← Book details Fareedah Nabeel Complete Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 34

Sashe 3

Fareedah Nabeel Complete Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

HEY
MARAICIN AZRAH FAN'S CLUB
daku nike
Ku tashi daga barci
Wallahy Allah ko
NARUFE gidan
Kuma kusan Wannan ƙaramin aiki nane ehem🤷🏻‍♀️Haba mana malam kullum gida kenan shiru shiru kamar makabarta ko yar Sada zumunci nan bakuyi*

*ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI*

#COMMENT'S PLEASE !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!

*A'ISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹
*FAREEDAH NABEEL*
🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*AISHA FULANI GAL*

*EDITED BY UNCLE YUSEEP NADABO*

*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*

*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I'm
selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951

*🌺chapter 3-4🌺*

BOSSO ESTATE

__________NABEELAH _______

Wata kyakkyawar yarinya ce tabugawa a jarida na hango, fara ce sol kyakkyawar matashiyar budurwa ce, Asalin kyakkyawar kuwa domin duk inda ake batun kyau to wannan matashiyar budurwar zata amsa first number, Sanye take cikin wata koriyar atamfa me ratsin ruwan hanta ajiki ɗinki babu karya yayi matukar kyau sosai sai dai anci ma atamfan mutunci sosai riga da sket ne aka yi mata 8piece's kuma ya yi mata kyau dan duk wani kyawun dirin ta yagama bayyana ...

_____NABEELAH KENAN ____
Wanda bata haura shekara goma sha shida...... A duniya ba ta had'u iya haduwa dan komai nata me kyaune, gwanin birgewa,,.. Tsaye NABEELAH take a cikin bedroom d'inta, daga ganin alamunta waya take yi,
wayace kare a kunnenta, , cikin zazzakar muryarta mai matukar dad'in sauraro take magana, "..

Alright to gani nan fitowa

Cikin nutsuwa ta juya kana ta nufi hanyar fita daga cikin ɗakin cikin salon takun tafiyar ta mai
matukar ɗaukan hankali,....
Acikin parlourn su ta tadda Hajiya Nafisat tana zaune a saman two-seater daga ganin alamunta tana zaman jiran fitowar y'ar tatace,..

Zaune take a cikin hamshakin parlour d'inta, kallo daya zaka mata kasan dukiya sun zauna mata, ga wata Tsaleliyan phone d'inta kiran iPhone 15 agefen tah,.
Ta hakince Sai takama take yi da gadara, yayinda wata Ma'aikaciyar Gidan take ta famar mata fiffita, duk da uban sanyin dake falon kuwa, daga ganin alama ita ko sanyi bataji. a cewa ita zafi take ji,
da sanyi safiyarnan, Cike da izza take kad'a yan-yatsun tah wanda suka sha gwala-gwalai, Saman kyakkyawar wuyanta Shima yasha ado da sarka Mai ban mamaki.
Sannan ta gyara sumar kanta, Sai sheki yake, sannan ta daura mashi, Dan kwali irin daurin ture kaga tsiya nan.

______HAJIYA NAFISAT KENAN, WATO MAHAIFIYAR SU NABEEL D'IN FAREEDAH,

Ita ko Ma'aikaciyar Gidan Tana ganin fitowar Nabeelah ta d'an d'ago kanta,sai da ta d'an kalli NABEELAH tukkun kafin daga bisani cikin girmamawa ta Dan dukar da kanta,tare da furta...

"Barka da fitowa
Karamar hajiya!...
Ina kwana!! da fatan kin tashi lafiya ?..

Kallonta Nabeelah tayi tukkun kafin daga bisani cikin kulawa ita ma ta bud'e bakinta tace..

"Lafiya kalau

Cikin nutsuwa ta maida Kallonta izuwa gurin Mommyn su A inda take zaune.

Smiling Nabeelah tasake tare da fad'in "

Mommy yau kuma sai ina da sassafen nan,halan unguwa zaki?

Mik'ewa tsaye HAJIYA Nafisat tayi cik'e da gadara cikin izza da isa, sannan a hankali ta bud'e bakinta tafara magana, "...

Sai gidan uban ki cewar Mom tana mai d'aure fuska

Sannan cikin d'aure fuska mommy ta cigabada cewar "
Dan Allah ki yi kokari ki shiga kitchen, ki had'a mana abinchin breakfast kafin In dawo,don kema kisan bana iya cin girkin kazamai yan aikina ,saura kuma ki tsaya tsumulmulah da iya yi irin naki..........

"Okay..
To anyi angama yanzu ma kuwa zan shige cikin kitchen d'in Insha Allahu inji cewar NABEELAH sannan ta cigaba da cewar "
Dama na tsaya yin wanka ne shiyasa kikaga ban fito da wuri ba,..

"Cikin d'aure fuska Mommy tace" nizan wuce gidan NABEEL , Dan so nake da sassafen nan naje na ci mutumci matarr sa , Dan nagaji da jiran gawan shanu ba kaho,..." ɗaure fuska NABEELAH
tayi kafin cikin ɗaure fuska had'i da b'ata fuskarta Nabeelah ta furta"..
Haba mana Mommy wanann wacce irin masifa ce haka
Yanzu ke bakijin kunyar tashi tunda sassafe kije gidan surukan ki neman rigima ba, wannan wacce irin masifa ce haka!
ke kenan kullum cikin masifa da bala'i dan Allah Mommy kibar matan Yaya Nabeel tah huta haka, dan Allah ki sakar mata mara tayi fitsari, ki duba kigani
Sabida tsabar masifar ki ne fa yasa suka bar gidan nan ba shiri.......

Cikin fusata Mommy ta daka mata tsawa tace "..

