Sashe 23
Fattomah Book Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sake runtse idanunta tayi saboda tsoro cikin faɗa ya ce"gidan ubanwa kika je?" rawa jikin Fattomah ya fara yi tama kasa furta masa koda kalma ɗaya sai kuka take kamar wacce ke gaban mala'ika, kwafa ya yi ya ce"wato bakida bakin magana saboda kin fita yawon gabanki yar ficiciya dake har kinsan fita wani wajen ki kwana har tsawon kwanaki wato duk abinda za'a yi miki ayi miki bakida asara toh bari kiji Wlh sai kin gane Allah ɗaya ne, daga rana mai irinta yau bazaki sake aikata abinda kika aikata ba ke koda kuɗi kuwa aka ce za'a baki I'll teach you a lesson" fashewa tayi da kuka ta fara zagaye ɗakin tana bashi haƙuri sosai abin ya ɓatawa Imad rai musamman yanda take kukan kamar ranta zai fita baisan sanda zuciya ta ɗebeshi ya fincikota ta waɗo gabansa ba, bulalar ya shiga sauke mata ta ko'ina dan baya ma duba inda zai daka jikinta, kusan 10mins yana aikin dukanta tuni jikinta yagama saki gabaɗaya dan babu alamun tana numfashi duk jikinta ya fashe gwanin ban tausayi, tsaki ya yi sannan ya taka cikinta ya yi ball da'ita ya shige yana fita ya mayar da ƙofar ɗakin ya rufe ya sanya lock sannan ya fice daga gidan gabaɗaya dan baya jin zai iya cigaba da kallon yarinyar musamman idan ya tuna abinda Yusuf ya faɗa masa akanta shine ma abinda ya ƙara sawa ya yi mata wannan mugun dukan da bai taɓa yi mata irinsa ba. Kai tsaye gidan gonarsa ya shige dan nan kaɗai ne yakejin zai samu farin ciki zuciyarsa tayi sanyi, sosai gidan gonar zai baka sha'awa saboda irin abubuwan dake cikinsa kai tsaye wajen da peacock ɗinsa suke nan ya nufa, gamayyar ɗawisu ne aƙalla sunkai guda 50 maza da mata yanda suke buɗe jelarsu kaɗai ya isa ya sanya mutum nishaɗi zama Imad ya yi kan wata farar kujera yana kallonsu. Har aka idar da sallar isha'i Fattomah bata iya tashi ba duk da zuwa sannan ta farfaɗo daga sumar da tayi yanda fuskarta ta koma sai ta baka tausayi dan bazaka taɓa cewa ita ce ba duk fuskarta ta kumbura saboda irin marunka da ya yi mata sannan ko'ina na fatar jikinta ya fashe sai jini ne ke ɗiga ko kuka ta kasa yi sai ajiyar zuciya da take saukewa duk irin yanda tayi attempting na tashi amma abin ya faskara, kifa kanta wanda yake barazanar tsage mata tayi kan cinyarta tana jin wani irin jiri na ɗibanta dukda azaunen da take. Har wajen 10pm tana nan zaune ahankali kuma akaro na babu adadi ta yunƙura da niyyar tashi wata irin ƙara ta saki saboda wani irin kullewa da cikinta ya yi tana jin kamar ana zarar ranta kasa komawa ta zauna tayi sai tsayawa da tayi tana riƙe da cikin nata, buɗe ƙofar ya yi bayan ya yi unlocking nata ya shigo kallo ɗaya ya yi mata sannan ya kama hannunta ba tareda ya ce komai ba suka fita a ɗakin, janta kawai yake domin ba tafiya take ba har sannan kuma hannunta na kan cikinta yana shiga bedroom ɗin ya hankaɗata har saida ta waɗi nan kasan carpet cikin kakkausar murya ya ce
