← Book details Doguwar Hanya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 39

Sashe 30

Doguwar Hanya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*******
Tunda Lawuri ta dawo hayyacinta ta tariyo duk abinda ya faru se hankalin ta ya mugun tashi, tanaso taga Abu Hurairah ko yaya ne, da gaske tayi murnar ganin iyayenta amma bata farin ciki barin su Abu hurairah tana me aka dawo da ita gidan? Ta tuna komai ta gane komai ta fahimci komai daya faru rad'am!! Ina zataje taga haske, tundaga sannan kullum seta yiwa mahaifinta kuka akan ya sanya a mayar da ita ta masa alk'awarin zata dawo, da wannan yace babu damuwa ze bada dama taje wani satin, tunda tasan hanya inyaso gardawa sesu rakata....... Tofa!!!!!!

**********
Dad shiru yae yana tunanin wannan zancen dasuka zo masa dashi, mom ma tarasa ta cewa, sunyi shiru na wasu en dak'ik'u kafin General yae gyaran murya cikin b'acin rai yana me kallon Huraira yace masa

"Kai yanzu da hankalinka da komai Abu Hurairah zakayi wannan sakarcin, ni bama zancen auren ya dameni ba, na tabbatar bazakayi aure da gangan ba abu mafi ban haushi da takaici yanda ka b'oye mana 1, 2 kuma yanda ka cutar da yarinyar mutane, wani shegen ne yasanya ka tara da ita bayan kasan basanta kake ba, idan ma hakanne bazaka sauwaqe mata iymgiyar aurenka ba batare daka koda tab'a taba se tsabar rashin hankali ka daddage kawa matar ka ta sunna ciki sannan ka barta da ganin garari? Ni yanzu me kakeso nayi? Idan da siyama aka mawa zakaji dad'i ne? Eh nace zakaiji dad'i ne?" Hakuri ya hau bayar wa, ita kuma mom ta wani b'ata rai

"Haba Ganeral yaran nan sunmaka bayani akan cewar itace da kaud'in d'aura auren ma, bayaga haka aisunce maka so d'aya ne wani abu na auratayya ya gifta a tsakanin su? Abu na k'arshe kuma baya santa koda ganinta akai ni zan saka ya saketa" wata uwar k'ara ya saka irin ta tsofaffin sojoji

"Kee!! Adama wlhy duk rabar daya rabu da ita kema nan gidan zaki bari, kuma seya nemo 'yar mutane, ni zaku kawowa rainin hankali ku mayar dani k'aramun mutum, duk kanin abubuwan dasuka faru kece sila, an kawo yarinya yaranki suna so kince arniya ce babu wanda yazo a musulmi dan gatan sa, Allah ne yaso ya kuma zab'emu, dan ya zab'i wasu bawai illa bane ba, shibe guji bayin sa amma ke duk kin jagula maganar, tun Anan zaki gano cewar Allah mabuwayi ya nuna miki ikon sa, danma be bashi bamaguzar ba, kikakai aya, daya ya bashi musulma yarinyar dayake magana zuhra nasan mahaifinta farin sani, case na b'atanta ma nasan dashi harni anje nemanta dani, Allah ne ya nuna miki abinki kuma wlhy na bashi sa'o'i 72 ya nemo 'yar mutane kona mai hauka nima, zanje in gana da ubanta yanzu shima ya b'ata raina da wayon sa da komai aida ya tuhumeta yaji". Mom shiru tamkar ruwa ya cinyeta d'anya ko motsinta baka ji ko kad'an tsit kakeji.

