Sashe 11
Fattomah Book Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wata irin zabura Imad ya yi ya miƙe tsaye yama kasa magana sai riƙe gefen zuciyarsa da yayi ba shi kaɗai ba hatta Jawaad Saida ya mike tsaye baisan yaushe ba kuma baisan meyasa ba kawai yaji wasu zafafan hawaye na gangarowa kan fuskarsa, kallonsu kawai iyayen sukayi da rashin fahimta, sosai parlon ya yi shiru kamar ba'a taɓa hallitar mutane cikinsa ba sai Imadudden da yake ta sauke ajiyar zuciya har sannan kuma bai zauna ba. Daddy ne ya kalli Jawaad ganin yanda yake kuka kamar ƙaramin yaro yasa ya kamo hannunsa zama Jawaad ya yi yana kallonsu kamar wani zararre Daddy ya ce"Jawaad meya faru?"kallon Daddy ya yi sai kuma ya fashe da kuka kamar ba shiba ya ɗora kansa kan cinyar Daddy yana kukan, da mamaki kowa yake kallonsa banda Mommy wacce daman tasan kwanan zance kwata-kwata basu yanke abinda ya kamata ba domin Jawaad shine wanda yafi dacewa da Fattomah ba Imad ba dukda tanason Fattomah ta kasance surika awajenta amma tasan bazata samu farin ciki ba indai tana tare da Imad dan ba tun yau ba ya nuna zallar ƙiyayyarsa ga yarinyar. Shafa kansa Daddy ya shiga yi dan yasan tunda har Jawaad ya zubar da hawayensa to tabbas abune mara daɗi ya sameshi, ita kuwa Ayrah da idanu ta bishi tama rasa murna zatayi ko baƙin ciki
Mai martaba ne ya ce"wai Jawaad mene haka wannan wane irin abune mene yake damunka?" a hankali Jawaad ya fara rage kukansa amma har sannan bai ɗago fuskarsa ba Daddy ne ya ce"kai kuma akanme kake tsaye kan mutane?" A fusace Imad ya ce
"Daddy wallahi bazai yiwu ba, ni bazan iya zama da wannan yarinyar matsayin wata matata ba banida wani interest nayin aure yanzu kuma koda zanyi auran to ni ban shirya auran ƙaramar yarinya ba bazan iya wahala ba banida wani feeling akan yarinyar kuma kunsan bazanyi abinda zan cutar da rayuwata ba banasonta kuma bazan taɓa sonta ba domin ita bata dace dani ba nima kuma ban dace da ita ni ba ajinta bane ni Imadudden Ibraheem Baira nafi ƙarfin auran wannan yarinyar shi dayake da buƙata kuma ya nuna yanaso kuna iya bashi aurenta amma ni.......har abada!!"
Yanda yake huci yana maganar yasa duka suka zuba masa idanu suna kallonsa duk sunyi mamaki banda Daddy wanda daman yasan hakan zata iya kasancewa domin ya daɗe da lurada yanda yake mu'amala da yarinyar cikin gidan kuma yasan halin Imad da mugun taurin kai ga kafiya kamar mutanen farko koda yake barewa batayi gudu ɗanta ya yi rarrafe ba dan shima Daddy number 1 ne wajen kafiya da gaddama. Uncle Kabeer ne ya ce rai a haɗe"ba shawararka muke nema ba Imad umarni ne kuma dolenka kayi biyayya ko kanaso ko baka so"
Bai ce komai ba kuma har sannan bai zauna ba sai wani irin numfashi yake saukewa kamar wani zakin da yake a yunwace danma sun raina masa hankali shine sai shi zasu bawa auren yarinyar da ko a hanya baya fatan haɗuwa da'ita bare kuma ya zauna da'ita gida ɗaya matsayin matarsa never!!!