"Daga yau nan ne wajen zamanki kuma ba zaki sake fita koda parlon cikin gidan nan ba saida kiyi rayuwarki anan tunda yar iska kike neman zama kuma koda school billahil Azeem ba zaki sake zuwa ba muddin kina cikin gidan nan saida bayan kin bar gidan nan" duk irin halinda Fattomah ke cike hakan bai hanata rike ƙafafunsa ba cikin dashasshiyar muryata ta ce"dan Allah Uncle kayi haƙuri ka barni naje makaranta wllh bazan sake zuwa ko'ina ba dan Allah Uncle karka hanani" janye ƙafarsa ya yi yana yi mata wani mugun kallo ya ce"idan kika sake riƙeni sai na gwaɗa miki mari" saurin ɗauke hannuta ta yi ya yi tsaki ya juya ya fita. Wani irin raunataccen kuka Fattomah ta fara yi kukane wanda yake tsuma zuciyar mai sauraro kukane wanda yake cikeda abubuwa daban-daban, kukane wanda yake tabbatar da maraicinta a wannan ranar tabbas da tanada iyaye toh haka bazata faru da'ita ƙaddara ce ta rabata da iyayen ta kawota rayuwa inda ake ɗaukarta tamkar dabba dan wani lokacin ma gwara dabba da abinda ake mata, gashi batada kowa wanda zai rarrasheta saida tayi kukanta ya ishe ta tayi shuru abinta haka ta zauna taci kukanta har Allah ya sanya mata dangana da haƙuri bacci ya ɗauketa a wajen.
Kallonsa Ayrah tayi sai kuma ta ce"wai saurin me kake ne?" hular hannunta ya karɓa ya ce"bazaki gane ba ke kam kawai sai nadawo" kwaɓe fuska tayi ta ce"wai kana nufin ba zaka ci abinci ba zaka fita dear?" murmushi ya yi yaja kumatunta ya ce"I'm sorry wlh idan na tsaya makara zanyi kuma kinsan halin Imad dai" haɗe rai ta yi ta ce"ni daman nasan tunda naga kana wannan saurin toh shine ya kira ka shi ya fiye nuna isa wlh ko kai da kake ɗan sarkin baka...." ganin kallon da yake mata ya sa ta yi shuru da bakinta saida ya ɗaura wrist watch ɗinsa sannan ya ce" banason sake jin irin wannan maganar a bakin ki okay?" gyaɗa masa kai tayi ta ce"I'm sorry dear" murmushi ya yi ya ce"ya wuce saina dawo" "bari na rakaka toh" okay ya ce sannan suka fita suna rike da hannu juna. Rai ɓace Aysha ta ce"banda rainin hankali tasan yau akwai paper amma tayi zamanta haka ranar Friday ma tayi ko ubanme take nufi da kanta bansani ba" murmushi Fa'eeza ta yi ta ce"ke kuma kin fiye saurin fusata maybe akwai wani abun kinsan haka kawai Fateemah ba zata ƙi zuwa exam ba" Zainab ce ta ce"wlh kuwa amma mu kirata awaya mana naga kwana biyu bata hau online kwata-kwata" tsaki Aysha ta yi ta ce"ai babu waya a hannunta bare a kirata kuma gashi bamusan gidan da take ba balle muje muga ko lafiya" da damuwa Fa'eeza ta ce"gaskiya kam Allah dai yasa lafiya" Ameen Zainab ta ce sannan suka miƙe dan sannan zasu shiga biology.