********
*Bayan kwana biyu*

Daga asibitin ta fito sun koreta akan batada kud'in magani bazasu karb'eta ba,fitowa tayi abin duniya ya dameta, ga d'akin datake zama a hotel kaf har kud'in sark'arta data siyar ya cinye tunda hotel ne, gashi batada lafiya scaning ma takeso amata amma abun ya gagareta asibiti sun gaji sun koreta, asibitin datazo da hotel datake zama ma akwai jayawa gashi 600 kad'ai ne a hannunta ga yunwa, yaudai ta yanke shawarar komawa gun iyayenta hatta wayar da aka siya mata ma ta siyar ta cinye kud'in, da k'afa take tafiya gashi tarasa dalilin kumburin jikinta, cikinta yayi saurin girma wataninsa dudu nawane hud'u fa amma kaman gobe zata haihu, jiri ne yasoma kwasarta adaidai sanda tazo tsallaka titin dashine ze sadata da gidansu General kuwa adaidai nanne yake shigo layin yana k'ok'arin kaiwa mahaifinta ziyara domin su nemi mafita dan tun ranar ya taresa da maganar ma, Kad'an ya rage su bigeta seda koda basu kad'e tanba fad'uwa tayi a k'asa warwas!!!

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

*Book nawa na kud'ine, idan kinsan baki biyaba dan Allah karki karantamun kokimun sharin book nawa a groups, idan kina buqatar siya ki nemeni ta wannan number 07084161619.*

28

Sauka sukai daga kan titin suka fito da sauri duk sukai kanta, basu b'ata lokaciba wurin sakata a mota su juya akalar motarsu zuwa asibiti bayan da suka dire General agidan yabasu umarnin su kaita asibiti cikin gaggawa.

Wayar ya zaro a daidai sanda yazo shiga k'ofar parlor bayan an masa iso, Abu Hurairah yakira

"Hello Dad" cikin dakakkiyar murya yace

"Kana ina ne?" Saisaita nutsuwar sa yae

"Dad ina kan hanya da zanje gidana"

"Kaje National hospital na tura wata patient dana kusan bigeta a titi amma seta suma kaman fad'uwar gabane,tare dasu umar take da sauransu u contact of them, kaje ka biya Bill nata ka tabbatar duk wata kulawa ta samu, ka jira a wurin idan ta farfad'o ta gaya maka gidann su asanar da mijinta ko iyayenta halin datake ciki" kafin yae wata maganar harya kashe wayar... Juya akalar kiransa yae zuwaga Abu Sufyan yace a sanar masa yazo ya sameshi gidan zasu koma gida atare.

*********
Kai tsaye asibitin ya nufa yaje ya tarar sun karb'i patient d'in nurse d'in se mita takeyi

"So nawa zan gaya muku bazamu karb'i patient ba kud'i ba, gata da hawan jini ga k'aton ciki agabanta da 4month, tarasa duk duniya wanda ze biya mata kud'i a duba lafiyan ta dana babyn ta, wanda suka kawota idan bazasu iyaba su koma da ita gaba d'aya" matsowa yae dan sojin sun gayamai patient da suka kawo ce akewa wannan izgilin ya kalli nurse d'in

"Meye bill nata duka abinda take buk'ata?" Kallon shi tayi amma bataga alamar wasa ba

"72500 duka kud'in ta ta gagara biya se sintiri take anan" hararata yae

"To zamu biya ki kula da ita cikin gaggawa" ya juya batare daya jira cewar taba, rashin zuhra yana neman hallakar dashi ma gaba d'aya zata bashi haushi akan wasu tsirarrun kudad'e.....Befi 1 hour dazama ba nurse din tadawo gunsa

"Sir likita yanason ganin wanda yazo da patient d'in d'azu" kallon ta yae kafin yaja gajeran tsaki ya mik'e

"Muje" haka suka rankaya har gun likitan, sun gaisa sannan ya zauna

"Dama kane mijin waccen yarinyar, a gaskia kun kusa kasheta yarinyara batada lafiya ga juna biyu amma baku kulaba, ita batacin komai na gina jiki ga yara biyu acikinta ga pcv d'inta yaje down sosai yanzu haka 24% yazatayi surviving da shi gabyara biyu ga hawan jini? What on earth were u doing daze sanya kabar iyalanka su shiga fitina har haka" kallon mamaki yama Dr. D'in amma kfin ya samu damar magana likitan yaci gaba