Mai martaba ne ya ce anutse"Imadudden!" kallonsa Imad ya yi cikeda girmamawa ya ce"na'am Dad" da hannu ya yi masa alama da yazo ya karaso gabansa ya tsuguna kallonsa ya yi cikeda tausayawa ya ce"mene matsalar?" ajiyar zuciya ya sauke ya ce
"Dad wallahi bana so bamu dace da juna ba amma shi Jawaad yana matuƙar ƙaunarta dan Allah Dad ku mayar da auran kansa please ban shirya ba wlh" shafa kansa Mai martaba ya yi ya ce"ƴar uwarka ce Imad kuma munyi la'akari da cewa kaine kafi buƙatar mace ba Jawaad ba kaine kake da buƙatar second wife dan kamar wanda bashida mata haka kake kuma Fateema yarinyar kirki ce marainiya idan ka kula da rayuwarta Allah zai kula dakai kaima" girgiza kai Imad ya yi ya ce"Dad wallahi banajin zan iya domin zuciyata zafi yake min idan ina tuna cewa wannan yarinyar matsayin matata take ko a mafarki bantaɓa tunanin haka ba ko Jawaad daya nuna yana so banyi supporting nasa ba why yanzu kuma abun zai ƙare akaina Da?, wlh banason auren yarinya" murmushi mai martaba ya yi ya ce"itama yarinyar watarana girma zatayi sannan duk abinda ka ɗorata shine wanda zata aikata maka yarinya tafi daɗi wajen sha'anin aure kayi tunani Imad" shuru Imad ya yi badan ya gamsu da abinda mai martaba ya faɗa masa ba saidan bayason yawan jayyaya da iyayensa, Fulani ce ta ce"nikam dan Allah yaya idan abun zai zama faɗa kawai a haƙura" wani kallo uncle Kabeer ya yi mata ya ce"ku daman mata ai ƙaramin tunani ne daku karki sake cewa komai amaganar nan" shiru ta yi batace komai ba.
Daddy ya ce"shikenan Imad kanason yarinyar nan ko baka sonta?" kallonsa Imad ya yi da idanunsa wanda suka canza launi ya ce"wlh Daddy bana sonta" jinjina kai Daddy ya yi ya ce"good, yanda kace haka za'ayi an rigada an ɗaura muku aure saboda haka dole sai ka saketa"
Shiru duka suka yi suna sauraren maganar yayan nasu tunda suka ji ya magantu tofah tabbas akwai abinda hakan zai haifar kuma daman bada son ransa suka ɗaura musu auren ba
"Zan raba auren dake tsakaninka da'ita amma bisa sharaɗi guda ɗaya" da sauri Imad ya ce"na amince koma mene ne Daddy zanyi"girgiza kai ya yi ya ce"ka fara tsayawa kaji abinda zance, zan bar garin nan ita kuma yarinya anan take karatunta kuma ta kusa ƙarasawa babu buƙatar a tsayar mata da karatu saboda haka Faɗeematoh zata zauna wajenka cikin gidanka a matsayin yarinyar da kake riƙo daga nan har zuwa sanda zata kammala karatunta wanda yanzu ya kasance watanni uku nan gaba har sanda wannan lokacin zai cika bazaka saketa ba daga ranar da suka gama jarrabawa zan aiko a ɗaukar min ita shikenan daga nan sai ka saketa" gorar ruwan da take gefensa ya ɗauka ya buɗe saida ya kusa shanyewa sannan ya ajiye ya cigaba da faɗin
"Har zuwa sanda zan karɓeta zata zauna matsayin ƴar riƙo wacce zaka kula da rayuwarta matsayin ƴar uwarka banason jin wani tashin hankali ko wata magana tsakaninku Fattum batasan da wannan maganar ba kuma ba zata sani ba" kallon Jawaad ya yi wanda har sannan yake kwance kan cinyar Daddy ya ce"karka damu Jawaad nayi maka alƙawarin auren Fateema indai ina raye kuma kaima kana raye da zarar ta kammala secondary school zan ɗaura maka aure da'ita karka damu kanka kaji" sanin indai Daddy ya faɗi magana sai ya cikata yasa Jawaad goge hawayensa ya ce"thank you Daddy"shafa kansa Daddy ya yi ya ce"Allah ya yi maka albarka" Ameen kowa na parlon ya amsa.