Dakyar ta idar da sallar asuba ɗin sannan ta zauna gefen gadon banda raɗaɗi babu abinda jikinta ke mata ko'ina babu daɗi ga bakinta wanda take jin yana yi mata wani irin ɗaci rabonta da abinci har ta manta dan bata iya cin komai ruwa ma dakyar take samu tasha kuma shima sai ƙishirwar ta ƙure kuma bata iya sha da yawa saidai kaɗan hakan yasa duk fatar jikinta ta fara yamushewa kana ganinta kasan babu wadataccen jini da ruwa ajikinta cikin sati ɗaya da tayi a haka koda sau ɗaya Imad bai leƙo da niyyar dubata ba saidai kullum taji alamun tashin motarsa idan zai fita idan har wanda yasan Fattomah watanni uku da suka shige zai ganta yanzu toh tabbas sai ya yi dagaske kafin ya iya gane itace duk tayi baƙi ga wata uwar rama da tayi idanuwanta duk sun faɗa ciki Fattomah wacce ta kasance mai yawan hira da wasa da dariya yau sai tayi kwanaki ba tace uffan ba idan har zata buɗi bakinta to saidai wajen karatun sallah amma ko kaɗan bata hira to dawa ma zata yi hiran???????? Ita ba uwa ba ita ba uba ba Allah sarki kaɗan daga cikin ƙalubalen maraici kenan. Cikin kwantar da murya da son faɗa masa gaskiya ya ce
"Wallahi dagaske nake maka babu amfanin wannan abinda kake aikatawa, yarinya ce ƙarama batasan komai ba ko wace irin tarbiyya kake so zaka iya ɗorata kuma tabi amma wlh duk ranar da Fattum ta fara gane kanta bazaka taɓa iya lankwasa taba, duka baya taɓa sakawa yaro ya daina abu saima tunzurashi da yake wasu lokutan bare kuma Fattomah da batada saka magana ko kaɗan yarinya ce wacce bata damu da rayuwar kowa ba beside kuma batada laifi dan ba itace ta kawo kanta gidanka ba bata cancanci irin wannan rayuwar ba kamata ya yi ka tausayawa maraicinta ka kula da rayuwarta naɗan wannan lokacin ka daina dukanta domin hakan tamkar zaluntarta ka ke, ka dinga ƙoƙarin sassauta fushinka akanta kuma wani lokacin ba laifi tayi ba kawai saboda kanajin cewa ka tsaneta cikin ranka yasa kake mata haka, dan Allah Imad ka faɗa min mene ne lafin Fattomah daya sanya ka tsaneta dan Allah ka faɗa min?" Shiru Imad ya yi dan tabbas bashida amsar bashi kuma baisan dalilin hakan ba kawai yaji baya ƙaunarta ko kaɗan cikin ransa aduk sanda ya ganta ji yake tamkar ya shaƙe mata wuya ta mutu ko ya daina ganin fuskarta bai taɓa jin tsanar mutum cikin zuciyarsa irin Fattomah ba ko mene dalili ohooooo?????, Jawaad ya cigaba da faɗin"dan Allah ka buɗe yarinyar nan kuma karka sake rufe ta saboda alfarmar Annabi koda bazaka kula da'ita ba to karka cutar da'ita kabarta haka nan please Bro" ajiyar zuciya Imadudden ya sauke sannan ya gyaɗa masa kai a hankali ya ce"in sha Allah kodan saboda kai nasan bakason kaga matarka cikin damuwa right?" kallonsa Jawaad ya yi amma bai ce komai ba, da sallama ta shigo parlon tana sanye cikin wata atamfa Holland coffee color ta sanya farin mayafi ɗan ƙarami hannunta riƙe da mukullin mota, gaisawa suka yi da Jawaad sannan ta kalli Imad ta ce"daman zan fitan ne" okay ya ce mata sannan ta juya ta fita abinta. Kwance ya tarar da'ita ta duƙunƙune cikin duvet, ahankali ya ƙarasa gaban gadon ya tsaya yana kallon fuskarta wacce tagama sauya kammani gefen duvet ɗin ya daka hakan yasa ta buɗe idanunta saboda batada nauyin bacci da sauri tayi baya cikin tashin hankali ta fara faɗin
"Da..Da...dan Allah Uncle kayi haƙuri da. n Allah"
Kallonta kawai ya tsaya yana yi dan baima san abinda zai ce mata ba kuma daman ba shigowa ya yi dan ya yi mata maganar ba tsayawa tayi da kukan ganin ya juya ya yi fitarsa jingina tayi da jikin gadon tana sauke numfashi ahankali, saida ta nutsu sosai sannan ta miƙe tana tafiya a hankali ta shige toilet.