Ke
Naci gidanku idan baki rufe min bakiba

"Cikin sanyi murya Nabeelah ta bud'e bakinta tace "kiyi hakuri, Allah ya huce zuciyar ki dear Mom, sai kin dawo Allah ya tsare hanya ta k'arasa maganarta tana mai kama kunnenta "batare da Mom tace da ita komai ba tanufi hanyar fita daga parlourn cikin bacin rai mai tsananin gaske
, tana k'arasa fitowa tsakiyar compound d'in Gidan, ta tadda Idi drivern-ta a tsaye yana jiran fitowar ta, ai kuwa yana ganin fitowar Mommy cikin sauri Idi driver ya bud'e mata marfin motah, ta shiga sannan ya rufe, cikin sauri ya zagaya yashiga cikin motar shima, Kallon sa tayi tare da fad'in
"Kai Dan kutumar ubanka baka iya gaisuwa bane!?

Atsorace Idi drive yace.

“Ina kwana Hajiya Nafisat?.

"Mtswww
Batare da Mommy ta amsa masa gaisuwar tasaba taja masa wani dogon tsoki,
cikin sauri Idi ya tada motar kana gate man ya wangle masu kofar gate d'in Gidan suka fice cikin gudu kamar zasu tashi sama Dan yasan halinta yana fara tafiya kadan kadan zata daka masa Tsawa tace masa ya kara wuta

_______*GIDAN NABEEL*____

Bayan 30minutes mommy ta iso GIDAN NABEEL ,cikin sauri MOMMY , ta shigo cikin parlour,tare da furta "

Asallamu aleykum!

Assalamu alaikum!!

Assalamu alaikum....

"Cikin sanyin murya had'i d'an d'aga murya ! FAREEDAH Ta katse Mom ta hanyar fad'in".

AMIN WALKSLM

"FAREEDAH ta amsa ma Mom sallamar tata, cikin sauri FAREEDAH ta fito daga cikin kitchen,Wani irin Dam! Kirjin FAREEDAH ya bada wani mugum sautin na bugu saboda ganin Mommy NABEEL da FAREEDAH tayi atsaye acikin parlourn su kafin kace k'obo tun jikin FAREEDAH yafara rawa sai wani irin mugum k'aduwa sassan jikinta yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,,,
Kai tsaye inda Mommy take tsaye ta nufa ,cikin sauri FAREEDAH ta k'araso gurin Mommy a inda take jikinta sai wani kad'uwa yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,
cikin nutsuwa had'i da fad'uwar gaba ta durk’usa akan gwuiwowin ta Wanda suka lume cikin lallausar carpet d'in dake parlourn ,sannan cikin tashin hankali da kuma firgicin da ta samu kanta aciki,murya na rawa tamkar wacce aka jonawa shocking tace.
"Momma Dan Allah kiyi hakuri ina kitchen ne banji shigowar kiba! , Good morning hope kin ta tashi lafiya? bismillah zauna mana..... ....cikin fusata!Mommy ta katseta ta
hanyar fad'in "....

Kin Ci Gidan ku! Tana mai aika mata da dakuwa, nace kinci ubanki Malamin tsubbu shegiya yar matsiyata
.Bakar juya...

Sannan ta buɗe baki cikin tsantsar masifa haɗi da bala'in da suke cinta tana mai cigaba da faɗin"
Da ban kwana ba zaki ganni,nace, da ban kwana ba zaki ganni Nazo Gidan d'ana NABEEL!
Sannan kuma ni HAJIYA Nafisat ban shigo Gidan nan dan in zauna a matsayin gidan surukata ba, tun da kin d'aura Dan-maran zama anan gidan, to ni kuma Sai na tuka miki tuwon kaya. Miyar allurah.. Sannan
Kuma Sai na shimfid'a miki, tabarman kashi. Wanda dolenki ki zauna a sama, ,kuma barikiji... tunda kince ke ba zaki bar NABEEL ya kara aure ba, duk matan duniya nan, NABEEL yace bai-ga kowa ba .Sai .ke. zai Aura.. ga ki nan juya, Wanda ta gaji bakin kishi daga gurin kakanintah, tunda kika hana NABEEL auren Azmerh . Yar kanwar MAHAIFIYAR sa,..
To ke ma Sai kin bar Gidan nan, domin ni HAJIYA Nafisat na koshi. Da bak'in cikinki, abin ya isheni hakanan!

Sabida haka in ya dawo, kice masa Ina nemansa da gaggawa..

Saura kuma ki ki fad'a masa insake dawowa inci mutuncinki, wadda batada wani amfani shashsha kawai mai mugun hali,
Tana Gama ƙarasa maganarta tanufi hanyar fita daga parlourn tare da ficewa daga gidan gabadaya Abinta.

"Na shiga uku
!!! Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un FAREEDAH ta fad'i tana mai fashewa da kuka sannan cikin sheshshekar kuka ta cigaba da cewa "
Sai yaushe ne zan samu sauyin lamari acikin rayuwa ta? , d'a Namijin da nake tattalinsa fiye da komai nawa , haka kuma d'a mijin tilo da nake ji dashi acikin zuciyarta, rayuwarta komai nawa , lallai kam tabbas idan har Mommy tayi nasar raba nida farin ciki na shakka babu mutuwa zanyi Dan tasan nawa yakare bazan iya rayuwa babu shiba,Cikin zubarda hawayen take cigaba da fad'in "I don’t know how to love somebody, but mah feelings for you justified how much I love you, NABEEL Ina MATUƘAR SONKA
Share kwallar dake zuba a cikin idanuwanta tayi haka dai tacigaba da sharara kuka ita dai har NABEEL ya DAWO daga masallacin ya tadda ita ahaka, "NABEEL ne ya shigo cikin parlourn tare da furta "

Asallamu Aleykum!
Chapter 3 · 0% Book details