Mai martaba ya ce"Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi"Ameen suka amsa sannan ya kalli Imad ya ce"ka yarda da wannan hukuncin?" gyaɗa masa kai y yi y ace"magana zakayi Babana" a hankali cikin sanyin murya ya ce"na yarda Dad zan barta cikin gidana har zuwa sanda zata kammala karatunta amma zan dawo da'ita kuma kome za'a ce bazan zauna da'ita na tsayin rayuwa ba domin ni bana sonta" murmushi Daddy ya yi ya ce"ba Saika cigaba da faɗa ba mu muna sonta muna ƙaunarta kuma bamu kyamatarta Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya"
Miƙewa Imad ya yi ya ce"zan tafi inada ayyuka" gaba ya yi kafin ya kai waje ya tsinkayi Daddy yana cewa
"Amma ka sani koda wasa naji wani abu bayan zamanta matsayin ƴar riƙo ranar zaka gane bakada wayo kuma bakasan kanka ba, ranar zan nuna maka the other side of me saboda haka take note" wani irin murmushi Imad ya yi sannan ya fice daga parlon. Daddy ne ya kalli Jawaad ya ce"tashi ku tafi kaji karka damu kamar yanda na faɗa maka Fattomah matarka ce in sha Allah"murmushi ya yi ya ce"tom Daddy nagode sosai Allah ya ƙara girma" Ameen ya ce sannan ya miƙe yana kallon Ayrah wacce ta cika ta batse ya ce"tashi muje" miƙewa tayi ko sallama bata yi musu ba ta fice daga parlon saida ya yiwa su Mommy Sallama sannan ya fita shima. Murmushi Uncle Mukhtar ya yi ya ce"Allah ya nuna mana wannan ranar" murmushi shima Uncle Kabeer ya yi ya ce"aikam ranar akwai kallo dukda nasan babu lallai ma su rabu" miƙewa Daddy ya yi ya ce"kamar sun rabu sun gama saidai idan bana raye amma sai Imad ya saki yarinyar" shuru sukayi jin ya yi magana mai martaba ya mike ya ce"zan koma Allah ya tsare hanya" okay Daddy ya ce sannan duka suka tashi kowa ya tafi Daddy ya kalli Mommy wacce ta dawo daga raka su Fulani ya ce"jeki kiramin Fattum"toh ta ce sannan ta juya ta fita
*Ameenatou ce#*
*Nanameera ce#*
*Like nd share*
[5/13, 9:29 PM] Nanameera: *FATTOMAH*
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION.
PAGE 21-22.
*Ameenatou I Ibraheem*
*Nanameera ce#*
Cikin yanayin na mutuwa Daddy ya fara cewa"Fateema zan bar garin nan ranar Friday kuma naso ace tare zamu tafi saida ke kinada makaranta kuma banason karatunki ya tsaya tunda har kinzo gangara, saboda haka zaki zauna gidan Imad har zuwa sanda zaki kammala karatunki daga nan zaki dawo wajena mu cigaba da rayuwa"
Mai martaba ne ya ce"wai Jawaad mene haka wannan wane irin abune mene yake damunka?" a hankali Jawaad ya fara rage kukansa amma har sannan bai ɗago fuskarsa ba Daddy ne ya ce"kai kuma akanme kake tsaye kan mutane?" A fusace Imad ya ce
"Daddy wallahi bazai yiwu ba, ni bazan iya zama da wannan yarinyar matsayin wata matata ba banida wani interest nayin aure yanzu kuma koda zanyi auran to ni ban shirya auran ƙaramar yarinya ba bazan iya wahala ba banida wani feeling akan yarinyar kuma kunsan bazanyi abinda zan cutar da rayuwata ba banasonta kuma bazan taɓa sonta ba domin ita bata dace dani ba nima kuma ban dace da ita ni ba ajinta bane ni Imadudden Ibraheem Baira nafi ƙarfin auran wannan yarinyar shi dayake da buƙata kuma ya nuna yanaso kuna iya bashi aurenta amma ni.......har abada!!"
