Sashe 1
Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
 *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 1
Shiri sosai tayi dama Sarkin gayu ce tayi ƙyau ƙwarai dan tana da irin jikin nan da ake ce ma karuwan jiki,ko wane kaya tasa sai ya yi mata ƙyau an ɗebe su sai hotel ɗin da aka tsara haɗaɗɗiyar dinner, wacce abokan Ango suka shirya guri ya yi guri sanda suka isa,jin gaban ta bai faɗi ba yasa ta shiga cikin ƙwanciyar hankali suna zaune an soma ciye-ciye . Can sai taji gabanta ya yi mugun faɗuwa take ta ji komai ya ginshe ta duk da waƙar da mawaƙin keyi da farko ta shiga ranta, amma yanzu sai taji komai ya tsaya mata cak. Da sauri ta miƙe Sadiya da Munira suka dube ta, ina zaki? Ta ce ina zuwa,can bayan wasu ƴan labulaye taje daga inda take tana duban ƙofa. Haka kawai taji cewa yanzun zai shigo.
*** **** **** ****
Dady ya fito wanka ya kuma gajiye yake jin shi ba dan bai samu halartar ko ɗaya daga cikin programs ɗin bikin ba da zaya huta ne don yayi azumi yau kuma a wahale yake ya ɗan ja tsaki shima yana tunanin haka nan zaya haƙura asa bikinshi da Zainab ya gaji da azumin nan shi kanshi yasan yana buƙatar mace kuma yana ganin kamar yana da ƙarfin sha'awa shiyasa gara ya yi auren tunda wadda yake so bazai samu ko ganinta ba bare har ya aura.
Shadda kalar blue hularshi da duk kayan da yasa blue ne,rafar ƴan ɗari biyar ya zuba cikin aljihu ya fesa turare ya ɗauki key ɗin Hummer ya fito. A falo ya samu Sunday yana zuba Hollandia cikin firji, ya ce "Sunday kai min ɗaya cikin motar daka goge min", ya ce "Ok sir." Ya ɗauka ya fita yana matuƙar mamakin irin son da ubangidan nashi kema wannan Hollandia ya kamata campanyn ta suyi mishi ƙyauta ta musamman,ko dan tsananin ƙaunar da yake mata."
Gidan su Zainab Dady ya wuce a phone ya kirata ta fito bayan tayi sallama da mahaifiyarta, Hajiyarta tana tsananin son Æ´arta Zainab ta auri Dady ba dan komai ba sai don iyayenshi sun tara, haka kuma shima ya tara sai godiya.
Yana daga cikin mota yana kallonta ta nufoshi cikin wani leshi ɗan gaske mai kalar green yasha ado da zare silba haka sarƙa da ƴankunne suma silba jaka da takalmi sai wani ɗan mayafi ƙarami duk farare ta yi ƙyau sosai sha'awarta ta ƙaru a zuciyarshi, ta shiga motar bayan ya buɗe mata ƙamshin jikinsu ya buɗe su,ta dube shi My dear har na zaci ka fasa zuwa dani, ya ce "saboda me?" Ta ce naga goma ta wuce sannan baka kira phone ɗina ba, ya ce ina can ina tunanin yakamata mu ma azo mana dinner fa dan na gaji da rungume filo yakamata nima nasan halin da nake ciki, daɗi ya kamata ta ce ba na ce maka ba tuni, amma ka ƙi wai na jira ka,Ƙila kafi son ƙwana da filon shiyasa." Ya shafi fuskarshi ranar asabar za'a kawo lefe da komai tunda Allah yasa sun san komai dama nine matsalar kuma yanzu nima ina buƙatar auran,sati Uku zamu sa fa.?"
Cikin zumuɗi Zainab ta ce "Ya yi nima na matuƙar ƙosawa."