"Thank God yaran suna lafiya, sedai basuda wani nauyi sabida yunwa basuda kuzari sabida babu wadataccen jini ajikin uwar, yanzu zamu baku cross marching na jini kaje a gwada naka idan zeyi da gaggawa muke buk'atar sa idan bazeyiba ku siya kawai sabida bamuda lokaci wannan ze iya sakawa ta rasa rayuwarta har abada" Mik'ewa likitan yae bayan ya tura masa takardar gwajin ya shige ban d'akin dake cikin toilet d'in nashi, mik'ewa yae jikinsa a sanyaye yakira dad yake sanar masa

"Kaje a gwada jinin naka idan zeyi ka bayar" kan yae magana har Dad ya kaste kiran, yaya ze bayar da jininsa ga wacce beko santa ba? Ko ganinta be tab'a yiba haka yake yaja soja uku akaje gwajin a lab duk nasu baya yi senashi, haka aka eba se qunquni yake aka bashi gado domin ya huta na 1 hour koda yazo har an soma d'ura mata jinin, shiko kallon tama beyi ba yace zeje ya dawo da dare.

***********
"Maganar auren nawane bakyaso kuma Ayusher? Mena miki yanzu wai kika tsaneni haka?" Kallon sa tae tana murmushi

"Ba abinda kamun nikam kurun dai nabaka damane ka wofintar yanzu kuma kaga Raubil ma yazo yace ze gabatar da manyan sa ya kakeso nace masa? So tari abinda muke rainawa shine yake mana wahalar samu wataran, kayi hak'uri kawai kaje gun Lawuri ka koma doguwar hanyar dazata sadata da garinsu ka aurota tunda Abu Huraira be samu ba" sumar kanshi ya shafa

"Ayusher pure heart d'in ki nefa? Wani kallon banza ta masa

"Pure heart d'in kuwa to sai me?" Shiru yae maganar tafi k'arfin sa yace

"Zan koma sena kiraki a waya" murmushi ta k'arayi

"Base ka kiraba idan na nutsu zan kiraka da kaina" murmushi shima yae

"Ba damuwa nagode" daga haka ta juya shima yabar gidan zuciyar sa ba dad'i.

********
"Me kake tunani game dani ne wai Al-hassan?, tun jiyan dama baka koma ba? Haka mukai dakai? Bance ka bari ta farfad'o ka nemi iyayen taba, kasan dama ina cike dakai ne fam ko? Wlhy ka kiyayeni maza katashi kaje ka duba ta, zancen yarinyar cen kuma anduba duka dangi kaf bata cen sekasan nayi" godiya yae ya mik'e jikinsa a mace zuwa gunta.

Anyi nasarar fitowa daga jeji su Lawuri sedai en riga sun kafe akan bazasu rakasu wajen gari ba, da k'yar me gari danya sanya ya basu kud'in jirgin dazasu hau su tsallaka ruwan na garuruwa uku, gasu dai a inda zasu hau mota amma ko anini basuda shi, ta rik'e sunan Abuja rad'au sedai bazata iya kai kanta gidansu ba, abu d'aya ta sani kota halin yayane setaga Abu Hurairah, kwanansu hud'u suna kwana a tasha, har lokacin motar ma taba tashi se bayan sati biyu kuma, mutanen garin sun soma gajiyawa dasu suna yaren fulani suke jiba.

*********
Kai tsaye wurin gadon patient d'in yaje ya kalleta tana baccinta cikin nutsuwa, wutsiyar hannun ta ya kalla ya tuna last maganar su sanda suka kwana hotel data karb'i wani agogon fata daya siya dasuka isa garin tace tanaso, shine rad'au a hannunta, d'ayan hannunta na dama sanye da ruwa ana k'ara mata, murza idansa yae cikeda mamaki, lokaci d'aya maganganun likitan nan suka dawo masa, kenan dukkaninsu akan shi yakeyi, dama zuhra ce ke cikin wannan mawuyacin halin lallai ya aikata zunubi Allah ma baze barshi ba........ Zama yae a d'akin har kusan sa'a fiye da d'aya seda ta farfad'o sannan ya tashi da azama yae kanta
Chapter 30 · 0% Book details