Yanda yake huci yana maganar yasa duka suka zuba masa idanu suna kallonsa duk sunyi mamaki banda Daddy wanda daman yasan hakan zata iya kasancewa domin ya daɗe da lurada yanda yake mu'amala da yarinyar cikin gidan kuma yasan halin Imad da mugun taurin kai ga kafiya kamar mutanen farko koda yake barewa batayi gudu ɗanta ya yi rarrafe ba dan shima Daddy number 1 ne wajen kafiya da gaddama. Uncle Kabeer ne ya ce rai a haɗe"ba shawararka muke nema ba Imad umarni ne kuma dolenka kayi biyayya ko kanaso ko baka so"
Bai ce komai ba kuma har sannan bai zauna ba sai wani irin numfashi yake saukewa kamar wani zakin da yake a yunwace danma sun raina masa hankali shine sai shi zasu bawa auren yarinyar da ko a hanya baya fatan haɗuwa da'ita bare kuma ya zauna da'ita gida ɗaya matsayin matarsa never!!!
Mai martaba ne ya ce anutse"Imadudden!" kallonsa Imad ya yi cikeda girmamawa ya ce"na'am Dad" da hannu ya yi masa alama da yazo ya karaso gabansa ya tsuguna kallonsa ya yi cikeda tausayawa ya ce"mene matsalar?" ajiyar zuciya ya sauke ya ce
"Dad wallahi bana so bamu dace da juna ba amma shi Jawaad yana matuƙar ƙaunarta dan Allah Dad ku mayar da auran kansa please ban shirya ba wlh" shafa kansa Mai martaba ya yi ya ce"ƴar uwarka ce Imad kuma munyi la'akari da cewa kaine kafi buƙatar mace ba Jawaad ba kaine kake da buƙatar second wife dan kamar wanda bashida mata haka kake kuma Fateema yarinyar kirki ce marainiya idan ka kula da rayuwarta Allah zai kula dakai kaima" girgiza kai Imad ya yi ya ce"Dad wallahi banajin zan iya domin zuciyata zafi yake min idan ina tuna cewa wannan yarinyar matsayin matata take ko a mafarki bantaɓa tunanin haka ba ko Jawaad daya nuna yana so banyi supporting nasa ba why yanzu kuma abun zai ƙare akaina Da?, wlh banason auren yarinya" murmushi mai martaba ya yi ya ce"itama yarinyar watarana girma zatayi sannan duk abinda ka ɗorata shine wanda zata aikata maka yarinya tafi daɗi wajen sha'anin aure kayi tunani Imad" shuru Imad ya yi badan ya gamsu da abinda mai martaba ya faɗa masa ba saidan bayason yawan jayyaya da iyayensa, Fulani ce ta ce"nikam dan Allah yaya idan abun zai zama faɗa kawai a haƙura" wani kallo uncle Kabeer ya yi mata ya ce"ku daman mata ai ƙaramin tunani ne daku karki sake cewa komai amaganar nan" shiru ta yi batace komai ba.
Daddy ya ce"shikenan Imad kanason yarinyar nan ko baka sonta?" kallonsa Imad ya yi da idanunsa wanda suka canza launi ya ce"wlh Daddy bana sonta" jinjina kai Daddy ya yi ya ce"good, yanda kace haka za'ayi an rigada an ɗaura muku aure saboda haka dole sai ka saketa"
Shiru duka suka yi suna sauraren maganar yayan nasu tunda suka ji ya magantu tofah tabbas akwai abinda hakan zai haifar kuma daman bada son ransa suka ɗaura musu auren ba
"Zan raba auren dake tsakaninka da'ita amma bisa sharaɗi guda ɗaya" da sauri Imad ya ce"na amince koma mene ne Daddy zanyi"girgiza kai ya yi ya ce"ka fara tsayawa kaji abinda zance, zan bar garin nan ita kuma yarinya anan take karatunta kuma ta kusa ƙarasawa babu buƙatar a tsayar mata da karatu saboda haka Faɗeematoh zata zauna wajenka cikin gidanka a matsayin yarinyar da kake riƙo daga nan har zuwa sanda zata kammala karatunta wanda yanzu ya kasance watanni uku nan gaba har sanda wannan lokacin zai cika bazaka saketa ba daga ranar da suka gama jarrabawa zan aiko a ɗaukar min ita shikenan daga nan sai ka saketa" gorar ruwan da take gefensa ya ɗauka ya buɗe saida ya kusa shanyewa sannan ya ajiye ya cigaba da faɗin
"Har zuwa sanda zan karɓeta zata zauna matsayin ƴar riƙo wacce zaka kula da rayuwarta matsayin ƴar uwarka banason jin wani tashin hankali ko wata magana tsakaninku Fattum batasan da wannan maganar ba kuma ba zata sani ba" kallon Jawaad ya yi wanda har sannan yake kwance kan cinyar Daddy ya ce"karka damu Jawaad nayi maka alƙawarin auren Fateema indai ina raye kuma kaima kana raye da zarar ta kammala secondary school zan ɗaura maka aure da'ita karka damu kanka kaji" sanin indai Daddy ya faɗi magana sai ya cikata yasa Jawaad goge hawayensa ya ce"thank you Daddy"shafa kansa Daddy ya yi ya ce"Allah ya yi maka albarka" Ameen kowa na parlon ya amsa.