Ya dubeta "dame kika ƙosa?" Ta ce "Da abin da yake hana ka bacci." Kai ya girgiza yana mamakin Zainab, Sam batada irin kunyar nan ta mata, ya tuna Pretty ɗin shi, ita kam kowane lokaci ya yi mata wata magana mai ɗan nauyi takan rufe fuskarta da tafukan hannayenta ta ce,kai ko? Ita kam Zainab sai dai ta biyeshi suyi,hakan baya birgeshi yana son mace mai kunya da jan aji.
Suna shiga gurin dinner yaji gabanshi ya faɗi inda sabo ya saba,ba wata Pretty ɗin shi a nan gurin, zuciyarshi ce dai kullum tana ayyana mishi sai gabanshi ya dinga faɗuwa, haka ya raya a ranshi don haka sai kawai, ya shige, sun samu an daɗe da soma dinner, amma duk da haka sai da aka sanar da zuwanshi a matsayin babban abokin ango akan idon Ruƙayya suka shigo, tana dubansu san da suka zarce kusa da ango suka zauna yayin da Zainab ta maida ɗuwawunta gurin da Ruƙayya ta tashi, gaban Ruƙayya ya faɗi ta tsorata da ganin Zainab domin ta gane wacce suka haɗu a saloon ce, ta gode Allah da yasa ta tashi don haka can ta fita duk da tsoron dake cike fal a ranta haka ta zauna a harabar Hotel ɗin tunda ga haske tamkar rana.
Sadiya ta dubi Munira "M Bash har yanzu kusan awa Ruky M bata dawo ba fa." Munira ta ce "Kai gaskiya ki je ki duba ta, tunda ba phone a hannunta bare ma mu kira."
Son Guy (kamar yadda suke kiran Dady) ya dubi Al-Mustapha.
"Ina neman afuwa Musty bamu samu isowa akan kari ba." Zainab ta ce "Ya hidimomi ango?"
Al-Mustapha ya ce da godiya.
Zainab ta dubi Munira "Amarya ya jama'a?" Munira bata gane Zainab ba, har suka gaisa suka gaisa da Sadiya basu gane ta ba, Zainab ta ce "Naga baku gane ni ba ko?" Sadiya ta ce "Ni dai ina son tuna inda muka haɗu." Zainab ta ce "A saloon." Nan take suka tuna ta, amarya sun gaisa da Son Guy inda ya yi mata ƴar tsokana. Zainab ta ce "ina ɗayar nan kuma mai gashi?." Sadiya ta ce "kina nufin Ruƙy M ko?" Ta ce "Yes ita kam bata zo ba?" Ta ce yanzun nan ta tashi ko ina ta shiga Oho, Zainab ta ce "Ashe zamu gaisa." Munira ta ce "Armaya'u ki je ki duba ta kin san fa Ruƙy ƴar daru ce zata iya tafiya gida."
Al-Mustapha ya ce "Kai Ruƙy ɗin nan tana da shagwaɓa,da ƙyar dama ta zo.
Shiru Dady ya yi yana ƴan dube-dube tamkar baisan mai suke cewa ba, amma kunnen shi yana gurin su,a ranshi kuma sai yaji yana mai tsananin son yaga Ruƙy M ɗin nan, wancan karan ya kuskure ganinta sakamakon wanka da tashi ga, yanzu kan shi sai fa yaga kalarta, shi kam dama yana matuƙar girmama mai sunan ta,yasha alwashin in har ya haifi ƴa mace sunan ta Ruƙayya. Nan ya tuno ma kanshi son Ruƙayya take hankalinshi ya tashi kanshi ya shiga sarawa nan ya ji zuciyarshi ta tsani duk wata mace, duk hirar da Al-Mustapha yake yi mishi sam bai ji ba,sai da Zainab ta ce My dear ya kamata ka duba masu waƙar nan tuntuni sai waƙa suke yi. Nan ya tashi cikin sanyin jiki yana musu liƙi, Zainab ta zuba mishi ido tana tsananin son shi ita ma nan take ta tashi taje tana mishi liƙi, Ango da amarya suma suka taso suna ma su Dady liƙi nan fa guri ya kaure mai waƙa sai rerawa yake yi.
