya miƙa mata kuɗin da shima bai san iyakar su ba............
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[7/31, 16:44] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 2
Baisan yawan su ba, ya ce "gashi na cin goro, wannan kuma ki ba ma Saude." Ta ce mungode Allah shi albarka ya biya buƙatu. Ya ce amin Hajja nagode, ta ce a'a nice da godiya Yusufa aini sai hamdala da Ubangiji ya barni da raina, da ubanka ne me min komai gashi har mun kai matsayin da ya haifeka gashi kaima kana kula dani, ya ce duk albarkarki muke nema Hajja.
Har waje ta rakashi inda ya shiga mota direba yaja shi suka tafi.
*** *** *** ***
Yau kam a gajiye Ruƙayya ta taso daga kotun da aka tura ta game da wata shari'a. Bakin gate suka yi kiciɓis da Nuraddeen Kano. Ya ce a'a Ruƙy yana ganin ki haka hula a hannu jaka hannu gari yai sanyi? Ta ce kai dai bari kawai Nuri,yau ɗin nan na gaji sosai fa ta nufi ɗakin su ta shiga sai da ta huta tayi wanka taci abinci sannan ta yi sallah.
Washegari tana ɗauraye after dress ɗin ta da T shirt ɗin ta,Nura ya sameta Ruƙy ina tunanin duk ma yanda za'ayi gobe Friday koda yamma ne zan je Kano, ta ce ka dawo yaushe? Ya ce Sunday ko Monday." Ta ce Kash, nima da ina da issasun kuɗi da mun je sai nima na sauka Kaduna,in yaso in kana dawowa sai na baka adireshin gidan mu sai mu dawo.
Ya ce "Oh muje in kuÉ—in naki sun kasa sai na cika miki dan nima sai a hankali,allwasce É—ina ne na wancan watan ta ce aini nawa tuni sun sha aiki.
Ranar juma'a tunda safe suka soma shiri,tasowar asuba suka yi,dan haka huɗu tai musu a Kaduna. Sun tsaya a garejin Mando nan Ruƙayya ta sauka,Nura ya rako ta inda yake cewa gashi ba waya a hannunki bare in na shigo unguwarku na kira ki. Ya kamata ace kina da waya fa ba girmanki ba ne. Ta yi dariya sannan ta ce Nuri kenan,Ni nan daka ganni ban so na riƙe waya ba ne, Amma ko ada,na riƙe waya a lokacin da sai wanda ya isa ne yake riƙewa, kuma ma yanzun ban ga dama bane, amma ka bari insha Allahu sai dai kaji calling ɗina. Alƙawari zan kiraka da layina, ya ce shikenan.
Mashin ta samu ɗari uku tun daga Mando gareji zuwa Kabala su kenan kuɗin ta dan haka ta ce muje ai gida nazo kuma bana son shiga mota ga hadari yana ta harhaɗowa gara na isa gida akan kari,bana son ruwa ya taɓa lafiya ta. Sun iso daf da shiga Kabala suna kan titin independence aka soma tsula ruwa nan kuma mashin tayi faci. Ruƙayya ta ce "Oh ni Ruƙy ya zanyi kenan? Ta sauka ta bashi ɗari ukun ya ce "Yaya zaki bani duka gashi bamu kai ba? Ta ce ba komai kaje kawai bari na taka, ya ce ga ruwa? Ta ce kar ka damu,tana tafiya duk ta jiƙe.
Tun daga nesa Sabi'u ya dubi ubangidansa "Ƴallaɓai ga wata can tana buƙatar taimako." Dady ya amsa ba tare da ya ɗago ba, ya ce "A taimaka mata." Ya rufe baki tare da faɗuwar gaba irin wacce bai taɓa ji ba, ya kai hange ga yarinyar da Sabi'u ya ce su taimaka mata,da tazara tsakanin su kuma shekaru baƙwai masu ƙyau bai ganta ba, amma sai da ya gane ta. Ko shakka ba zaya yi ba waccan Pretty ɗin shi ce, domin duk da basa tare kuma idanunshi sun daina ganin ta wannan ba zai hana zuciyarshi kullum karanta surar ta ba, haka yake tsarata kullum.
Sanye take da jallabiya doguwa baƙa haɗe da gyalenta,jaka da takalmin ta ma duk baƙaƙe ne,sai dai ta jiƙe sharkaf har ɗiga take yi.
Jijiyoyin jikin Dady suka tsaya cak, komai ya daina kai saƙo a jikinshi lokacin da ya tsinkayi muryar Ruƙayya suna magana da direba yana cewa baiwar Allah shigo mu taimaka miki ta ce "a'a, nagode Malam na kusa gida gashi kuma duk na jiƙe,ka na jiƙa muku kujera." Ya ce, bakomai shigo taimako ne ai."