Mai martaba ya ce"Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi"Ameen suka amsa sannan ya kalli Imad ya ce"ka yarda da wannan hukuncin?" gyaɗa masa kai y yi y ace"magana zakayi Babana" a hankali cikin sanyin murya ya ce"na yarda Dad zan barta cikin gidana har zuwa sanda zata kammala karatunta amma zan dawo da'ita kuma kome za'a ce bazan zauna da'ita na tsayin rayuwa ba domin ni bana sonta" murmushi Daddy ya yi ya ce"ba Saika cigaba da faɗa ba mu muna sonta muna ƙaunarta kuma bamu kyamatarta Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya"
Miƙewa Imad ya yi ya ce"zan tafi inada ayyuka" gaba ya yi kafin ya kai waje ya tsinkayi Daddy yana cewa
"Amma ka sani koda wasa naji wani abu bayan zamanta matsayin ƴar riƙo ranar zaka gane bakada wayo kuma bakasan kanka ba, ranar zan nuna maka the other side of me saboda haka take note" wani irin murmushi Imad ya yi sannan ya fice daga parlon. Daddy ne ya kalli Jawaad ya ce"tashi ku tafi kaji karka damu kamar yanda na faɗa maka Fattomah matarka ce in sha Allah"murmushi ya yi ya ce"tom Daddy nagode sosai Allah ya ƙara girma" Ameen ya ce sannan ya miƙe yana kallon Ayrah wacce ta cika ta batse ya ce"tashi muje" miƙewa tayi ko sallama bata yi musu ba ta fice daga parlon saida ya yiwa su Mommy Sallama sannan ya fita shima. Murmushi Uncle Mukhtar ya yi ya ce"Allah ya nuna mana wannan ranar" murmushi shima Uncle Kabeer ya yi ya ce"aikam ranar akwai kallo dukda nasan babu lallai ma su rabu" miƙewa Daddy ya yi ya ce"kamar sun rabu sun gama saidai idan bana raye amma sai Imad ya saki yarinyar" shuru sukayi jin ya yi magana mai martaba ya mike ya ce"zan koma Allah ya tsare hanya" okay Daddy ya ce sannan duka suka tashi kowa ya tafi Daddy ya kalli Mommy wacce ta dawo daga raka su Fulani ya ce"jeki kiramin Fattum"toh ta ce sannan ta juya ta fita
*Ameenatou ce#*
*Nanameera ce#*
*Like nd share*
[5/13, 9:29 PM] Nanameera: *FATTOMAH*
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION.
PAGE 21-22.
*Ameenatou I Ibraheem*
*Nanameera ce#*
Cikin yanayin na mutuwa Daddy ya fara cewa"Fateema zan bar garin nan ranar Friday kuma naso ace tare zamu tafi saida ke kinada makaranta kuma banason karatunki ya tsaya tunda har kinzo gangara, saboda haka zaki zauna gidan Imad har zuwa sanda zaki kammala karatunki daga nan zaki dawo wajena mu cigaba da rayuwa"