Ruƙy wacce abin duniya ya dama sai gizo Dady ke mata tana ganin san da suke shigowa da Zainab fuskarshi wasai ƙyawun shi ya ƙaru fiye da da, wata kamala ta musamman ta sauka a fuskar shi, ya zama namiji sosai ga wani ɗan tumbin kuɗi da ya fito ya yi mishi ƙyau,a da sam bata son tumbi amma na Dady ya yi mishi ƙyau.
Hawaye suka zubo mata lallai Dady ya karya alƙawari. Ta tuna da yanda suka so juna ashe duk na baki ne,sai yanzu ma tayi wani tunani, gaskiya ya kamata ma ta gane tuntuni dan me ya hana ya neme ta tuntuni bayan rabuwar su? Kuma phone ɗin da ya bata me ya hana shi kiranta akan layin. Har ta tafi makarantar ƙwana? Duk ma shekarun nan da yana sonta daya neme ta, don haka taba kanta baki tare alƙawari sauraron duk wani wanda ya zo da sunan sonta. Kuma daga yau tayi banƙwana da garin Abuja gobe tana tafiya shikenan,in ba kuma M Bash bace ta haihu bata ƙara zuwa bare ta ganshi. Kai tana ganin ma gara ta je ta auri talaka ɗan'uwanta ya fiye mata ƙwanciyar hankali. Ga Nasir tela duk da ya yi aure har da yara uku,yana nan yana nacin ta har tayi degree ita kam yanzu zata daina biyewa ƴaƴan masu dashi ɗin nan,gara Armaya'u da M Bash suna da halin shiga law school ita kam zata je service ɗin ta ya fiye mata tana gamawa ta nemi aiki koma a ina ne kafin Allah ya bata miji, tunani bar katai sun cika ta har san da aka tashi.
Tana ganin mutane sun soma fitowa, sai ta koma can gurin motar da suka zo cikinta. Ta ganin su Armaya'u da sauran ƙawayen suna sallama da Zainab, yayin da Dady dasu Al-Mustapha suka nufo gurin da take. Tsoro ya kamata da sauri ta zaga bayan motocin ta ɓoye bayan wata.
Jikin wadda ta ɓoye ya shiga tana jin san da yake cewa Musty "Musty Allah ya bada zuriya ɗayyiba, kayi ƙoƙarin samun Baby a yau dare na farko." dariya suka saki sauran abokan suna cewa "Gaskiya ne Son Guy." Ya ce Zee zo muje dare nayi fa." Ta na barwa su Sadiya saƙon gaisuwa zuwa ga Ruƙayya, ta zo tana cewa,My dear mu tafi ko? Ya ce shiga, ta tsugunna tana jin su a bayan motar da bata zata tashi bace sai da taji ya tashi motar ta koma bayan wata da sauri.
Yana bari gurin ta miƙe tana maida numfashi taje gurinsu Munira dake ta shishshiga mota. Sadiya har tsoro ta ji ta ce daga ina? Ruƙy ta ce ku muje kawai basu jima a gidan Munira ba Abokan ango suka ƙwashe su sai gidan Mom. Sun cika su uku Munira M Bash, Sadiya Armaya'u, Ruƙayya M Sani, tayi ta yi da safe su biyo kafin su wuce, sun ce to dan ta ƙwantar da hankalinta, amma ba zasu dawo ba saboda Armaya'u Kano ta nufa, Mom ta haɗa su da kayan biki da kuma godiya tare da cewa suyi ma iyayen su ban gajiya. Dan Umma ta zo Hajiyan su Sadiya ma tazo.
Tunda suka dawo bikin Munira kullum maganar aure Umma da Affa suke mata,ita kam ta ƙosa a tura su service. Takardun na fitowa sai taga ita Legos aka tura ta, bata damu ba dan ita burinta shi ne ta matsa daga gidan.
