Sashe 24
Fattomah Book Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da mamaki ta ƙaraso tana kallonsa murmushi ya sakar mata itama ta mayar masa amma kana ganinta kasan mamakine fal fuskarta, gaisawa suka yi ya ce"sannu kinganni gidanku ko?" gyada masa kai Aysha ta yi ta ce"Eh mana kamar na taɓa ganinka" murmushi kawai Kamal ya yi ya ce"Eh mana kece ƙawar Fattomah ko?" gyaɗa masa kai tayi nan ma ya ce"daman ina son na tambayeki ne" Aysha ta ce"Allah yasa na sani" gyara tsaiwarsa ya yi sannan ya ce
"Daman Fattomah ce bana ganinta kwana biyu kuma na kira wayarta several times switch up to shine nazo school ɗinku jiya na tambayi wasu yan class ɗin ku suka cemin kece best friend ɗinta shine nazo na tambayeki ko lafiya?" numfasawa Aysha ta yi sai kuma ta ce"wlh nima abinda ke damuna kenan ina cikin tashin hankali yau kusan sati biyu kenan banga Fattum ba kuma bansan inda zan sameta ba bata zuwa makaranta kuma babu waya ahannunta duk na damu" da mamaki ya ce"kema bakisan inda take ba toh, kina ƙawarta bakisan gidan su ba?" hawayen da yake zubowa afuskarta ta goge sannan ta ce asanyaye
"Ai bata gidansu saboda babanta ya rasu Mamanta kuma bata garin nan tana gidan relative ɗinta kuma ban sani ba" dafe kansa ya yi cikin ɗunbin damuwa ya ce"inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun wlh ina matukar son ganin yarinyar nan yanzu babu inda zan ganta hasbunallah" kallonsa kawai Aysha tayi dan ita tama fishi son ganin Fattum tunda suke basu taɓa rabuwa irin haka ba koda kuwa hutu aka yi Aysha zataje gurinta su zauna suyita hira amma sai gashi cikin lokaci ƙanƙani ta nemata ta rasa, shuru ya yi na wasu mintuna sai kuma ya ce"shikenan zan tafi in sha zan sake shigowa naji ko akwai wani abu da kika samu" okay Aysha ta ce masa sannan ya zaro rafar yan ɗari biyu a aljihunsa yana kallonta ya miƙa mata ya ce"take this" girgiza kanta ta yi ta ce"A'a nagode sosai" murmushi ya yi sannan ya ajiye mata kuɗin gefenta ya bar wajen tana nan tsaye har taga tashin motarsa sannan ta ɗauki kuɗin ta shige gida.
Tsaki Saleem ya yi ya ce"kai ma ai kayi ganganci har zaka bari baka karɓi address nata ba to yanzu gashi babu wayar kuma bakasan inda take ba" hannunsa ya sanya ya wargatsa gashin kansa sannan ya ce"idan har inada rabon aurenta nasan tabbas watarana zamu sake haɗuwa naji haka cikin rai na" gyaɗa kansa ya yi ya ce"Ehh Lallai to Allah ya tabbatar da Alkhairi" jingina ya yi da jikin kujerar ya ce"oh god!!" kallonsa kawai Saleem ya yi sannan ya girgiza kai.
Kallonta kawai Jawaad yake har ta karasa sakkowa daga benen tafiya take kamar wacce kwai ya fashewa ajiki har ta ƙaraso wajensu, tsugunawa tayi tana cize laɓe saboda wata irin azaba data ziyarci kwakwalwarta, Imad ne ya ce"tashi anan wajen" toh ta ce sannan ta kama kujera tana niyyar tashi dakyar ta miƙe ta haɗa wani uban gumi ta zauna kan kujerar tana maida numfashi, Jawaad ne ya ce"bakida lafiya ne Fattum?" girgiza masa kai ta yi ya ce"A'a ki faɗa min gaskiya mene yake damunki" a hankali ta kallesa hawaye na taruwa a idanunta ta ce"yaya ƙafata ciwo take kullum haka" Jawaad ya ce"Ayyah sannu kinji bari zan kawo miki magani sai ki dinga shafawa okay?" gyaɗa masa kai ta yi Imad ya ce"have you eaten?" girgiza kanta ta yi ya ce"tashi kije ki ɗebi abinci" kwaɓe fuskarta ta yi bata ce komai ba, ganin yanda tayi yasa ya ce"ko maid ta kawo miki?" girgiza masa kai ta yi ta ce"A'a na ƙoshi ni" haɗe rai ya yi sannan ya kira wata maid cikeda ladabi ta ce"gani sir" "ki kawo abinci amma bamai nauyi ba something liquid haka" okay ta ce sannan ta juya tabar wajen.