Sam Ruƙayya bata ga Dady ba kasancewar motar na waje baya ganin na ciki, amma shi Dady yana ganin ta, tana shaga gaban motar gabanta ya faɗi sai dai har ga Allah bata zata da wani cikin motar ba, don haka sai tayi addu'a a ranta dan kar ta faɗa mugun hannu.
Ta ɓalle maɓallan gaban abayar ta cire sai ga riga T.Shirt mai ɗauka da rubutun N.Y.S.C ta bayyana da wandon ta, ta zage jakar hannunta ta ciro rigar sanyin N.Y.S.C tasa ta ɗaura gyale kamar ɗan ƙwali sannan ta ciro hijabi ƙarami tasa ta maida abaya cikin jaka. Ƙamshin da take shaƙa da faɗuwar gabanta da yaa tsananta sune suka tuna mata da wani abu, tabbas duk inda turaren nan ya fito daga gurin Dady ne, domin tun da suka rabu da Dady bata kuma jin ƙamshin nan ba sai yau.
Ya Allah! Ta faɗa cikin wata muguwar faɗuwar gaba, lokacin da ta dubi madubi ta ga Dady zaune a bayanta. Daga nan bata kuma motsi ba sai ƙwatancen da ta dinga ma direba har lungunsu. Ta ce da direba nagode fa, ya ce bakomai." Ta buɗe mota ta fita.sannan ta saci kallon Dady ta rufe ta tafi, zuciyarta cike da mamakin Dady. Lallai duniya wai kamar Dady ya ganta ya share ta, hawaye ya zubo mata tayi nadamar zuwan ta Kaduna a yau.
Shi kam Dady be ma san anzo har Ruƙayya ta fita ba,haƙiƙa jikinshi ya mutu, zuciyarshi ba ta tare dashi,yana tunanin dama Pretty bata yi aure ba,ko ko tayi ta cigaba da karatun a gidan mijinta? Auren ya mutu ne? Ko ko mijinne ya mutu? Ko ko da auren ta? Wanene zai bashi wannan amsar. Ganin Ruƙayya ya tsorata Dady gami da firgita shi, ta taɗo mishi da wata sabuwar muhimmiyar soyayyar ta.
A fili ya ce "Wannan karon ko Pretty tana da aure ko batada shi, koma wanene mijinta sai ya bai mishi Pretty É—in shi,kai koma ta halin yaya ne shi bazaya barta ba,bai san sun iso gidan Hajja ba sai dai ya ji Sabi'u na cewa.
"Ƴallaɓai mun iso." Ga zaton shi gidan su Ruƙayyan, sai yaga gidan Hajja nan ya soma tunanin kodai mafarki ne? Kai ba mafarki bane. Ya dubi Sabi'u ya ce "ina Pretty ɗin fa? Kan Sabi'u ya ɗaure ya ce,wace Pretty kuma ko wacce muka ɗauko? Dady ya ce "Eh," Sabi'u ya ce ai mun sauke gida Ƴallaɓai baka kula bane." Nan Dady ya wayance ya ce "Ok." Ya shiga gidan Hajja ya bar Sabi'u da mamakin halin da Ƴallaɓai ya shiga kan yarinyar nan,a ranshi ya ce koda yake fa yarinyar ta haɗu dole Oga ya ruɗe har magana yake shi kaɗai ina jin shi.
*** *** *** ***
Yaraf ya zube a kujerar falon Hajja,Saude da ke jira abinci akan centre table tana faɗin "Uban masu gida kasha hanya,in fatan dai baka sha dukan ruwa ba?" Da ƙyar ya ce sannu Saude ina Hajja? Ta ce gata nan zuwa tana ɗauro alwala ne, sama-sama suka gaisa da Hajja don haka ta tasa shi da tambayoyi jikinne Yusufa ko ko gajiya ce?.
Numfashinsa yana sama-sama ya ce "Duk aƙwai." Ta ce "To ai gara ka je asibiti ko? Ya ce "wannan bana asibiti bane ku barni na huta bana son magana." Duk shiru suka yi,yana ƙwance har aka kira magriba, ya yunƙura da ƙyar ya tafi sallah. Hollandia kawai ya ɗaɗɗaka baici komai ba ya kira direba a waya ya zo ya ɗauke shi. Hajja ta yi tayi ya ci abinci kasancewar ya yi azumi ya ce "Kiyi haƙuri Hajja ba zan iya cin komai ba, ina cikin damuwa ki min addu'a." Ido ta bishi da shi har ya shiga cikin mota sam baya tare da tunanin shi, tunanin shi kawai ta ina zaya fara da wannan lamarin.?
A hankali ya ce "Sabi'u kaini gida gurin Momy."