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
Page 1
Shiri sosai tayi dama Sarkin gayu ce tayi ƙyau ƙwarai dan tana da irin jikin nan da ake ce ma karuwan jiki,ko wane kaya tasa sai ya yi mata ƙyau an ɗebe su sai hotel ɗin da aka tsara haɗaɗɗiyar dinner, wacce abokan Ango suka shirya guri ya yi guri sanda suka isa,jin gaban ta bai faɗi ba yasa ta shiga cikin ƙwanciyar hankali suna zaune an soma ciye-ciye . Can sai taji gabanta ya yi mugun faɗuwa take ta ji komai ya ginshe ta duk da waƙar da mawaƙin keyi da farko ta shiga ranta, amma yanzu sai taji komai ya tsaya mata cak. Da sauri ta miƙe Sadiya da Munira suka dube ta, ina zaki? Ta ce ina zuwa,can bayan wasu ƴan labulaye taje daga inda take tana duban ƙofa. Haka kawai taji cewa yanzun zai shigo.
*** **** **** ****
Dady ya fito wanka ya kuma gajiye yake jin shi ba dan bai samu halartar ko ɗaya daga cikin programs ɗin bikin ba da zaya huta ne don yayi azumi yau kuma a wahale yake ya ɗan ja tsaki shima yana tunanin haka nan zaya haƙura asa bikinshi da Zainab ya gaji da azumin nan shi kanshi yasan yana buƙatar mace kuma yana ganin kamar yana da ƙarfin sha'awa shiyasa gara ya yi auren tunda wadda yake so bazai samu ko ganinta ba bare har ya aura.
Shadda kalar blue hularshi da duk kayan da yasa blue ne,rafar ƴan ɗari biyar ya zuba cikin aljihu ya fesa turare ya ɗauki key ɗin Hummer ya fito. A falo ya samu Sunday yana zuba Hollandia cikin firji, ya ce "Sunday kai min ɗaya cikin motar daka goge min", ya ce "Ok sir." Ya ɗauka ya fita yana matuƙar mamakin irin son da ubangidan nashi kema wannan Hollandia ya kamata campanyn ta suyi mishi ƙyauta ta musamman,ko dan tsananin ƙaunar da yake mata."
Gidan su Zainab Dady ya wuce a phone ya kirata ta fito bayan tayi sallama da mahaifiyarta, Hajiyarta tana tsananin son Æ´arta Zainab ta auri Dady ba dan komai ba sai don iyayenshi sun tara, haka kuma shima ya tara sai godiya.
Yana daga cikin mota yana kallonta ta nufoshi cikin wani leshi ɗan gaske mai kalar green yasha ado da zare silba haka sarƙa da ƴankunne suma silba jaka da takalmi sai wani ɗan mayafi ƙarami duk farare ta yi ƙyau sosai sha'awarta ta ƙaru a zuciyarshi, ta shiga motar bayan ya buɗe mata ƙamshin jikinsu ya buɗe su,ta dube shi My dear har na zaci ka fasa zuwa dani, ya ce "saboda me?" Ta ce naga goma ta wuce sannan baka kira phone ɗina ba, ya ce ina can ina tunanin yakamata mu ma azo mana dinner fa dan na gaji da rungume filo yakamata nima nasan halin da nake ciki, daɗi ya kamata ta ce ba na ce maka ba tuni, amma ka ƙi wai na jira ka,Ƙila kafi son ƙwana da filon shiyasa." Ya shafi fuskarshi ranar asabar za'a kawo lefe da komai tunda Allah yasa sun san komai dama nine matsalar kuma yanzu nima ina buƙatar auran,sati Uku zamu sa fa.?"
Cikin zumuɗi Zainab ta ce "Ya yi nima na matuƙar ƙosawa."