Juyi kawai take kan gadon amma ta kasa bacci banda ciwo babu abinda cikinta ke mata gashi daman wajen ya yi wani irin ja da kuma kumbura tun ranar da Imad ya daketa koda wasa bata taɓa nuna wani abu agabansa wanda zai sa ya fahimci haka ba dakyar take iya taka ƙafarta duk jijiyoyin wajen sun riƙe haka take kasancewa duk dare cikin rashin samun bacci wadattace,
Fitowar ta kenan daga wanka tana tsaye tana ƙoƙarin shafa mai ajikinta batasan sanda ya shigo ɗakin ba har ta gama shafa man sannan ta zame towel ɗin da niyyar ɗaukan rigarta
"Keeeeee!!"
Afirgice ta juyo tana kallonsa dan batasan sanda ta karasa yarda towel ɗinba hankali tashe yake kallon cikin nata yama kasa furta komai ita kuwa fashewa tayi da kuka tana ƙoƙarin rufe jikinta batasan ko kaɗan tunanin Imad bai zo wajen ba, tsugunawa ya yi gabanta yana kai hannunsa kan cikin nata, sosai abun ya bashi mamaki haɗi da tashin hankali dan bai taɓa ganin irin abun azahiri ba saidai akaratu bakinsa na rawa ya furta
"Keeee..keee...Mee..mene wannan?"
Cikin kukan ta ce"dan Allah Uncle kayi haƙuri dan Allah karka dakeni wlh mutuwa zanyi dan Allah Uncle" miƙewa ya yi kawai bai ce komai ba ya miƙa mata rigarta sannan ya juya ya yi waje, rigar ta sanya har sannan tana ci-gaba da kukanta dan gani take kamar sake dukanta zai yi, shi kuwa rasa abinda zai yi, ya yi duk hankalinsa ya tashi ko yaushe ta samu wannan ciwon???.
Suna shiga cikin asibitin aka shige da'ita emergency Imad kuwa ya kasa zaune ya kasa tsaye dan tashin hankalinsa ɗaya abinda zai cewa Daddy idan ya tambaye shi ya kuma san halin Daddyn nasa, Jawaad ne ya ƙara so yana kallonsa amma ya kasa ce masa komai dan ransa a matuƙar ɓace yake kusan 5mins suna tsaye kafin ya ƙaraso yana kallonsa ya ce"friend wane bashida lafiya?" asanyaye Imad ya ce"wlh yarinya ce kuma gaskiya abun ba karami bane please kaje ka gani" okay ya ce sannan ya kalli Jawaad da sauri ya sake kallonsa ganin kamar yaso ya tuna inda ya sanshi kallonsa shima Jawaad ya yi amma bai ce komai ba shima Kamal shigewa ya yi saboda ya duba mara lafiyar.
Kusan mutuwar tsaye Kamal ya yi ganin Fattomah kwance an sanya mata oxygen bai taɓa tsammatar haka ba dukda ya yi mamakin ganin Jawaad amma bai ɗauka ita ce batada lafiyar ba tunaninshi ɗaya yanzu mene ne alaƙarta da abokinsa Imadudden har zai kawota asibiti shidai yasan shi kaɗai iyayensa suka haifa bare yace ƙanwarsa ce wannan tunanin shine abinda ya sanya duk ya zama moody har aka shiga da yarinyar domin dubata.
Da sauri Jawaad ya fizge takardar hannun Kamal ɗin cikin son gazgata abinda Kamal ɗin yake faɗa ji ya yi numfashinsa na neman barin jikinsa lokacin daya gama karanta takardar bai taɓa tunanin haka ba koda kuwa cikin mafarki ne zama ya koma ya yi jin jiri na neman ɗibansa ba shi kaɗai ba shima kansa Kamal ya kasa magana ji yake inama ace mafarkine wannan abinda yake faruwa ɗin ba gaskiya ba, inama ya farka daga wannan mafarkin wanda yake neman tarwatsa masa farin cikinsa zuciyarsa da kwakwalwarsa duk a dagule suke kuma cikeda tambayoyi masu tarin yawa. Kamar wani zaki haka ya mike yana riƙeda takardar ya fice daga cikin office ɗin, shigowarsa kenan bayan yaje gida dan ɗauko mata kaya ganin Jawaad tsaye ya haɗe hannayensa a ƙirji yasa ya ƙara sa ya dafa shi cikin sanyin murya ya ce"Jawaad ya jikin nata?"