"Daga yau nan ne wajen zamanki kuma ba zaki sake fita koda parlon cikin gidan nan ba saida kiyi rayuwarki anan tunda yar iska kike neman zama kuma koda school billahil Azeem ba zaki sake zuwa ba muddin kina cikin gidan nan saida bayan kin bar gidan nan" duk irin halinda Fattomah ke cike hakan bai hanata rike ƙafafunsa ba cikin dashasshiyar muryata ta ce"dan Allah Uncle kayi haƙuri ka barni naje makaranta wllh bazan sake zuwa ko'ina ba dan Allah Uncle karka hanani" janye ƙafarsa ya yi yana yi mata wani mugun kallo ya ce"idan kika sake riƙeni sai na gwaɗa miki mari" saurin ɗauke hannuta ta yi ya yi tsaki ya juya ya fita. Wani irin raunataccen kuka Fattomah ta fara yi kukane wanda yake tsuma zuciyar mai sauraro kukane wanda yake cikeda abubuwa daban-daban, kukane wanda yake tabbatar da maraicinta a wannan ranar tabbas da tanada iyaye toh haka bazata faru da'ita ƙaddara ce ta rabata da iyayen ta kawota rayuwa inda ake ɗaukarta tamkar dabba dan wani lokacin ma gwara dabba da abinda ake mata, gashi batada kowa wanda zai rarrasheta saida tayi kukanta ya ishe ta tayi shuru abinta haka ta zauna taci kukanta har Allah ya sanya mata dangana da haƙuri bacci ya ɗauketa a wajen.
Kallonsa Ayrah tayi sai kuma ta ce"wai saurin me kake ne?" hular hannunta ya karɓa ya ce"bazaki gane ba ke kam kawai sai nadawo" kwaɓe fuska tayi ta ce"wai kana nufin ba zaka ci abinci ba zaka fita dear?" murmushi ya yi yaja kumatunta ya ce"I'm sorry wlh idan na tsaya makara zanyi kuma kinsan halin Imad dai" haɗe rai ta yi ta ce"ni daman nasan tunda naga kana wannan saurin toh shine ya kira ka shi ya fiye nuna isa wlh ko kai da kake ɗan sarkin baka...." ganin kallon da yake mata ya sa ta yi shuru da bakinta saida ya ɗaura wrist watch ɗinsa sannan ya ce" banason sake jin irin wannan maganar a bakin ki okay?" gyaɗa masa kai tayi ta ce"I'm sorry dear" murmushi ya yi ya ce"ya wuce saina dawo" "bari na rakaka toh" okay ya ce sannan suka fita suna rike da hannu juna. Rai ɓace Aysha ta ce"banda rainin hankali tasan yau akwai paper amma tayi zamanta haka ranar Friday ma tayi ko ubanme take nufi da kanta bansani ba" murmushi Fa'eeza ta yi ta ce"ke kuma kin fiye saurin fusata maybe akwai wani abun kinsan haka kawai Fateemah ba zata ƙi zuwa exam ba" Zainab ce ta ce"wlh kuwa amma mu kirata awaya mana naga kwana biyu bata hau online kwata-kwata" tsaki Aysha ta yi ta ce"ai babu waya a hannunta bare a kirata kuma gashi bamusan gidan da take ba balle muje muga ko lafiya" da damuwa Fa'eeza ta ce"gaskiya kam Allah dai yasa lafiya" Ameen Zainab ta ce sannan suka miƙe dan sannan zasu shiga biology.