Ya dubeta "dame kika ƙosa?" Ta ce "Da abin da yake hana ka bacci." Kai ya girgiza yana mamakin Zainab, Sam batada irin kunyar nan ta mata, ya tuna Pretty ɗin shi, ita kam kowane lokaci ya yi mata wata magana mai ɗan nauyi takan rufe fuskarta da tafukan hannayenta ta ce,kai ko? Ita kam Zainab sai dai ta biyeshi suyi,hakan baya birgeshi yana son mace mai kunya da jan aji.
Suna shiga gurin dinner yaji gabanshi ya faɗi inda sabo ya saba,ba wata Pretty ɗin shi a nan gurin, zuciyarshi ce dai kullum tana ayyana mishi sai gabanshi ya dinga faɗuwa, haka ya raya a ranshi don haka sai kawai, ya shige, sun samu an daɗe da soma dinner, amma duk da haka sai da aka sanar da zuwanshi a matsayin babban abokin ango akan idon Ruƙayya suka shigo, tana dubansu san da suka zarce kusa da ango suka zauna yayin da Zainab ta maida ɗuwawunta gurin da Ruƙayya ta tashi, gaban Ruƙayya ya faɗi ta tsorata da ganin Zainab domin ta gane wacce suka haɗu a saloon ce, ta gode Allah da yasa ta tashi don haka can ta fita duk da tsoron dake cike fal a ranta haka ta zauna a harabar Hotel ɗin tunda ga haske tamkar rana.
Sadiya ta dubi Munira "M Bash har yanzu kusan awa Ruky M bata dawo ba fa." Munira ta ce "Kai gaskiya ki je ki duba ta, tunda ba phone a hannunta bare ma mu kira."
Son Guy (kamar yadda suke kiran Dady) ya dubi Al-Mustapha.
"Ina neman afuwa Musty bamu samu isowa akan kari ba." Zainab ta ce "Ya hidimomi ango?"
Al-Mustapha ya ce da godiya.
Zainab ta dubi Munira "Amarya ya jama'a?" Munira bata gane Zainab ba, har suka gaisa suka gaisa da Sadiya basu gane ta ba, Zainab ta ce "Naga baku gane ni ba ko?" Sadiya ta ce "Ni dai ina son tuna inda muka haɗu." Zainab ta ce "A saloon." Nan take suka tuna ta, amarya sun gaisa da Son Guy inda ya yi mata ƴar tsokana. Zainab ta ce "ina ɗayar nan kuma mai gashi?." Sadiya ta ce "kina nufin Ruƙy M ko?" Ta ce "Yes ita kam bata zo ba?" Ta ce yanzun nan ta tashi ko ina ta shiga Oho, Zainab ta ce "Ashe zamu gaisa." Munira ta ce "Armaya'u ki je ki duba ta kin san fa Ruƙy ƴar daru ce zata iya tafiya gida."
Al-Mustapha ya ce "Kai Ruƙy ɗin nan tana da shagwaɓa,da ƙyar dama ta zo.
Shiru Dady ya yi yana ƴan dube-dube tamkar baisan mai suke cewa ba, amma kunnen shi yana gurin su,a ranshi kuma sai yaji yana mai tsananin son yaga Ruƙy M ɗin nan, wancan karan ya kuskure ganinta sakamakon wanka da tashi ga, yanzu kan shi sai fa yaga kalarta, shi kam dama yana matuƙar girmama mai sunan ta,yasha alwashin in har ya haifi ƴa mace sunan ta Ruƙayya. Nan ya tuno ma kanshi son Ruƙayya take hankalinshi ya tashi kanshi ya shiga sarawa nan ya ji zuciyarshi ta tsani duk wata mace, duk hirar da Al-Mustapha yake yi mishi sam bai ji ba,sai da Zainab ta ce My dear ya kamata ka duba masu waƙar nan tuntuni sai waƙa suke yi. Nan ya tashi cikin sanyin jiki yana musu liƙi, Zainab ta zuba mishi ido tana tsananin son shi ita ma nan take ta tashi taje tana mishi liƙi, Ango da amarya suma suka taso suna ma su Dady liƙi nan fa guri ya kaure mai waƙa sai rerawa yake yi.