"Ka kyauta Imad!! Ka kyauta wannan shine cika alƙawari haka shine daidai wllh ban taɓa zaton haka daga gareka ka koda kuwa a mafarki ne ban ɗauka zaka kasance mai son zuciya kuma mara imani har haka ba nasan kawai Kanada saurin fushi da fusata amma ban yi zaton kai azzalumi neba Imadudden kaci amana kayi yaudara kuma kayi zalunci wanda kai ma kasan Ubangiji bazai taɓa barinka ba kai ɗin azzalumi ne!!!"
Kallonsa kawai Imad yake yi tunda ya fara maganar dan baisan abinda yake nufi ba kuma baisan akan me yake magana duk sai ya ruɗe gashi Jawaad sai surfa masifa yake ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba
"Ka sanar dani wai mene ne abinda ke faruwa Jawaad?" murmushin takaici Jawaad ya yi sannan ya miƙa masa takardar hannunsa, ahankali ya warwareta ya fara karantawa anutse, wani irin gumi ne ki tsassafo masa tundaga tsakiyar kansa da sauri ya kalli Jawaad yaga shi yake kallo da alamar tuhuma, zama Imad ya yi kan wata kujera daya gani wajen dan ji yake kamar ya yi hauka ya rasa mene ne yake shirin faruwa farin ciki ya kamata ya yi ko kuwa baƙi ciki???, damuwa ce fal ransa da kuma tashin hankali dan baisan da wane idanu zai tari Daddy ba shine babban tashin hankalinsa, kallonsa Jawaad ya yi sai kuma ya ce
"Imad why??why??why??, Dan Allah wace irin tsana ka yiwa wannan yarinyar?, mene laifinta daka yanke shawarar rabata da farin ciki?, me ta aikata maka wanda kake tunanin ta cancanci wannan hukuncin?, akan wane dalili ne Imad?" Dafe kansa ya yi dan bashida amsar da zai bawa Jawaad a halin yanzu dan kome zai faɗa masa bazai ɗauka ba. Miƙewa Imad ya yi bai ce komai ba ya yi waje yana haɗa hanya saboda ciwon da kansa ke masa, da kallo Jawaad da bisa yasan tunda ya yi haka bazai faɗa masa sannan bane shiyasa shima ya rabu dashi.
"Daman Fattomah ce bana ganinta kwana biyu kuma na kira wayarta several times switch up to shine nazo school ɗinku jiya na tambayi wasu yan class ɗin ku suka cemin kece best friend ɗinta shine nazo na tambayeki ko lafiya?" numfasawa Aysha ta yi sai kuma ta ce"wlh nima abinda ke damuna kenan ina cikin tashin hankali yau kusan sati biyu kenan banga Fattum ba kuma bansan inda zan sameta ba bata zuwa makaranta kuma babu waya ahannunta duk na damu" da mamaki ya ce"kema bakisan inda take ba toh, kina ƙawarta bakisan gidan su ba?" hawayen da yake zubowa afuskarta ta goge sannan ta ce asanyaye
"Ai bata gidansu saboda babanta ya rasu Mamanta kuma bata garin nan tana gidan relative ɗinta kuma ban sani ba" dafe kansa ya yi cikin ɗunbin damuwa ya ce"inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun wlh ina matukar son ganin yarinyar nan yanzu babu inda zan ganta hasbunallah" kallonsa kawai Aysha tayi dan ita tama fishi son ganin Fattum tunda suke basu taɓa rabuwa irin haka ba koda kuwa hutu aka yi Aysha zataje gurinta su zauna suyita hira amma sai gashi cikin lokaci ƙanƙani ta nemata ta rasa, shuru ya yi na wasu mintuna sai kuma ya ce"shikenan zan tafi in sha zan sake shigowa naji ko akwai wani abu da kika samu" okay Aysha ta ce masa sannan ya zaro rafar yan ɗari biyu a aljihunsa yana kallonta ya miƙa mata ya ce"take this" girgiza kanta ta yi ta ce"A'a nagode sosai" murmushi ya yi sannan ya ajiye mata kuɗin gefenta ya bar wajen tana nan tsaye har taga tashin motarsa sannan ta ɗauki kuɗin ta shige gida.