Dakyar ta idar da sallar asuba ɗin sannan ta zauna gefen gadon banda raɗaɗi babu abinda jikinta ke mata ko'ina babu daɗi ga bakinta wanda take jin yana yi mata wani irin ɗaci rabonta da abinci har ta manta dan bata iya cin komai ruwa ma dakyar take samu tasha kuma shima sai ƙishirwar ta ƙure kuma bata iya sha da yawa saidai kaɗan hakan yasa duk fatar jikinta ta fara yamushewa kana ganinta kasan babu wadataccen jini da ruwa ajikinta cikin sati ɗaya da tayi a haka koda sau ɗaya Imad bai leƙo da niyyar dubata ba saidai kullum taji alamun tashin motarsa idan zai fita idan har wanda yasan Fattomah watanni uku da suka shige zai ganta yanzu toh tabbas sai ya yi dagaske kafin ya iya gane itace duk tayi baƙi ga wata uwar rama da tayi idanuwanta duk sun faɗa ciki Fattomah wacce ta kasance mai yawan hira da wasa da dariya yau sai tayi kwanaki ba tace uffan ba idan har zata buɗi bakinta to saidai wajen karatun sallah amma ko kaɗan bata hira to dawa ma zata yi hiran???????? Ita ba uwa ba ita ba uba ba Allah sarki kaɗan daga cikin ƙalubalen maraici kenan. Cikin kwantar da murya da son faɗa masa gaskiya ya ce
"Wallahi dagaske nake maka babu amfanin wannan abinda kake aikatawa, yarinya ce ƙarama batasan komai ba ko wace irin tarbiyya kake so zaka iya ɗorata kuma tabi amma wlh duk ranar da Fattum ta fara gane kanta bazaka taɓa iya lankwasa taba, duka baya taɓa sakawa yaro ya daina abu saima tunzurashi da yake wasu lokutan bare kuma Fattomah da batada saka magana ko kaɗan yarinya ce wacce bata damu da rayuwar kowa ba beside kuma batada laifi dan ba itace ta kawo kanta gidanka ba bata cancanci irin wannan rayuwar ba kamata ya yi ka tausayawa maraicinta ka kula da rayuwarta naɗan wannan lokacin ka daina dukanta domin hakan tamkar zaluntarta ka ke, ka dinga ƙoƙarin sassauta fushinka akanta kuma wani lokacin ba laifi tayi ba kawai saboda kanajin cewa ka tsaneta cikin ranka yasa kake mata haka, dan Allah Imad ka faɗa min mene ne lafin Fattomah daya sanya ka tsaneta dan Allah ka faɗa min?" Shiru Imad ya yi dan tabbas bashida amsar bashi kuma baisan dalilin hakan ba kawai yaji baya ƙaunarta ko kaɗan cikin ransa aduk sanda ya ganta ji yake tamkar ya shaƙe mata wuya ta mutu ko ya daina ganin fuskarta bai taɓa jin tsanar mutum cikin zuciyarsa irin Fattomah ba ko mene dalili ohooooo?????, Jawaad ya cigaba da faɗin"dan Allah ka buɗe yarinyar nan kuma karka sake rufe ta saboda alfarmar Annabi koda bazaka kula da'ita ba to karka cutar da'ita kabarta haka nan please Bro" ajiyar zuciya Imadudden ya sauke sannan ya gyaɗa masa kai a hankali ya ce"in sha Allah kodan saboda kai nasan bakason kaga matarka cikin damuwa right?" kallonsa Jawaad ya yi amma bai ce komai ba, da sallama ta shigo parlon tana sanye cikin wata atamfa Holland coffee color ta sanya farin mayafi ɗan ƙarami hannunta riƙe da mukullin mota, gaisawa suka yi da Jawaad sannan ta kalli Imad ta ce"daman zan fitan ne" okay ya ce mata sannan ta juya ta fita abinta. Kwance ya tarar da'ita ta duƙunƙune cikin duvet, ahankali ya ƙarasa gaban gadon ya tsaya yana kallon fuskarta wacce tagama sauya kammani gefen duvet ɗin ya daka hakan yasa ta buɗe idanunta saboda batada nauyin bacci da sauri tayi baya cikin tashin hankali ta fara faɗin
"Da..Da...dan Allah Uncle kayi haƙuri da. n Allah"
Kallonta kawai ya tsaya yana yi dan baima san abinda zai ce mata ba kuma daman ba shigowa ya yi dan ya yi mata maganar ba tsayawa tayi da kukan ganin ya juya ya yi fitarsa jingina tayi da jikin gadon tana sauke numfashi ahankali, saida ta nutsu sosai sannan ta miƙe tana tafiya a hankali ta shige toilet.