Ruƙy wacce abin duniya ya dama sai gizo Dady ke mata tana ganin san da suke shigowa da Zainab fuskarshi wasai ƙyawun shi ya ƙaru fiye da da, wata kamala ta musamman ta sauka a fuskar shi, ya zama namiji sosai ga wani ɗan tumbin kuɗi da ya fito ya yi mishi ƙyau,a da sam bata son tumbi amma na Dady ya yi mishi ƙyau.
Hawaye suka zubo mata lallai Dady ya karya alƙawari. Ta tuna da yanda suka so juna ashe duk na baki ne,sai yanzu ma tayi wani tunani, gaskiya ya kamata ma ta gane tuntuni dan me ya hana ya neme ta tuntuni bayan rabuwar su? Kuma phone ɗin da ya bata me ya hana shi kiranta akan layin. Har ta tafi makarantar ƙwana? Duk ma shekarun nan da yana sonta daya neme ta, don haka taba kanta baki tare alƙawari sauraron duk wani wanda ya zo da sunan sonta. Kuma daga yau tayi banƙwana da garin Abuja gobe tana tafiya shikenan,in ba kuma M Bash bace ta haihu bata ƙara zuwa bare ta ganshi. Kai tana ganin ma gara ta je ta auri talaka ɗan'uwanta ya fiye mata ƙwanciyar hankali. Ga Nasir tela duk da ya yi aure har da yara uku,yana nan yana nacin ta har tayi degree ita kam yanzu zata daina biyewa ƴaƴan masu dashi ɗin nan,gara Armaya'u da M Bash suna da halin shiga law school ita kam zata je service ɗin ta ya fiye mata tana gamawa ta nemi aiki koma a ina ne kafin Allah ya bata miji, tunani bar katai sun cika ta har san da aka tashi.
Tana ganin mutane sun soma fitowa, sai ta koma can gurin motar da suka zo cikinta. Ta ganin su Armaya'u da sauran ƙawayen suna sallama da Zainab, yayin da Dady dasu Al-Mustapha suka nufo gurin da take. Tsoro ya kamata da sauri ta zaga bayan motocin ta ɓoye bayan wata.
Jikin wadda ta ɓoye ya shiga tana jin san da yake cewa Musty "Musty Allah ya bada zuriya ɗayyiba, kayi ƙoƙarin samun Baby a yau dare na farko." dariya suka saki sauran abokan suna cewa "Gaskiya ne Son Guy." Ya ce Zee zo muje dare nayi fa." Ta na barwa su Sadiya saƙon gaisuwa zuwa ga Ruƙayya, ta zo tana cewa,My dear mu tafi ko? Ya ce shiga, ta tsugunna tana jin su a bayan motar da bata zata tashi bace sai da taji ya tashi motar ta koma bayan wata da sauri.
Yana bari gurin ta miƙe tana maida numfashi taje gurinsu Munira dake ta shishshiga mota. Sadiya har tsoro ta ji ta ce daga ina? Ruƙy ta ce ku muje kawai basu jima a gidan Munira ba Abokan ango suka ƙwashe su sai gidan Mom. Sun cika su uku Munira M Bash, Sadiya Armaya'u, Ruƙayya M Sani, tayi ta yi da safe su biyo kafin su wuce, sun ce to dan ta ƙwantar da hankalinta, amma ba zasu dawo ba saboda Armaya'u Kano ta nufa, Mom ta haɗa su da kayan biki da kuma godiya tare da cewa suyi ma iyayen su ban gajiya. Dan Umma ta zo Hajiyan su Sadiya ma tazo.
Tunda suka dawo bikin Munira kullum maganar aure Umma da Affa suke mata,ita kam ta ƙosa a tura su service. Takardun na fitowa sai taga ita Legos aka tura ta, bata damu ba dan ita burinta shi ne ta matsa daga gidan.