Tsaki Saleem ya yi ya ce"kai ma ai kayi ganganci har zaka bari baka karɓi address nata ba to yanzu gashi babu wayar kuma bakasan inda take ba" hannunsa ya sanya ya wargatsa gashin kansa sannan ya ce"idan har inada rabon aurenta nasan tabbas watarana zamu sake haɗuwa naji haka cikin rai na" gyaɗa kansa ya yi ya ce"Ehh Lallai to Allah ya tabbatar da Alkhairi" jingina ya yi da jikin kujerar ya ce"oh god!!" kallonsa kawai Saleem ya yi sannan ya girgiza kai.
Kallonta kawai Jawaad yake har ta karasa sakkowa daga benen tafiya take kamar wacce kwai ya fashewa ajiki har ta ƙaraso wajensu, tsugunawa tayi tana cize laɓe saboda wata irin azaba data ziyarci kwakwalwarta, Imad ne ya ce"tashi anan wajen" toh ta ce sannan ta kama kujera tana niyyar tashi dakyar ta miƙe ta haɗa wani uban gumi ta zauna kan kujerar tana maida numfashi, Jawaad ne ya ce"bakida lafiya ne Fattum?" girgiza masa kai ta yi ya ce"A'a ki faɗa min gaskiya mene yake damunki" a hankali ta kallesa hawaye na taruwa a idanunta ta ce"yaya ƙafata ciwo take kullum haka" Jawaad ya ce"Ayyah sannu kinji bari zan kawo miki magani sai ki dinga shafawa okay?" gyaɗa masa kai ta yi Imad ya ce"have you eaten?" girgiza kanta ta yi ya ce"tashi kije ki ɗebi abinci" kwaɓe fuskarta ta yi bata ce komai ba, ganin yanda tayi yasa ya ce"ko maid ta kawo miki?" girgiza masa kai ta yi ta ce"A'a na ƙoshi ni" haɗe rai ya yi sannan ya kira wata maid cikeda ladabi ta ce"gani sir" "ki kawo abinci amma bamai nauyi ba something liquid haka" okay ta ce sannan ta juya tabar wajen.
Juyi kawai take kan gadon amma ta kasa bacci banda ciwo babu abinda cikinta ke mata gashi daman wajen ya yi wani irin ja da kuma kumbura tun ranar da Imad ya daketa koda wasa bata taɓa nuna wani abu agabansa wanda zai sa ya fahimci haka ba dakyar take iya taka ƙafarta duk jijiyoyin wajen sun riƙe haka take kasancewa duk dare cikin rashin samun bacci wadattace,
Fitowar ta kenan daga wanka tana tsaye tana ƙoƙarin shafa mai ajikinta batasan sanda ya shigo ɗakin ba har ta gama shafa man sannan ta zame towel ɗin da niyyar ɗaukan rigarta
"Keeeeee!!"
Afirgice ta juyo tana kallonsa dan batasan sanda ta karasa yarda towel ɗinba hankali tashe yake kallon cikin nata yama kasa furta komai ita kuwa fashewa tayi da kuka tana ƙoƙarin rufe jikinta batasan ko kaɗan tunanin Imad bai zo wajen ba, tsugunawa ya yi gabanta yana kai hannunsa kan cikin nata, sosai abun ya bashi mamaki haɗi da tashin hankali dan bai taɓa ganin irin abun azahiri ba saidai akaratu bakinsa na rawa ya furta
"Keeee..keee...Mee..mene wannan?"
Cikin kukan ta ce"dan Allah Uncle kayi haƙuri dan Allah karka dakeni wlh mutuwa zanyi dan Allah Uncle" miƙewa ya yi kawai bai ce komai ba ya miƙa mata rigarta sannan ya juya ya yi waje, rigar ta sanya har sannan tana ci-gaba da kukanta dan gani take kamar sake dukanta zai yi, shi kuwa rasa abinda zai yi, ya yi duk hankalinsa ya tashi ko yaushe ta samu wannan ciwon???.
Suna shiga cikin asibitin aka shige da'ita emergency Imad kuwa ya kasa zaune ya kasa tsaye dan tashin hankalinsa ɗaya abinda zai cewa Daddy idan ya tambaye shi ya kuma san halin Daddyn nasa, Jawaad ne ya ƙara so yana kallonsa amma ya kasa ce masa komai dan ransa a matuƙar ɓace yake kusan 5mins suna tsaye kafin ya ƙaraso yana kallonsa ya ce"friend wane bashida lafiya?" asanyaye Imad ya ce"wlh yarinya ce kuma gaskiya abun ba karami bane please kaje ka gani" okay ya ce sannan ya kalli Jawaad da sauri ya sake kallonsa ganin kamar yaso ya tuna inda ya sanshi kallonsa shima Jawaad ya yi amma bai ce komai ba shima Kamal shigewa ya yi saboda ya duba mara lafiyar.
Kusan mutuwar tsaye Kamal ya yi ganin Fattomah kwance an sanya mata oxygen bai taɓa tsammatar haka ba dukda ya yi mamakin ganin Jawaad amma bai ɗauka ita ce batada lafiyar ba tunaninshi ɗaya yanzu mene ne alaƙarta da abokinsa Imadudden har zai kawota asibiti shidai yasan shi kaɗai iyayensa suka haifa bare yace ƙanwarsa ce wannan tunanin shine abinda ya sanya duk ya zama moody har aka shiga da yarinyar domin dubata.
Da sauri Jawaad ya fizge takardar hannun Kamal ɗin cikin son gazgata abinda Kamal ɗin yake faɗa ji ya yi numfashinsa na neman barin jikinsa lokacin daya gama karanta takardar bai taɓa tunanin haka ba koda kuwa cikin mafarki ne zama ya koma ya yi jin jiri na neman ɗibansa ba shi kaɗai ba shima kansa Kamal ya kasa magana ji yake inama ace mafarkine wannan abinda yake faruwa ɗin ba gaskiya ba, inama ya farka daga wannan mafarkin wanda yake neman tarwatsa masa farin cikinsa zuciyarsa da kwakwalwarsa duk a dagule suke kuma cikeda tambayoyi masu tarin yawa. Kamar wani zaki haka ya mike yana riƙeda takardar ya fice daga cikin office ɗin, shigowarsa kenan bayan yaje gida dan ɗauko mata kaya ganin Jawaad tsaye ya haɗe hannayensa a ƙirji yasa ya ƙara sa ya dafa shi cikin sanyin murya ya ce"Jawaad ya jikin nata?"
"Ka kyauta Imad!! Ka kyauta wannan shine cika alƙawari haka shine daidai wllh ban taɓa zaton haka daga gareka ka koda kuwa a mafarki ne ban ɗauka zaka kasance mai son zuciya kuma mara imani har haka ba nasan kawai Kanada saurin fushi da fusata amma ban yi zaton kai azzalumi neba Imadudden kaci amana kayi yaudara kuma kayi zalunci wanda kai ma kasan Ubangiji bazai taɓa barinka ba kai ɗin azzalumi ne!!!"
Kallonsa kawai Imad yake yi tunda ya fara maganar dan baisan abinda yake nufi ba kuma baisan akan me yake magana duk sai ya ruɗe gashi Jawaad sai surfa masifa yake ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba
"Ka sanar dani wai mene ne abinda ke faruwa Jawaad?" murmushin takaici Jawaad ya yi sannan ya miƙa masa takardar hannunsa, ahankali ya warwareta ya fara karantawa anutse, wani irin gumi ne ki tsassafo masa tundaga tsakiyar kansa da sauri ya kalli Jawaad yaga shi yake kallo da alamar tuhuma, zama Imad ya yi kan wata kujera daya gani wajen dan ji yake kamar ya yi hauka ya rasa mene ne yake shirin faruwa farin ciki ya kamata ya yi ko kuwa baƙi ciki???, damuwa ce fal ransa da kuma tashin hankali dan baisan da wane idanu zai tari Daddy ba shine babban tashin hankalinsa, kallonsa Jawaad ya yi sai kuma ya ce
"Imad why??why??why??, Dan Allah wace irin tsana ka yiwa wannan yarinyar?, mene laifinta daka yanke shawarar rabata da farin ciki?, me ta aikata maka wanda kake tunanin ta cancanci wannan hukuncin?, akan wane dalili ne Imad?" Dafe kansa ya yi dan bashida amsar da zai bawa Jawaad a halin yanzu dan kome zai faɗa masa bazai ɗauka ba. Miƙewa Imad ya yi bai ce komai ba ya yi waje yana haɗa hanya saboda ciwon da kansa ke masa, da kallo Jawaad da bisa yasan tunda ya yi haka bazai faɗa masa sannan bane shiyasa shima ya rabu dashi.